Sashe 3
Gobe Da Nisa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Mariya bayan barin office ɗinsa office ɗinsu ta wuce, zuciyarta cike da mamakin wannan aiki nasu, sai taji ma ya mata sauƙi da har tana cewa za taje musu tambayoyi.
Tana shiga zama ta yi ta ajiye handbag ɗinta da files ɗinda ya bata, ta lumshe idanuwanta ta buɗe tana kai hannu ta jawo file ɗin sama ta buɗe na farko ta buɗe.
Cikin nutsuwa ta fara karanta shari'ar da abin da ake ƙara, tabbas sabo ne kamar yadda ya faɗa don babu wani bayani ko ɗaya, dole ita za ta shiga ta fita ta nemo mafita.
'To kuma ya hanani zuwa musu tambayoyi.' Ta faɗa a zuci tana rufe files ɗin, ta ma rasa me za ta yi, duk yadda taso fassara kan aikinta ta ka sa, idan ya ɗauko zafi sai taga akasin hakan.
Ga wannan case ɗin dole tana buƙatar yin tambayoyi duba da yadda wanda yake ƙara an kama yana cell a station.
'To ni ya zan yi.' Ta faɗa a zuci, a zahiri kuma fuskarta ta bayyana damuwar da take ciki. Ta rasa mafita akan wannan abin, hakan yasa ta kasa tabuka komai akai, dole sai ta ƙara tunani akan mafita.
Jinginar da case ɗin ta yi gefe, ta kunna computer gabanta, bincike ta fara anan taga ya turo mata case biyun da ya bata ta email ɗinta kamar na farko. Buɗewa ta yi ta gani ta fita ta kashe computer.
Rasa abin yi yasa ta miƙe tabar office ɗin, masallaci ta nufa ganin ƙarfe ɗaya saura. Alwala ta yi ta shiga ganin akwai ɗaiɗaikun mutane, gefe ta samu inda babu mutane sosai ta zauna. Wayarta ta ciro a jaka tare da earpiece ta saka, ta nemo karatun Alkur'ani ta fara ji.
Idanuwanta lumshe tana saurara, wani nutsuwa da kwanciyar hankali yana shigarta, a hankali zuciyarta ta dawo mata da abin da ta gani ɗazu.
Buɗe idanuwanta ta yi da sauri jin yadda zuciyarta ta buga, sam ta daina fahimtar karatun jin zuciyarta ta faɗa wani tunani daban, hakan yasa ta zare earpiece ɗin kunnenta ta kashe, ta mayar wayar jaka.
Ta jima cikin tunanin abubuwan da suka wuce, ganin za ta haddasawa kanta wani damuwar yasa ta miƙe don fita, sai kuma daidai aka fara ƙiran sallah, dole ta koma ta zauna har aka gama ƙira.
Mintuna biyar da haka aka shiga masallaci don fara sallah, ire-irenta masu alwala suka yi jam'i suka fara bin sallah. Bayan an idar Mariya tayi addu'o'i ta shafa akan Allah ya cika mata burinta, ya bata mafita a kowane case. Miƙewa ta yi ta ɗauki jakarta ta fita a masallacin, wajen cin abinci ta nufa, bayan ta shiga ta zauna tasa aka kawo mata meatpie da drink na orange juice.
Cikin nutsuwa taci ta kammala ta miƙe, ta biya su sannan ta fita. Office ta koma ta samu matan biyu suna nan sauran basu dawo ba, zama ta yi bayan ta ce musu sannu.
Ƴar gefenta ta ce.
"Ke wai ba kya magana?"
Mariya kallonta tayi, tai murmushin da ya bayyana dimples ɗinta tace.
"Ina yi."
Baki ta taɓe jin amsar da ta bata, ta cigaba da aikinta. Haka ita ma Mariya ta ɗauke kanta ta cigaba da aikinta akan yadda za ta ɓullowa case ɗin nan. Murmushi tayi ba ta san lokacin da ya suɓuce mata ba na jin hukuncin da zuciyarta ta yanke mata.
