Sashe 10
Gurbin Ido Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Amma kinyi kyau maimunatuna......ina fata babu wanda ya kallemin ke" yayi maganar yana washe baki,kanta ta daga a hankali tana duban gefe da gefanta,tana fatan kada Allah ya kawo Ibrahim a yanzu har sai buderi ya wuce,tasha jin alwashi daga bakin buderin na cewa,duk randa yaga wani ya rabi maimunatunsa,wala shakka sai ya sha jininss,tana kyautata zaton wannan na daya daga cikin dalilan daya sanya babu wanda yake mu'amala da ita
"Me kike nema kuma?" Ya fada yana hade rai,kai ta girgixa
"Babu komai" amsarta tasa ya saki fuska
"Na sani,kinfi kowa hankali cikin 'yammatan rugar nan,nasan babu wanda zaki kula,ungo wannan" yayi maganar yana miqa mata wata leda.
Babu batun ma tace ba zata karba ba,don kuwa bata baki ne,don haka ta saka hannu ta karba tana cewa
"Na gode"
"Yauwa,medillu,dan men waratam?(zan tafi,yaushe zanzo?" Mummunan faduwa gabanta yayi,kada dai xancan da innar laulo ke gaya mata ya tabbata,buderi..... Buderi ne zai fara zuwa tadi wajenta?
"Ban sani ba" sandarsa ya wulwula sama ya caketa a qasa
"Shikenan,ni xan saka rana da kaina" sai ya juya abinsa ya fara tafiya,dama can shi din ba mutum ne da ya iya yin sallama ba,da ya gama abinda ya kawoshi xai saka kai ya wuce abinsa,har ya dan bata rata sai taga ya dawo da tsaya a gabanta
"Baki taba cewa kina so ba maimunatu,ate ayyam?,ayid'iyam?(zaki aureni?,kina sona?)" Banbarakwai taji maganar tasa,ta kuma rasa amsar da zata bashi,tana matuqar tsiron buderi,batajin xai kasa maketa a wajen idan tace bata sonshi,amma kuma idan tace tana sonsa din tayi masa qarya,sannan yaudara ta shigo ciki.
Dariya ya bangare da ita
"Ja'ira,kunyar gayamin kikeji kenan.....shikenan,idan nazo saiki gayamin tunda zuwan dare ne,bana ganinki sosai" daga haka ya juya abinsa yana waqar tauri.irin ta matasan fulani yana cilla sandarsa.
Baya taja a hankali ta jingina bayanta da bishiyar dake wajen,ta sauke nannauyar ajiyar zuciya tana lumshe idanunt,sannan ta saki ledar hannunta a hankali ta sulale zuwa qasa.
A matakin rayuwarta gaba daya ba zata iya dorar da komai ba,ba zata iya fadin meye ainihin rayuwa ba,kamar yadda ba zata iya fadin me rayuwa ta qunsa ba,meye manufar tata rayuwar?,me ta cimma?,me takeso ta cimma?,tabbas a karan kanta tasan cewa akwai abubuwa da dama da takeso ta cimma,tana da mafarkai da burika masu yawa irin na kowanne dan adam,saidai ita kanta batasan wadanne ne burikanta ba,me takeso ta cimma din,dukka bata sani ba,rayuwata qwaqwalwarta dama komai nata na tattare ne a waje daya,a yanzun kumma innar laulo ta dauko hanyar da zara qara ruguzata zuwa pieces gaba dayanta,aure da buderi?,me hakan yake nufi?,wanne buri ne a ran innar da takeso ta cimma?.
Ta jima a haka kafin ta iya bude idanuwanta,dukka wani fata da take dashi na ganin ibrahim ya fara zagwanyewa daga zuciyarta gaba daya,ganin yadda lokacin da ya dace tabar wajen zuwa gida ya gabato,jiki a mace ta miqe daga jikin bishiyar,saidai tana taku biyu takalminta ya katse
"Innalillahi" ta fada gabanta yana faduwa,ta duqa a hankali da zummar daukoshi,sai tayi arba da ledar da buderi ya kawo mata wadda ta jima da faduwa a wajen,ta sanya hannunta a nutse ta budeta,sai tayi arba da gasashen naman daji,cikin tashin zuciya ta dauki ledar gaba daya tayi wurgi da ita can cikin daji,sannan ta dauki takalminta ta duba da kyau,ya gama moruwa,bataga laifinsa ba,saboda yayi mata iyakar qoqari,bata da wata sauran dabara data rage mata,abu dayane a yanzu yayi mata saura shine ta cire dayan ta dauresu a qugunta,sannan taci gaba da tafiya da zallar tafin qafarta tana fara hade kan dabbobin,tanayi tana takatsantsan kada ta taka qaya.
