← Book details Gurbin Ido Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 113

Sashe 24

Gurbin Ido Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ayi haquri anni" abinda dr yake fada kenan,don yasan da biyu take wannan fadan,tana tunanin kamar shike qin bada auren yaran nasa,bayan kuma yaran da kansu suke sha'awar karatu shi yasa ya qyale kowacce da zabinsa,uwa uba ma duka duka salma hafsat da laila ne a makarantun gaba da secondary,samma hafsa nadiya fa'iza da khadija sune 'yan candyn bana,zahra'u na ss one,sai rahama dake j.s,mazan kuwa dukkansu ba wanda ya gama jami'a banda ja'afar da haisam,sai Mahmoud dake ajin qarshe

"Yanzu fisabillahi....salma zaman me take?,shi karatun da take cewa akayi bashi yuwuwa ta qarasashi cikin dakinta?"

"Ta fiddo wanda takeso anni,ai baza'a qi aurar da ita ba"

"To ta fitar kuma shi take ta raragefan gaya maka kai da uwar tata" qas amma tayi da kanta,wal'alla ta gayawa anni sunyi zancan da ita kenan

"To ba damuwa anni,zanyi magana da umar(qaninsa kenan me bi masa),saita turashi can yaje ya gaidasu"

"To ba laifi" annin ta fada tana sassautan fadan,dai dai sanda salma tayi dake labe daga waje tayi tsallen dadi,anni tasu,anni ta wajensu,ayi tsiya ayi dadi,ga tsiya ga aiki,lallai yau dole ta yiwa annin wani tagomashi,saita juya cikin jin dadi zuwa ma'ajiyar motocin gidan,inda driver yake jiranta,ranta fari qal.

Daga can falo kuwa duban dr anni ta sakeyi

"Shi kuma jabiru da ja'afar fa?,da aka barsu suke zaune a wata uwa duniya,ga wancan qaton tuzurun haisam?" Miqewa amma tayi saboda kara da yakana irin tata,tana ganin ya kamata ta basu waje suyi maganrsu sosai

"Ina kuma zuwa?" Anni ta fada tana binta da kallo

"Zan duba meye baku dashi a kitchen"

"Idan kin shiga,kiyi waya can gidansu marigayiya,ya kamata a dawo da amna,jimawar da tayi a can wannan karon tayi yawa"

"To anni" ta amsa mata cikin girmamawa tayi ciki,dawo da dubanta tayi ga dr marwan tana tattara hankalinta sosai a kansa sanda ya fara mata bayani

"Maganar da nakeso muyi kenan.....a jiya da kika sameni da baqi kamar yadda na gaya miki ministern ilimi ne na qasa ya kawomin ziyara,bayan mun gama tattaunawa kan batutuwa irin namu,sai kuma ya jefomin maganar diyarsa unaisa,ya yimin tayin aurenta da ja'afar kamar sanda ya taba yimin a baya ban karba ba,lokacin ja'afar din yana aviation school,magana kuma tayi nisa tsakaninsa da marigayiya,to a yanzun inajin nauyi na sake qin karba din,kada yaga kamar banason hada zuri'a ne dashi ko kuma wani abu makamancin haka,na amsa masa ne duba da cewa gaba dayanmu dama muna laluben masa abokiyar zaman da zata iya zama dashi bisa juriya da kuma haquri kan sauyin hali da dabi'arsa,na kuma tabbatar kema idan kikaji hakan zaki farinciki,tunda burinmu kenan gaba daya"

Shuru anni tayi tana duban dr marwan,bawai don yayi kuskure ko kuma maganganunsa ba'a kan hanya suke ba,a'a......saidai tana tunanin wace unaisa?,akwai yiwuwar samun dacewar zama tsakaninta da ja'afar din?,uwa uba kuma ga batun maimunatu da take tafe dashi,sai takega kamar akwai matsala.

