Sashe 6
Gobe Da Nisa Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Da safiyar ranar lahadi bacci suka sha kamar babu gobe, musamman Mariya ita ce ƙarshen farkawa wajen ƙarfe sha biyu saura mintuna ashirin, tayi mamakin baccin da tayi, amma idan ta tuna bata kwanta da wuri ba kuma bata samun bacci kwanakin ba yasa bai dameta ba.
Tana farkawa wanka kawai tayi ta fito tasa kaya ta fita, wasu suna falo wasu kuma alama suna ɗaki. Kusa da Umma ta ƙarasa tana gaishe da ita, ta amsa mata tana cewa.
"Kinsha bacci."
Murmushi kawai Mariya tayi ta miƙe ta wuce dining, abinci ta duba taga babu sai guntu. Kitchen ta wuce ta dafa tea ta fara sha don yunwa, kafin ta ɗaura noodles. Tana tsaye ya dahu ta kwashe ta fito falon, zama tayi a dining ta fara ci.
Ta kusa cinyewa Abba yayi sallama ya shigo falon, cak ta tsaya da cin abincin bugun zuciya ya ziyarceta.
Abba da ya hangota bayan amsa gaisuwar yaransa da ya hanya ya ƙarasa dining ɗin, kujera yaja ya zauna yana faɗin.
"Me kike ci haka yanzu? Breakfast sai ƙarfe sha biyu Mariya, ba kya tsoron ulcer?"
Da ƙyar Mariya ta girgiza kanta, murya ƙasa ƙasa ta ce.
"Ina kwana. Ya hanya?" Sai yanzu tasan ma yayi tafiya, shi yasa jiya bai kwana a gida ba har dare suka kwanta bai shigo ba.
Ruwan da ta ajiye a bottle ya ɗauka ya buɗe bottles ɗin, bai fara sha ba sai da yace. "Hanya lafiya lau."
Sannan yasha ruwan rabi ya ajiye sauran ya tura mata gabanta.
Mariya miƙewa tayi ɗauke da plate ɗin gabanta, ta wuce kitchen ta ajiye. Wani ruwan ta ɗauka tasha ta jefa goran a dustbing, sannan ta fito ta ƙarasa dining inda Umma ta maye gurbin inda take, guntun ruwan bottles da Abba ya ajiye ta ɗauka ta wuce ɗakinsu dashi.
Abba da kallo ya bita fuskarsa ɗauke da murmushi. Umma da take kallon su tayi murmushi ta ce.
"Jan ajin ƴarka har na gida bai bari ba."
Maganar Umma yasa ya maido da hankalinsa kanta, ya faɗaɗa murmushinsa sannan ya ce.
"Hakan ya yi, gwara tayi ta gara kan yan maza manya da yara."
Dariya ƙasa ƙasa Umma tayi don yadda kaf yaran yafi damuwa da Mariya da lamuranta, har wasu suna nuna kishin yafi sonta, sai dai yayi murmushi domin ai duk yaransa ne bai ga abin bambamci ba, Mariya kuma so yake tana sakewa dashi tamkar sauran.
...
Haka suka gama wunin ranar babu inda suka je. Mariya ba ta ƙara fitowa ba sai da taji wani yunwar, da ƙyar ta fito bisa matsawar Haneefa suka fito suka ci abinci sannan ta koma ɗaki.
Da dare kam ƙin fita tayi, da taga Haneefa zata matsa mata kawai ta ɗauko file din case din Isah Hamza ta fara dubawa. Dole yasa Haneefa barinta ta fice, tana gani ta fita ta mayar ta rufe ta ajiye.
Miƙewa tayi ta gabatar da sallar isha'i, tayi shirin bacci ta haye gado ta kwanta abinta, so take bacci ya ɗauketa don samun isashshen bacci domin farkawa da wuri ta tafi aiki akan lokaci karta makara.
#vote
#comment
GOBE DA NISA
Page 6
Na Pharty BB
Da sallama ya shigo babban falon gidansu cikin shirin fita aiki kamar kullum, da mahaifiyarsa da ƙannensa mata da suke zaune ya fara cin karo, suna ganinsa suka gimtse dariyar da suke, musamman Nabeela da ita ce kan gaba na dalilin dariyar nasu da yake cike da farin ciki.
Ciki ya ƙarasa sai lokacin suka lura da wacce take bin bayansa, ita ma cikin shirin fita nata aikin take. Take fara'ar fuskarsu ta ɗauke banda na Ammi.
