← Book details Gurbin Ido Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 113

Sashe 27

Gurbin Ido Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mutum biyu dake zaune cikin falon,daya farar fata ne,bature sosai,mr denis evoy dan asalin qasar Belarus,yayin da dayan ya kasance baqar fata ne,wanda ya mallaki wata sassalkar fata me kyan gani da kuma burgewa ko cikin jinsin masu baqar fatar da ake kira da chocolate color,CAPTAIN JA'AFAR MARWAN KHALID AKKO qwararren kuma sanannen matuqin jirgin sama wanda ya ajjiye aikinsa,ya kuma yi switching kansa ya zuwa babban dan kasuwa,mamallakin kamfanoni dake samar da manyan gine gine na manyan ma'aikatu jami'o'i da manyan kamfanoni tituna dama gidaje,manyan gine gine masu ban sha'awa da qayatarwa.

Kyakkyawa ajin farko,irin kyan nan da a hankali yake bayyana kansa,wankan tarwada ne,a very husky man built like a football player,dukka qirar jikinsa na nuna alamun qarfi dake bayyana cikar mazantaka,yana da tsaho da kuma kauri dai dai misali wanda ya taimaka wajen sake boye ainihin tsahonsa,wasu irin shanyayyun idanu masu matuqar daukan hankali da kuma tafiya da imanin diya mace ko wacece ita,lafiyayyen qasumba ne dashi wansa bata rabo da saisaye da kuma gyara,gyaran da yake dacewa da kyawawan labbansa hancinsa me tsaho da tudu da kuma cikakkiyar girarsa,akwai wata suma ta musamman saman kansa mai sulbi da kuma sheqi ta asalin bafullace,wadda batayi yawa ba hakanan ba kadan bace.

Iya lafiyayyar fatarsa da kuma zara zaran yatsun qafarsa da na hannu kadai idan ka kalla zakasan cewa a huce yake cikin cikakkiyar wadata da kuma hutu,sau tari qannensa na sha'awar yanayin qafarsa dake luwai luwai kamar ta mace,saboda yadda ta samu hutu da kuma gyara,tako ina ja'afar ya cika cikakken namiji,wanda ya samu kusan cikar komai na rayuwa......saidai abu biyu daya rageshi,na farko mutum ne shi miskili na gasken gaske,irin miskilancin dake baiwa mutane da dama mamaki,ake kuma tunanin lokaci zaizo da zai sauya,saidai har zuwa lokacin da aka tsammaci zai sauya din yazo bai sauya ba,lokacin kuma ya sake zuwa ya hade masa da baqar qaddarar rasa matarsa da kuma diyarsa mafi soyuwa a wajensa,abinda ya sake canzashi kenan,ya kuma sake cillashi duniyar miskilanci.

Sosai yayi relaxing bayansa da jikin kujerar da yake zaune,very calmly yake kallon Mr Denis,sai kayi tsammanin duk duniya bashi da wata matsala a rayuwarsa dake barazana ga farinciki da kuma ci gabansa.
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 19

*Arewabooks:Huguma*
https://arewabooks.com/chapter?id=6351005edace9b957e575eaf

Saidai shi din haka yake,komai nasa a nutse yake cike da tsari da kuma nutsuwar,yana duban mr denis ne jabir dake jingine da fridge shima yana nazarinsa,cikin kwanakin nan gaba daya aikin ja'afar din kenan,ya dawo da dukka hankalinsa akan kamfaninsa,ganawa yake tayi da mutane daban daban duka akan kamfanin,wani irin huge change yake gani tatare dashi a dare daya,sau tari yakanyi sha'awar inama ace ja'afar din ya tabbata a haka?,wasu lokutan a baya sai yayi kamar zaici gaba da rayuwarsa kamar kowa,sai kuma abun ya sake tabarbarewa,but surely a wannan karon yana ganin yanayin kamar ya banbamta da na baya,ko wannan din zai dore?.

Murmushi jabir ya saki,yana dora cup din saman fridge din sanda yaji mr denis na complain kan cewa

"Sir, you didn't say anything since we start the negotiation" a ransa yake cewa da alama mr denis ja'afar din baqo ne a wajensa,sai ya fara takawa zuwa inda suke zaunen,gab kuma da zai qarasa wayar ja'afar din ta dauki ruri kiran anni ya shigo.