_To masu karatu,muje zuwa,shin al'amarin zai yiwu?,duk da bamusan wacece unaisa ba,abbi baisan wace maimunatu ba,kamar yadda wanda aketa abun a kansa baisan wainar da ake toyawa bama_
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: *17*

"Ni ai tuni na samarwa ja'afar matar aure"anni ta fada kanta tsaye,ba tare data jira komai ba ta dora

"Ire irensu unaisa ba daya ba ba biyu ba......amma sun kasa jumuri da juriya da kuma samar mana da abinda mukeso" anni ta fada cikin cikakkiyar nutsuwa da bawa zancan muhimmanci,har yanzu ita dr marwan yake kalla,ganin haka ya sanyata ta dora

"Eh,hakan yasa na sauya shawara bisa hasashen ramatu" nan ta ware masa komai kan hasashen yuuma,da yadda ta gamsu da maganarta,da kuma yadda ya zamana tashin farko maimunatu ce ta fara zuwa mata zuciya da ranta,mizani da ma'aunai masu yawa da maimunatun ta hau taga kuma tabbas ta dave da matsayin matar ja'afar.

Cikin nuna gamsuwa dr marwan yake gyada kai,dukka hasashen annin dama abinda ta aikata yayi dai dai da nasa ra'ayin

"Saidai duk wanda keson naka yakeson hada jini da kai ba qaramin masoyinki bane,sa'an nan wannan ba shine karon farko da ya nuna sha'awarsa kan hakan ba,to bai kamata mu watsa masa qasa a ido ba,kuma namiji mijin mace hudu ne ai,fatanmu shine Allah yasa a dace,yasa qarshen matsalar kenan" kai abbi ya gyada

"Gaskiya ne anni,Allah ya saka da alkhairi,ya qara girma"

"Banga abun godiya ba marwan,wajibi na nayi,babu abinda bazanyi ba saboda rayuwar ahalina matuqar bai sabawa shari'a ba,yanzu abu daya ya rage,ja'afar ya dawo cikinmu,koda zai koma sai komai ya dai daita,don ban gamsu mu bashi yaran mutane ya tafi dasu har wata uwa duniya ba"

"Gaskiya ne anni,hakan yayi"

"Shikenan,zan sa a kiramin jabirun ko zuwa anjima ne".

Dai dai lokacin maimunatu ke fitowa daga dakinta zuwa falon,tayi wankanta ta shirya tsaf bayan baba tabawa ta leqa da safen sun gaisa,ta kuma umarceta da yin wankan,mamaki ne yaketa kasheta,duka duka yaushe tayi wankan jiya?awa nawa ne a tsakani?,duk da hakan bata musa ba tayi kamar yadda baba tabawa ta umarceta,ta kuma shirya kamar jiya,saidai yau din haskenta ya sake fitowa fiye da jiya.

Da murmushi anni ke kallonta sanda take isowa wajen,daga nesa dasu ta zube har qasa tana gaidasu,abbi baisan wace ba,amma ya amsa mata cikin kulawa kafin ya maida kansa ga labaran qasa da ake gabatarwa a tashar NTA da ya dauki hankalinsa.

Cikin kulawa anni itama ta amsa

"Ya kwanan baqunta?" Ta tambayeta cikin salon jan mutum a jiki da kuma son ya sake,murmushi kawai tayi mata tana sad da kanta qasa

"Kinsan kitchen ai,leqa kice aishatu tazo,ta taho da qarin plates"

"Toh" maimunatun ta amsa tana miqewa a nutse tayi kitchen din.

Kafin ta qarasa tadan dinga jiyo hirarraki da alama akwai mutane a kitchen din,ta saka kanta a hankali bakinta dauke da sallama,abinda yaja hankalin amma dake tsaye suna magana da baaba tabawa,hannunta dauke da wata roba tana duba rubutun jiki.

Waiwayowa tayi,sai suka hada idanu da maimunatu,dan zubawa maimunatun idanu tayi,tana mamakin jin irin muryar data sani daga gareta,amma kuma batasan fuskar ba,bata taba ganinta ba.

Gaisuwar da take mata ta amsa cikin kulawa,sannan ta maida dubanta ga robar hannun nata,saidai kuma hankalinta naga muryar tata sanda take gayawa baaba tabawa anni ce ta aikota ta kira wata,kasa fadar sunan tayi kai tsaye,saboda suna ne dake da girma da kima a idanunta

"Yanzun bansan wa anni ke nema cikin madafa ba,kin kuma kasa fadi,hala sunan yana da nauyi a wajenki maimunatu" murmushi tayi a takure gami da jin nauyinsu su duka,musamman amma da hakanan taji tayi mata kwarjini.