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 07
Tun batayi nisa ba gaba daya qafafunta taji sun daddaure saboda tsakuyiyin da take takawa,wani gurin harda cabalbalin daya cakude da ruwa da qasa,tuni ta jima da sanin cewa ba qaramar rahama bane takalman a gareta,rashinsu a yan mintuna kadan yasa fa fara dandana kudarta,bata kuma san sanda zata sake mallakar wasu ba.
A hankali motarsu daada ke kutsawa rubibbiyar hanyar mai yawan gargada,kamar yadda sukazo a yanzunma su hudune,saidai yanzun akwai qarin saddam da zai musu rakiya,a hanyarsu ta zuwa ziyara qauyen dake kusa da rugar ummarun.
Cikin motar tattaunawa suke kan yadda gwamnati tayi banza da nuna halin ko in kula da jama'ar dake rayuwa a irin wadan nan muhallan,babu ruwa ba wuta babu hanya me kya bare azo ga maganar tsaro
"Subhanallah" salmanu driver ya fada yana taka burki sanda shanun suka fara keto burtalin xasu wuce,salmanu ya kalli agogon hannunsa yana cewa
"Aqalla sai sun kusa minti biyar ko takwas suna wucewa,shi yasa tun dazun nake sauri mu wuce kafin su iso"
"Wai daman kuna iya kula da dabbobi babu duka?" Laila ta fada cikin mamaki,idanunta nakan maimunatu dake koro shanun daga can baya
"Qalilan ne gaskiya,kiwo yana da wuya fa adda laila" maganar data ja hankalin daada,ta daga kanta zuwa ga sashen da maimunatu take.
Ido ta zuba mata sosai cike da mamaki da kuma burgewa,gaskiya sadam ya fada ba kowane ke iyawa ba,kula da dabba koda guda daya ne abune mai matuqar wahala,sai mutum me haqurin gaske da kuma tausayi,bare wadan nan da sun haura talatin,banda akuyoyi,yarinya qarama irin wannan me qananun shekaru,ita daya babu mataimaki,zata iya cewa bata taba ganin wannan ba,koda akwai din sai jarumar mace mai kamar maza,wadda taga jiya ta kuma ga yau.
Idanun maimunatu nakan motar sanda ya rage ita daya ce zata haura hanyar,idanunta cike fal da fargaba da tsoro,karo na biyu kenan da taga motar,amma sai take ga kamar abinda ya faru da ita shekarun baya zai sake faruwa da ita,sassanyar ajiyar zuciya ta saki sanda taga ta tsallaka,dai dai lokacin da anni ta sauke idanunta ga qafafuwan maimunatu,mamaki ya cikata ganin yadda take ratsa wajen da zallan qafarta ba takalmi.
Ta buda baki xatayi magana ta jiyo sautin maimaunatun
"Wayyo Allah" tayi maganar a matuqar jigace tana duqawa zuwa qasa tana duban tafin qafafunta
"Tsaya salmanu.....dubamin me ya samu yarinyar can" anni ta tsaida salmanu dake shirin tada motar,wajen suka kalla su duka,laila tayi kamar zatayi magana amma sai ta fasa kada qilu ta jawo bau,seat belt din jikinsa ya zare ya bude murfin motar ya fita,bai wuce minti daya ba ya dawo
"Kaya ce ta shige mata qafa,ta huda wajen sosai,amma naga ta zareta ma"
"Garin yaya?" Wajen da take salmanun yakalla
"Qafarta ce ba takalmi,dana tambayeta yana ina sai tace ya tsinke ne"
"Ina silifa din nan da nace a sakaminsu a mota?,daukomin daya a ciki" ta fadawa laila,daukowa laila tayi ta miqowa annin
"Bawa salmanu yakai mata ta saka" hannu salmanun ya saka ya karba ya juya yakoma indatake,zuwa sannan ta miqe tsaye bayan ta yagi wani ganye dake gefanta ta manna a wajen.