Da idanu kawai ya kalla wayar,sai da yaga sunan me kiran sannan ya miqa hannu a nutse ya dauka,ya kalli mr denis

"Excuse me" ya fada da wata deep and husky voice,saidai kuma akwai taushi da laushi daya cika muryar.

Shi ya fara yiwa annin sallama cikin ginshira da nutsuwa gami da wani irin kamun kai kamar mace,daga can sashen anni ta amsa tana sauke ajiyar zuciya

"Anya?,anya babban mutum?" Anni ta fada tana nuni da yatsanta kamar yana gabanta

"Barka da warhaka anni" yayi fatali da zancanta ya maye gurbinsa da gaisuwa

"Barka kadai,kuna lafiya?"

"Alhamdulillahi,fatan kowa yana lafiya"

"Lafiyar dai da sauqi" anni ta fada zuciyarta fal kewa da kuma rashin dadi kan sauyawarsa

"Subhanallah,wani abu ya faru ne?" Ya tambayeta yana gyara zamansa kadan gami da yamutsa fuskarsa,abinda yasa girarsa dake cike da gashi ta kusan hadewa waje daya

"Mene ma bai faru ba ja'afar?,fisabilillahi.....yanzu ace haka rayuwa zata ci gaba da tafiya" qaramar ajiyar zuciya ya sauke,shi kansa yana damuwa,yana damuwa kan yadda ya kasa moving forward yadda ya kamata,yana damuwa kan damuwar da mutanen nan masu muhimmanci a rayuwarsa ke shiga damuwa saboda shi,yana damuwa da yadda kowa hankalinsa yake kansa,to amma ya zaiyi?,shaheeda ta daban ce,tayi masa wani mummunan tasiri me matuqar qarfi da kaifi a rayuwarsa

"Aci gaba da tayamu da addu'a, everything will be okay in sha Allah" nannauyar ajiyar zuciya ta sauke

"Addu'a kam ita aketa yi babu fashi,babu kuma kama hannun yaro.....sai yaushe ka shirya dawowa qasarka?" Ta jefa masa tambayar da shi kansa baisan amsarta ba,gani yake kamar bashi da wani sauran zama da zaiyi a qasar

"Ban shiryama hakan ba anni,har yanzu da sauran lokaci" fuska tadan hade kadan

"Kamar yaya ja'afar?,bakasan har yanzu zamanka a nan bashi da wani amfani ba?,idan kuma akwai ka gayamin"ta masa tambyar da salon titsiye,maimakon ya amsa mata sai ya sanya hannu saman kansa yana shafa lallausar sumarsa

"Ina amna?" Kamar tace masa sai yanzu zai tuna da ita?,sai kuma ta bari,don a yanzun babu abinda take da buqata irin dawowarsa

"Dazun maimunatu ta kaita wajen Aishatu"

"okay.......aci gaba da yimin addu'a,ita nafi buqata,am little busy,zan kiraki anni"

"Ja'afar!" Ta kirayeshi da kakkausar murya

"Naam"

"Ina jiran kiranka,akwai magana me muhimmanci da nakeso muyi dakai,ka tabbatar kome kakeyi ka kirani bayan ka kammalashi" kai ya jinjina,domin annin mutun ce me kima a idanunsa,ba kasafai yake mata kallon kaka ba,yafi mata kallon uwa

"In sha Allah" daga haka suka yanke wayar,yana dan tunani cikin ransa wacce magana zasuyi da annin?,duk da jikinsa ya bashi tatsuniyar gizo dai ba zata wuce ta qoqi ba.

Sanda yake qoqarin kiran ammansa yaji annin ta kirayi jabir,baisan me take ce masa ba,saidai jabir din ya tashi daga wajen ya fita yana amsa wayar annin.

Saida amma ta sauke ajiyar zuciya sanda taga kiranja'afar din nata,abune me matuqar wuya ta daga waya ta kirayeshi,saboda zallar kara da yakana irin tata,zamantowarsa dan fari a wajenta,ta ajjiye rigar amna da take ninkewa wadda yarinyar ta cire yanzun ta dauki wayar.

Kamar ko yaushe cikin girmamawa da qanqan da kai ya gaidata,ta amsa masa cikin nuna kulawa tare da tambayarsa jikinsa,wanda daga nan bata iya qara cewa komai ba,sai shine ya tambayi amna

"Yanzun nan maimunatu tazo ta dauketa suka fita"

"Okay amma" yayi mata sallama yana ajjiye wayar

"Maimunatu,maimunatu dai?,wacece haka?" sai yaji ransa yadan sosu,don yaso jin muryar yarinyar,yayi matuqar kewarta har baisan iyaka ba,yanason yazo ko don ita,amma duk sanda ya ganta tana karya masa gwiwa ne,don tana tuna masa da mahaifiyarsa da kuma 'yar uwar tagwaitakarta.