Murmushi amma tayi
"Falon zan koma,muje naji wanda ake kira....tabawa qarasa aikinki,idan kin gama ki sameni keda bara'atu a sassana,zaku yimin gyaran wardrobe"

"To in sha Allah" haka suka jero,amma tana gaba maimunatu tana binta a baya,har suka qaraso falon

"Baquwar taki ta kasa faden wanda kk nema anni" amma ta fada tana zama daura da dr cikin shirin serving dinsu abincin data kawo musun,murmushi anni tayi

"Ke na aika ta kiramin,hala kasa fadin sunan tayi" gyada kai amma tayi

"Eh wallahi,anni ina kika samo mana bafullatar usul"

"Daga garinsu ramatu,gata nan don Allah aishatu,inaso a kulamin da ita da kyau,so nake ta zama 'yar gida tamkar su salma"

"In sha Allah"amma ta fada tana dan sake kallon maimunatu kadan,wadda kanta yake qasa har lokacin,sai kuma ta miqe,don a takure take,ba zata iya zama cikinsu ba.

Anni na shirin tsaidata don taci abinci a cikinsu tabawa ta fito ta kirayeta zuwa kitchen,abinda yasa anni ta qyalesu,ta maida kanta ga surukuwarta da danta.

Cikin yanayi na shaquwa da kuma fahimtar juna suke cin abincin,suna kuma tattaunawa kan lamuran rayuwa wanda suka shafesu,amma na gefe ba tare data sanya musu baki ba,wannan daha daga cikin halayyarta kenan.

Gab da zasu gama akayi sallama cikin falon,kyakkyawan matashine,yana da white skin hakanan giant ne shi sosai,kamanninsa na zahiri shi da dr Marwan sun bayyana.

Yayi dressing very neat cike da tsafta kamun kai nutsuwa gami da zallar ilimi,hannunsa daya riqe da lab coat dake bayyana cewa shi din tabbas likita ne,a nutsensa sannan cikin girmamawa ya tube takalman qafarsa ya qaraso falon,ya duqa ya fara gaida anni sannan dr sai amma.

Kansa yadan shafa kadan da yasha saisaye me kyau

"Anni,zan samu sauran abinci kuwa?" Kai tsaye anni ta kalla amma

"Bakuyi girki ba yau aishatu?"

"Munyi anni,sanda zan fito ma na leqasu suna gab da gamawa,zuwa yanzu nasan sun gama" qaramin tsaki taja

"Shine wannan qaton gardin zaizo ya sani gaba da tambayar abinci?....kaga idan zaka wuce gwara ka wuce,kuci a waje kamar yadda kuka saba,tunda haka kuka zabarwa kanku" dama yasan za'a rina,tsautsayi yasa yayi mata maganar,tun kafin ta tafi adamawa dama taketa rikici dasu,aure kawai takeso wai kowannensu yayi,wani lokaci sai yaji gwara ma dasu JJ suka basa nan,sun huta da ciwon bakinta.

Idanun dr marwan dake a wajen ya sanyashi miqewa yana sake shafa qeyarsa hadi da cewa

"Allah ya baki haquri"

"O'o'o'o,na kusa yiwa tufkar hanci ai"

"Fitarmin da briefcase din nan,ka cewa muslimu ya tada motar gani nan fitowa" cewar dr marwan,sai haisam ya qarasa ya dauka jakar ya musu sallama ya fice,amma tana masa addu'ar Allah ya tsare.

Kusan idan da sabo amma ta saba raka dr koda a gaban anni ne,idan ma bata je ba zata ce ita ta tashi taje,don haka yanzun ma ta tako masa har zuwa farfajiyar dake sassan annin

"Da gaske wannan karon anni ta tada wannan rigimar kan yaran nan,gaba dayansu so take a kauda su" rausayar da aki amma tayi

"Eh banga laifinta ba,tunda abinda ya kamata kenan dama ayi,kowannensu ya kamata zuwa yanxu ace bashi kadai bane"

"Musamman ja'afar da yake da buqatuwa ta kowanne bangare" dr ya fada don yasan daya daga cikin abubuwan da amma ke kwana dashi ta tashi dashi ne a cikin ranta,amma kuma yakana da kara ya sanya bata nunawa ko a fuska,amma shi din sau tari yasha jinta cikin tsakiyar dare tana kaiwa Allah kukanta akan matsalar yaron nasu,ya sani dole abun zai tabata sosai ya kuma dameta kamar kowacce irin uwa.

Kamar yadda ya zata din kuwa fuskarta ta dan sauya daga yadda take a daxun,hakan yasa cikin kulawa ya bata dukka hankalinsa
Chapter 24 · 0% Book details