Daga kai tayi ta dubi salmanun sanda yake bata takalmin,sai taja baya kadan gami da girgiza kai alamun ba zata karba ba,abinda ya sanya salmanu dawowa inda anni ke zaune tana kallonsu
"Anni taqi karba fa,kamar bata yarda bane damu"
"Budeni" anni ta bashi umarni,sai ya zagayo ya bude mata qofar
"Anni,karkice zakiyi magana da ita,kaf fadin rugarmu babu wanda yake kulata" sadam ya fada,a mamakance anni ta kalleshi
"Saboda me?"
"Ban sani ba nima,amma tsoron mata magana akeyi" shuru anni tayi na wasu sakanni sannan ta zura qafafunta waje ba tare data sake bi ta batun saddam ba
Har maimunatun tayi taku daya biyu taji muryar anni
"Yarinya" cak ta tsaya,a tsorace ta waiwayo idanunta akan anni,tsoro ya sake kamata,don sam annin batayi zubin mutanensu ba.
"Yallijam" maimunatu ta fada a hankali ganin idanun annin har yanzu yana kanta
"Jam" anni ta maida mata tana kallonta tare da karantar yanayinta
"ya kike tafiya haka ba takalmi?" Qafarta ta kalla sannan ta kalla annin
"Sun tsinke ne daada" yadda ta kirata da girmamawa sai yasa anni ta saki murmushi
"Salmanu bata wadan nan ta saka,da hatsari wajen taka gurin nan haka" da fari kai maimunatu ta sake girgizawa kamar yadda ta yiwa salmanu,don batasan me zatacewa inna ba idan ta ganta da takalmin
"Na gode daada,zan qarasa a haka" haka kawai taji ta burgeta,akwai alamun tarbiyya da kamun kai me yawa tattare da ita
"Karki damu ki saka,idan ma kina tsoron fada ne a gida kice baquwa ce daga gidan bappa labaran ta baki" daga kai tayi sosai tana duban anni,idan ta canka dai dai fa kenam gidansu himu take nufi,ita a wa sa zata ambaci sunan gidan tace wani abu daga hannunsu ya fito zuwa gareta,a sanyaye ta karba takalman ta sakawa qafarta.
Cif da cif kuwa kamar an aunata,wasu irin slipper ne na danqo amma me garai garai dake nuna hoton flowers daga dukka jikin takalmin kaman tangaran,kallon qafar tata tayi ta sake kalla,sai ta daga kai a hankali tace
"Na gode sosai daada" duk kuwa da tana da yaqinin wannan takalmin idanunsa idanun inna ba rabonta bane,murmushi anni tayi
"Ba komai" sai ta juya maimunatun tana qara hanzari don ta taddo dabbobinta da sukayi gaba,tana kuma kiransu da wani irin salo da yasa anni ta bita da kallo.
"Anni....anni kenan,qaqale qaqalen mutane,tayiya jajibo jama'a ana zaune qalau" laila tayi 'ya qaramar mita ciki ciki,abinda yaja hankalin anni dake maida qafafunta cikin motar salmanu yana shirin rufe mata
"Me kike cewa ke kuma?"
"Bance komai ba"
"Oho miki,idan ma zagina kikayi kin zagi marwanu da Aishatu" idanu laila ta lumshe tana dafe goshinta,kafin tace wani abu wayarta dake kan cinyarta ta dauki sautin kida me dadi,saita daga wayar tana dubawa
"Ga marwanun nan" lailan ta fada tana hade rai tare da miqawa anni wayar
"Kin fada dai dai ai,sunan ubanki kenan" ta amsata tana warce wayar daketa harbawa da sunan super dad,ta shafa ta kara a kunnenta.
"Sai da salma ta gargadeni kan tafiyar nan,ashe ni zan karba gashin" bata daddara ba dai ta sake yin qorafin murya can cikin maqoshi,saidai babu yadda za'ayi anni taji,saboda tayi nisa a waya da shalelen dan nata.
Sai da tayi duk wani abu daya zame mata al'ada idan ta dawo da dabbobin daga kiwo sannan ta kira sunan innar,saidai babu ita ba motsinta,dole ta fara takawa zuwa cikin gidan,qirjinta yanata dukan uku uku,don batasan me zai biyo baya game da takalmin qafarta ba.