Kujera Waliy ya samu ya zauna, wacce suka shigo tare ta zauna a hannun kujeran da yake. Kamar kullum shi ya fara gaishe da Ammi sannan ita, duk da abin yana sosa ran Ammi haka ta amsa don karta nunawa Waliy ɓacin ranta akan Rumana. Sannan su Nabeela suka gaida su.
Rumana ce ta fara miƙewa, ta kalli Waliy tana gyara siririn gyalen kanta tace. "B zan yi latti fa, mu tafi."
Miƙewa ya yi, ya kalli Ammi da ta ɗauke idonta ya ce. "Ammi zamu wuce."
"Allah ya kiyaye ya yi jagora." Ta faɗa musu tana dawo da dubanta kansu.
Murmushi Waliy yayi da ya ƙara fitar da kamilalliyar fuskarsa mai tsorata mutum, ya juya ya fice yabi bayan Rumana da tuni ta fice.
A harabar gidan ya sameta jingine a jikin motarta, wajenta ya ƙarasa ya tsaya a gabanta. Fuskarsa a haɗe kamar ba yanzu ya gama murmushi ba. Wani kallo ya aika mata sannan ya buɗe baki ya ce.
"Wai yaushe za kiyi hankali Ruman? Zamu ɓata ina faɗa miki idan ba za ki ɗauki mahaifiyata da daraja ba."
"Me nayi B? Naga dai gaisuwa ce na gaisheta." Ta faɗa da Hausarta da ba ya fita tana kallonsa. Don ita gaskiyarta ba ta ga wani abin da tayi ba, amma shi kullum faɗarsa bata ba wa mahaifiyarsa daraja. Kuma duk safiya tana shiga ta gaisheta sai kuma washegarin da safe, ita ma yanayin aikinta baya barinta wuni a gidan sai yamma take dawowa, ta dawo kuma fta gaji.
Tsakin Waliy da barinsa wajenta yasa ta kallonsa taga ya wuce wajen motarsa. Kwafa tayi ta buɗe nata ta shiga, tana zaune zai zo ya bata haƙuri don tasan baya iya dogon fushi da ita saboda ƙaunarta da yake tun tushe.
Haka Waliy ya fice a gidan cikin jin haushin Rumana, abin nata ya fara ba shi haushi, duk da yana mata uzurin yanayin tashinta kenan babu kwaba da kuma al'adun inda ta taso.
Yasan ba don son da take mishi tun bata san kanta ba da babu abin da zai sakata baro ƴan uwanta, iyayenta ta biyo shi don aurensa da burin zama dashi.
Tana farkawa wanka kawai tayi ta fito tasa kaya ta fita, wasu suna falo wasu kuma alama suna ɗaki. Kusa da Umma ta ƙarasa tana gaishe da ita, ta amsa mata tana cewa.
"Kinsha bacci."
Murmushi kawai Mariya tayi ta miƙe ta wuce dining, abinci ta duba taga babu sai guntu. Kitchen ta wuce ta dafa tea ta fara sha don yunwa, kafin ta ɗaura noodles. Tana tsaye ya dahu ta kwashe ta fito falon, zama tayi a dining ta fara ci.
Ta kusa cinyewa Abba yayi sallama ya shigo falon, cak ta tsaya da cin abincin bugun zuciya ya ziyarceta.
Abba da ya hangota bayan amsa gaisuwar yaransa da ya hanya ya ƙarasa dining ɗin, kujera yaja ya zauna yana faɗin.
"Me kike ci haka yanzu? Breakfast sai ƙarfe sha biyu Mariya, ba kya tsoron ulcer?"
Da ƙyar Mariya ta girgiza kanta, murya ƙasa ƙasa ta ce.
"Ina kwana. Ya hanya?" Sai yanzu tasan ma yayi tafiya, shi yasa jiya bai kwana a gida ba har dare suka kwanta bai shigo ba.
Ruwan da ta ajiye a bottle ya ɗauka ya buɗe bottles ɗin, bai fara sha ba sai da yace. "Hanya lafiya lau."
Sannan yasha ruwan rabi ya ajiye sauran ya tura mata gabanta.
Mariya miƙewa tayi ɗauke da plate ɗin gabanta, ta wuce kitchen ta ajiye. Wani ruwan ta ɗauka tasha ta jefa goran a dustbing, sannan ta fito ta ƙarasa dining inda Umma ta maye gurbin inda take, guntun ruwan bottles da Abba ya ajiye ta ɗauka ta wuce ɗakinsu dashi.
Abba da kallo ya bita fuskarsa ɗauke da murmushi. Umma da take kallon su tayi murmushi ta ce.