Last time da ya kira haka akace tana wajen maimunatu,har kusan sau uku yana kira amma ana sake gaya masa tana wajenta,abinda ba al'adarsa bace maimaita kiran waya,wacece ita din ma?,amsar da baisan ta ba,haka kawai yaji kansa ya dauki zafi,sai ya dubi mr denis

"I heard everything you said,i need a time to think about what we discuss,i will contact you " kai mr denis ya kada masa,sannan ya bashi hannu sukayi musabaha,me denis ya tattare takardunsa ya masa sallama ya fice zuwa qofar gidan,inda PA dinsa ke zaune cikin mota yana jiransa.

Zazzafar iska ya furzar daga bakinsa wadda ta fito hade da sassanyan qamshin alawa me taste din mint da baya rabo da ita,hannunsa a saman goshinsa yana murzawa a hankali,ya daga shanyayyun kyawawan idanunsa ya aza kan agogon dake manne a falon,wanda yake nuna lokaci daga qasa kuma kwanan wata.

Duk rana irin ta yau rana ce da yake tafiya Istanbul ya kwana,washegari ya shiga ziyartar guraren tarihi da suka shafi annabawa da sahabbai,da wahala yayi missing ranar ba tare da yaje ba,abune me muhimmanci cikin rayuwarsa,yana daya daga cikin ababen tarihin da shaheeda ta barwa rayuwarsa,ita ta koya masa hakan,ita ta sanar dashi wanzuwar wajen,sai ya miqe da hanzarinsa dake nuna zallar lafiya da kuma cikar kuzari,ya dauki wayarsa da kuma agogon hannunsa dake saman table ya nufi dakinsa,dai dai lokaci jabir ya dawo falon,yabi hanyar da kallo,sai kawai ya rufa masa baya.

Goye yarinyar take a bayan maimunatu,suna takowa. Ahankali daga sassan amma zuwa wajen anni,tun sanda ta fuskanci anni waya zatayi ta zame daga dakin,ta kuma fake da dauko amna,hakan tafi nutsuwa da hakan,ko babu komai annin zata sake tayi wayarta yadda ya kamata,tun annin tana qorafi harta saba,indai wannan ne halin maimunatu ne.

Dariya yarinyar keta yi abinta,hankali kwancw tana jin dadin labarin da maimunatu ke bata.

Kusan minti goma kenan da dawowarsa cikin gidan,amma bai shiga ciki ba,ya tsaya daga bakin motarsa yana amsa waya,hannunsa dauke da briefcase dinsa da kuma lab coat,harda qarin baqar leda.

Siririyar muryarta dake cike da wani irin taushi ce ta ratso ta inda yake tsaye,abinda yaja hankalinsa kenan,ya daga kansa a hankali yana dubansu daga inda suke takowa.

Sanye take da skert high waisted wanda ya kama qugunta ya kuma baje sosai daga qasa,sai wadatacciyar rigarsa me hannu wanda ya tsaya mata iya gwiwar hannunta,kanta lullube yake da mini hijab wanda shima ya taimaka wajen suturce jikinta,saidai kuma yayi matuqar haskata kasancewarsa peach color.

Samun kansa yayi da binta da kallo,dan qaramin bakinta me siraran tausasan labba suna motsawa,tana da wani irin kyau me sanyi da fusgar hankali,tun ranar da ya fara ganinta ya tantance hakan,ta dauki hankalinsa ta kuma burge shi qwarai,duk da kasancewarsa mutum da ba kasafai mata ke burgeshi ba,bama shi kadai ba,kusan duk haka mazan gidansu suke,dalili da ya sanya ake musu kallon masu jin kai kenan

"La la la,kika yarda kike goyata a bayanki saita karya miki baya?" Maganar haisam ya ratsa kunnenta sanda take shirin giftashi ba tare data kula da tsaiwarsa a wajen ba,hada idanu sukayi,ya bita da murmushi,sai tayi maza ta janye idanunta tana sakin wani qaramin murmushin ba tare da tace komai ba.

Gyara tsaiwarsa yayi,yana maida wayarsa gaban aljihun rigarsa tare da sake cewa
Chapter 27 · 0% Book details