Daga qofar dakin innar ta tsaya
"Miwarti ɗilaulake inna(na dawo daga kiwo inna)" shuru taji,hakan yasa ta sake maimaitawa
"Me kike nema kuma?" Ya fada yana hade rai,kai ta girgixa
"Babu komai" amsarta tasa ya saki fuska
"Na sani,kinfi kowa hankali cikin 'yammatan rugar nan,nasan babu wanda zaki kula,ungo wannan" yayi maganar yana miqa mata wata leda.
Babu batun ma tace ba zata karba ba,don kuwa bata baki ne,don haka ta saka hannu ta karba tana cewa
"Na gode"
"Yauwa,medillu,dan men waratam?(zan tafi,yaushe zanzo?" Mummunan faduwa gabanta yayi,kada dai xancan da innar laulo ke gaya mata ya tabbata,buderi..... Buderi ne zai fara zuwa tadi wajenta?
"Ban sani ba" sandarsa ya wulwula sama ya caketa a qasa
"Shikenan,ni xan saka rana da kaina" sai ya juya abinsa ya fara tafiya,dama can shi din ba mutum ne da ya iya yin sallama ba,da ya gama abinda ya kawoshi xai saka kai ya wuce abinsa,har ya dan bata rata sai taga ya dawo da tsaya a gabanta
"Baki taba cewa kina so ba maimunatu,ate ayyam?,ayid'iyam?(zaki aureni?,kina sona?)" Banbarakwai taji maganar tasa,ta kuma rasa amsar da zata bashi,tana matuqar tsiron buderi,batajin xai kasa maketa a wajen idan tace bata sonshi,amma kuma idan tace tana sonsa din tayi masa qarya,sannan yaudara ta shigo ciki.
Dariya ya bangare da ita
"Ja'ira,kunyar gayamin kikeji kenan.....shikenan,idan nazo saiki gayamin tunda zuwan dare ne,bana ganinki sosai" daga haka ya juya abinsa yana waqar tauri.irin ta matasan fulani yana cilla sandarsa.
Baya taja a hankali ta jingina bayanta da bishiyar dake wajen,ta sauke nannauyar ajiyar zuciya tana lumshe idanunt,sannan ta saki ledar hannunta a hankali ta sulale zuwa qasa.
A matakin rayuwarta gaba daya ba zata iya dorar da komai ba,ba zata iya fadin meye ainihin rayuwa ba,kamar yadda ba zata iya fadin me rayuwa ta qunsa ba,meye manufar tata rayuwar?,me ta cimma?,me takeso ta cimma?,tabbas a karan kanta tasan cewa akwai abubuwa da dama da takeso ta cimma,tana da mafarkai da burika masu yawa irin na kowanne dan adam,saidai ita kanta batasan wadanne ne burikanta ba,me takeso ta cimma din,dukka bata sani ba,rayuwata qwaqwalwarta dama komai nata na tattare ne a waje daya,a yanzun kumma innar laulo ta dauko hanyar da zara qara ruguzata zuwa pieces gaba dayanta,aure da buderi?,me hakan yake nufi?,wanne buri ne a ran innar da takeso ta cimma?.
Ta jima a haka kafin ta iya bude idanuwanta,dukka wani fata da take dashi na ganin ibrahim ya fara zagwanyewa daga zuciyarta gaba daya,ganin yadda lokacin da ya dace tabar wajen zuwa gida ya gabato,jiki a mace ta miqe daga jikin bishiyar,saidai tana taku biyu takalminta ya katse
"Innalillahi" ta fada gabanta yana faduwa,ta duqa a hankali da zummar daukoshi,sai tayi arba da ledar da buderi ya kawo mata wadda ta jima da faduwa a wajen,ta sanya hannunta a nutse ta budeta,sai tayi arba da gasashen naman daji,cikin tashin zuciya ta dauki ledar gaba daya tayi wurgi da ita can cikin daji,sannan ta dauki takalminta ta duba da kyau,ya gama moruwa,bataga laifinsa ba,saboda yayi mata iyakar qoqari,bata da wata sauran dabara data rage mata,abu dayane a yanzu yayi mata saura shine ta cire dayan ta dauresu a qugunta,sannan taci gaba da tafiya da zallar tafin qafarta tana fara hade kan dabbobin,tanayi tana takatsantsan kada ta taka qaya.