Ƙarfe huɗu da rabi tabar office, kamar jiya napep ta tara ta koma gida. Bayan ta sauƙa ta ba shi kuɗinsa ta wuce cikin gida, da sallama ta tura ƙofar gida ta shiga, nan idanuwanta suka sauƙa samar Abba da yake zaune a bakin balcony nashi, hannunsa ɗauke da jarida.
Ɗauke kanta ta yi ta nuna tamkar ba ta ganshi ba ta nufi falon Umma.
Abba da kallo ya bita har ta shige, sai kuma ya mayar kansa kan abin da yake. Duk yadda yaso kawar da cewa bata ganshi bane ya kasa, zuciyarsa ta kasa gaskata hakan cewa Mariya ta ganshi ta ƙi gaishesa.
...
Mariya tana shiga falon babu kowa alama duk suna islamiyya, kai tsaye ɗakinsu ta wuce, ta samu Haneefa ta dawo suna zaune da Ummi Aisha. Sai hira suke wanda duk Ummi Aisha ce mai hiran. Sannu kawai ta musu suka amsa mata, ta cire hijab ɗinta ta ajiye jakarta ta wuce bathroom.
Wanka tayi ta ɗaura alwala ta fito ɗaure da towel, ta nufi wardrobe ɗinta ta buɗe ta ɗauki riga simple ta saka, ta saka hijab ta gabatar da sallar la'asar. Tana idarwa ta miƙe ta fita don yunwa take ji, dining ta nufa ta buɗe abinci ta zuba ta ɗauka plate ɗin ta koma ɗaki. A bakin gado ta zauna ta ɗaura plate din a cinyarta kafin ta fara ci.
Tayi loma kusan uku ta kalli Ummi Aisha ta ce."Ina Umma?"
Ummi Aisha da take daf da ita kwance ta ce.
"Ta fita gidan Aunti Laila dubawa Salim da Baba ƙarami kaya, wanda aka kawo basu mata ba."
Kai Mariya a ta jinjina ba tace komai ba, ta ci gaba da cin abincinta. Haneefa da take jinsu tabar abin da take ta kalli Mariya.
"Ya aikin? Akwai wahala?"
Murmushi Mariya ta yi, ta furzar numfashi a hankali sannan ta ce.
"Babu laifi."
Sanin iyakacin amsar yasa Haneefa ƙin cigaba da zancen, tasan yanzu ko ta matsa mata da tambaya amsar zai koma eh ko a'a.
Mariya sauran ragowar abincinta ta ƙarasa cinyewa ta miƙe, ta fitar plate ta dawo ɗakin lokacin an fara kiran sallar magriba. Sanin alwalarta yana nam kawai ta gabatar da sallah, bayan ta idar ta ɗauki wayarta jin yana ƙara.
Zakiyya ce ƴar Aunti Babie, ɗauka ta yi ta kafa a kunne tana mata sallama.
Daga can ta amsa tana tambayarta aiki. Mariya ita ma dai ce mata ta yi Allahamdulillahi kawai babu wani dogon zance. Sanin halinta yasa Zakiyyah yi mata sallama ta kashe wayarta.
Haka suka zauna har dare lokacin cin abinci, basu fita ba duk da suna jin hayaniyar su Ikhlas da Maryam, sai Baba ƙarami da Abba da Khadeeja, ga kukan Salim ɗan shekaru huɗu, Hassan da Hussain da Faruq suna makaranta a hostel.
Haneefa da Ummi Aisha sai ƙarfe takwas suka fita cin abinci. Mariya kam tace ta ƙoshi yanzu taci.
Ganin su biyu Umma da take bawa Salim abinci ta tambayesu.
"Ina Mariya?"
Ummi Aisha ta sanar mata cewa.
"Ai yanzu taci abinci."
Hakan yasa ta ci gaba da bawa Salim nashi, sauran wasu suna kallo wasu su wuce ɗakin baccinsu.