"Jan ajin ƴarka har na gida bai bari ba."
Maganar Umma yasa ya maido da hankalinsa kanta, ya faɗaɗa murmushinsa sannan ya ce.
"Hakan ya yi, gwara tayi ta gara kan yan maza manya da yara."
Dariya ƙasa ƙasa Umma tayi don yadda kaf yaran yafi damuwa da Mariya da lamuranta, har wasu suna nuna kishin yafi sonta, sai dai yayi murmushi domin ai duk yaransa ne bai ga abin bambamci ba, Mariya kuma so yake tana sakewa dashi tamkar sauran.
...
Haka suka gama wunin ranar babu inda suka je. Mariya ba ta ƙara fitowa ba sai da taji wani yunwar, da ƙyar ta fito bisa matsawar Haneefa suka fito suka ci abinci sannan ta koma ɗaki.
Da dare kam ƙin fita tayi, da taga Haneefa zata matsa mata kawai ta ɗauko file din case din Isah Hamza ta fara dubawa. Dole yasa Haneefa barinta ta fice, tana gani ta fita ta mayar ta rufe ta ajiye.
Miƙewa tayi ta gabatar da sallar isha'i, tayi shirin bacci ta haye gado ta kwanta abinta, so take bacci ya ɗauketa don samun isashshen bacci domin farkawa da wuri ta tafi aiki akan lokaci karta makara.
#vote
#comment
GOBE DA NISA
Page 6
Na Pharty BB
Da sallama ya shigo babban falon gidansu cikin shirin fita aiki kamar kullum, da mahaifiyarsa da ƙannensa mata da suke zaune ya fara cin karo, suna ganinsa suka gimtse dariyar da suke, musamman Nabeela da ita ce kan gaba na dalilin dariyar nasu da yake cike da farin ciki.
Ciki ya ƙarasa sai lokacin suka lura da wacce take bin bayansa, ita ma cikin shirin fita nata aikin take. Take fara'ar fuskarsu ta ɗauke banda na Ammi.
Kujera Waliy ya samu ya zauna, wacce suka shigo tare ta zauna a hannun kujeran da yake. Kamar kullum shi ya fara gaishe da Ammi sannan ita, duk da abin yana sosa ran Ammi haka ta amsa don karta nunawa Waliy ɓacin ranta akan Rumana. Sannan su Nabeela suka gaida su.
Rumana ce ta fara miƙewa, ta kalli Waliy tana gyara siririn gyalen kanta tace. "B zan yi latti fa, mu tafi."
Miƙewa ya yi, ya kalli Ammi da ta ɗauke idonta ya ce. "Ammi zamu wuce."
"Allah ya kiyaye ya yi jagora." Ta faɗa musu tana dawo da dubanta kansu.
Murmushi Waliy yayi da ya ƙara fitar da kamilalliyar fuskarsa mai tsorata mutum, ya juya ya fice yabi bayan Rumana da tuni ta fice.
A harabar gidan ya sameta jingine a jikin motarta, wajenta ya ƙarasa ya tsaya a gabanta. Fuskarsa a haɗe kamar ba yanzu ya gama murmushi ba. Wani kallo ya aika mata sannan ya buɗe baki ya ce.
"Wai yaushe za kiyi hankali Ruman? Zamu ɓata ina faɗa miki idan ba za ki ɗauki mahaifiyata da daraja ba."
"Me nayi B? Naga dai gaisuwa ce na gaisheta." Ta faɗa da Hausarta da ba ya fita tana kallonsa. Don ita gaskiyarta ba ta ga wani abin da tayi ba, amma shi kullum faɗarsa bata ba wa mahaifiyarsa daraja. Kuma duk safiya tana shiga ta gaisheta sai kuma washegarin da safe, ita ma yanayin aikinta baya barinta wuni a gidan sai yamma take dawowa, ta dawo kuma fta gaji.
Tsakin Waliy da barinsa wajenta yasa ta kallonsa taga ya wuce wajen motarsa. Kwafa tayi ta buɗe nata ta shiga, tana zaune zai zo ya bata haƙuri don tasan baya iya dogon fushi da ita saboda ƙaunarta da yake tun tushe.
Haka Waliy ya fice a gidan cikin jin haushin Rumana, abin nata ya fara ba shi haushi, duk da yana mata uzurin yanayin tashinta kenan babu kwaba da kuma al'adun inda ta taso.
Yasan ba don son da take mishi tun bata san kanta ba da babu abin da zai sakata baro ƴan uwanta, iyayenta ta biyo shi don aurensa da burin zama dashi.