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 07
Tun batayi nisa ba gaba daya qafafunta taji sun daddaure saboda tsakuyiyin da take takawa,wani gurin harda cabalbalin daya cakude da ruwa da qasa,tuni ta jima da sanin cewa ba qaramar rahama bane takalman a gareta,rashinsu a yan mintuna kadan yasa fa fara dandana kudarta,bata kuma san sanda zata sake mallakar wasu ba.
A hankali motarsu daada ke kutsawa rubibbiyar hanyar mai yawan gargada,kamar yadda sukazo a yanzunma su hudune,saidai yanzun akwai qarin saddam da zai musu rakiya,a hanyarsu ta zuwa ziyara qauyen dake kusa da rugar ummarun.
Cikin motar tattaunawa suke kan yadda gwamnati tayi banza da nuna halin ko in kula da jama'ar dake rayuwa a irin wadan nan muhallan,babu ruwa ba wuta babu hanya me kya bare azo ga maganar tsaro
"Subhanallah" salmanu driver ya fada yana taka burki sanda shanun suka fara keto burtalin xasu wuce,salmanu ya kalli agogon hannunsa yana cewa
"Aqalla sai sun kusa minti biyar ko takwas suna wucewa,shi yasa tun dazun nake sauri mu wuce kafin su iso"
"Wai daman kuna iya kula da dabbobi babu duka?" Laila ta fada cikin mamaki,idanunta nakan maimunatu dake koro shanun daga can baya
"Qalilan ne gaskiya,kiwo yana da wuya fa adda laila" maganar data ja hankalin daada,ta daga kanta zuwa ga sashen da maimunatu take.
Ido ta zuba mata sosai cike da mamaki da kuma burgewa,gaskiya sadam ya fada ba kowane ke iyawa ba,kula da dabba koda guda daya ne abune mai matuqar wahala,sai mutum me haqurin gaske da kuma tausayi,bare wadan nan da sun haura talatin,banda akuyoyi,yarinya qarama irin wannan me qananun shekaru,ita daya babu mataimaki,zata iya cewa bata taba ganin wannan ba,koda akwai din sai jarumar mace mai kamar maza,wadda taga jiya ta kuma ga yau.
Idanun maimunatu nakan motar sanda ya rage ita daya ce zata haura hanyar,idanunta cike fal da fargaba da tsoro,karo na biyu kenan da taga motar,amma sai take ga kamar abinda ya faru da ita shekarun baya zai sake faruwa da ita,sassanyar ajiyar zuciya ta saki sanda taga ta tsallaka,dai dai lokacin da anni ta sauke idanunta ga qafafuwan maimunatu,mamaki ya cikata ganin yadda take ratsa wajen da zallan qafarta ba takalmi.
Ta buda baki xatayi magana ta jiyo sautin maimaunatun
"Wayyo Allah" tayi maganar a matuqar jigace tana duqawa zuwa qasa tana duban tafin qafafunta
"Tsaya salmanu.....dubamin me ya samu yarinyar can" anni ta tsaida salmanu dake shirin tada motar,wajen suka kalla su duka,laila tayi kamar zatayi magana amma sai ta fasa kada qilu ta jawo bau,seat belt din jikinsa ya zare ya bude murfin motar ya fita,bai wuce minti daya ba ya dawo
"Kaya ce ta shige mata qafa,ta huda wajen sosai,amma naga ta zareta ma"
"Garin yaya?" Wajen da take salmanun yakalla
"Qafarta ce ba takalmi,dana tambayeta yana ina sai tace ya tsinke ne"
"Ina silifa din nan da nace a sakaminsu a mota?,daukomin daya a ciki" ta fadawa laila,daukowa laila tayi ta miqowa annin
"Bawa salmanu yakai mata ta saka" hannu salmanun ya saka ya karba ya juya yakoma indatake,zuwa sannan ta miqe tsaye bayan ta yagi wani ganye dake gefanta ta manna a wajen.
Daga kai tayi ta dubi salmanun sanda yake bata takalmin,sai taja baya kadan gami da girgiza kai alamun ba zata karba ba,abinda ya sanya salmanu dawowa inda anni ke zaune tana kallonsu
"Anni taqi karba fa,kamar bata yarda bane damu"
"Budeni" anni ta bashi umarni,sai ya zagayo ya bude mata qofar
"Anni,karkice zakiyi magana da ita,kaf fadin rugarmu babu wanda yake kulata" sadam ya fada,a mamakance anni ta kalleshi
"Saboda me?"
"Ban sani ba nima,amma tsoron mata magana akeyi" shuru anni tayi na wasu sakanni sannan ta zura qafafunta waje ba tare data sake bi ta batun saddam ba
Har maimunatun tayi taku daya biyu taji muryar anni
"Yarinya" cak ta tsaya,a tsorace ta waiwayo idanunta akan anni,tsoro ya sake kamata,don sam annin batayi zubin mutanensu ba.
"Yallijam" maimunatu ta fada a hankali ganin idanun annin har yanzu yana kanta
"Jam" anni ta maida mata tana kallonta tare da karantar yanayinta
"ya kike tafiya haka ba takalmi?" Qafarta ta kalla sannan ta kalla annin
"Sun tsinke ne daada" yadda ta kirata da girmamawa sai yasa anni ta saki murmushi
"Salmanu bata wadan nan ta saka,da hatsari wajen taka gurin nan haka" da fari kai maimunatu ta sake girgizawa kamar yadda ta yiwa salmanu,don batasan me zatacewa inna ba idan ta ganta da takalmin
"Na gode daada,zan qarasa a haka" haka kawai taji ta burgeta,akwai alamun tarbiyya da kamun kai me yawa tattare da ita
"Karki damu ki saka,idan ma kina tsoron fada ne a gida kice baquwa ce daga gidan bappa labaran ta baki" daga kai tayi sosai tana duban anni,idan ta canka dai dai fa kenam gidansu himu take nufi,ita a wa sa zata ambaci sunan gidan tace wani abu daga hannunsu ya fito zuwa gareta,a sanyaye ta karba takalman ta sakawa qafarta.
Cif da cif kuwa kamar an aunata,wasu irin slipper ne na danqo amma me garai garai dake nuna hoton flowers daga dukka jikin takalmin kaman tangaran,kallon qafar tata tayi ta sake kalla,sai ta daga kai a hankali tace
"Na gode sosai daada" duk kuwa da tana da yaqinin wannan takalmin idanunsa idanun inna ba rabonta bane,murmushi anni tayi
"Ba komai" sai ta juya maimunatun tana qara hanzari don ta taddo dabbobinta da sukayi gaba,tana kuma kiransu da wani irin salo da yasa anni ta bita da kallo.
"Anni....anni kenan,qaqale qaqalen mutane,tayiya jajibo jama'a ana zaune qalau" laila tayi 'ya qaramar mita ciki ciki,abinda yaja hankalin anni dake maida qafafunta cikin motar salmanu yana shirin rufe mata
"Me kike cewa ke kuma?"
"Bance komai ba"
"Oho miki,idan ma zagina kikayi kin zagi marwanu da Aishatu" idanu laila ta lumshe tana dafe goshinta,kafin tace wani abu wayarta dake kan cinyarta ta dauki sautin kida me dadi,saita daga wayar tana dubawa
"Ga marwanun nan" lailan ta fada tana hade rai tare da miqawa anni wayar
"Kin fada dai dai ai,sunan ubanki kenan" ta amsata tana warce wayar daketa harbawa da sunan super dad,ta shafa ta kara a kunnenta.
"Sai da salma ta gargadeni kan tafiyar nan,ashe ni zan karba gashin" bata daddara ba dai ta sake yin qorafin murya can cikin maqoshi,saidai babu yadda za'ayi anni taji,saboda tayi nisa a waya da shalelen dan nata.
Sai da tayi duk wani abu daya zame mata al'ada idan ta dawo da dabbobin daga kiwo sannan ta kira sunan innar,saidai babu ita ba motsinta,dole ta fara takawa zuwa cikin gidan,qirjinta yanata dukan uku uku,don batasan me zai biyo baya game da takalmin qafarta ba.
Daga qofar dakin innar ta tsaya
"Miwarti ɗilaulake inna(na dawo daga kiwo inna)" shuru taji,hakan yasa ta sake maimaitawa