Bangaren Mariya miƙewa ta yi ta gabatar da sallar isha'i, ta canza kaya zuwa na bacci ta haye gado, addu'a tayi ta rufe idanuwanta don so take bacci ya ɗauketa.
A hankali kuma abin da ya faru tsakaninta da Barrister Waliy ya faɗo mata. Kamar yana kallonta ta taɓe baki, tana mamakin wasu da idan suka ga sunfi mutum su dinga nuna isa. Kawar da tunaninsa ta yi gefe, ta faɗa na yadda za ta ɓullowa case din, nanma kawarwa tayi ta shiga na wanda tayi lokacin tana masallaci.
Motsin taji yasa ta buɗe ido taga Haneefa ce ta shigo, mayar idanuwanta tayi ta rufe, a haka bacci ya ɗauketa ba tasan lokacin da dukkansu suka kwanta ba.
Ƙarfe ɗayan dare da minti goma.
A mugun firgice Mariya ta farka dalilin mafarkin da ta yi gamo dashi a baccinta, ta dafe kirjinta jin yadda yake bugu da ƙarfi gaske tamkar yau ta fara. Ganin ba gaske bane kamar kullum yasa ta karanto addu'a na neman cigaba da tsarin mafarkinta a gaske da mafarki.
Bayan ta gama ta kwanta tana matsawa jikin Haneefa sosai tamkar za ta shige mata. Ƙarshe ma ta ɗaga hannun Haneefa ta ɗaura a jikinta yadda ko me zai faru za taji itama. Daga haka wani baccin mai daɗi ya kwasheta.
#vote
#comment
GOBE DA NISA
Page 3
Na Pharty BB
Motsi da Mariya ta yi ne ya farkar da Haneefa, ta ji Mariya ta rumgumeta, ba ta iya hanata ba ta sake ƙarfin riƙeta a jikinta da kyau, domin mafarkin da Mariya take yi ta fara sabawa dashi, sai dai har yau ta ka sa tambayarta dalili, ta bar abin a mummunar mafarki ne da kowa yana yi. Haka suka koma bacci.
Da asubanin bayan sun gabatar da sallah basu koma ba, Mariya ta hau gyara kayanta, Haneefa ta tattare ɗakin tas, suka barwa Ummi Aisha shara tunda tana gida ita.
Wanka suka yi suka shirya zuwa aiki suka fita, a falo suka samu Umma da sauran yara da suka shirya zuwa makaranta. Gaishe da ita suka yi yaranma suka gaishe dasu, daga nan suka yi breakfast suka mata sallama suka fita a gidan.
A hanya suka rabu kowacce ta hau napep ta wuce wajen aikinta.
Mariya kasancewar yau tayi sauri sai bata damu ba, a cikin nutsuwa ta ƙarasa cikin office ɗinsu. Wayam ta gani alamar babu kowa amma kuma a buɗe. Agogon ɗaure a tsintsiyar hannunta ta duba taga takwas da kwata saura mintuna kafin tayi latti. Abin ne ya ɗaure mata kai da tunanin ko basu zo bane ganin lokaci yaja.
Rasa mai bata amsa yasa ta taɓe bakinta ta fara ƙoƙarin zama, kamar daga sama taji maganarsa. "Me ya hanaki zuwa meeting?"
Tana shiga zama ta yi ta ajiye handbag ɗinta da files ɗinda ya bata, ta lumshe idanuwanta ta buɗe tana kai hannu ta jawo file ɗin sama ta buɗe na farko ta buɗe.
Cikin nutsuwa ta fara karanta shari'ar da abin da ake ƙara, tabbas sabo ne kamar yadda ya faɗa don babu wani bayani ko ɗaya, dole ita za ta shiga ta fita ta nemo mafita.
'To kuma ya hanani zuwa musu tambayoyi.' Ta faɗa a zuci tana rufe files ɗin, ta ma rasa me za ta yi, duk yadda taso fassara kan aikinta ta ka sa, idan ya ɗauko zafi sai taga akasin hakan.
Ga wannan case ɗin dole tana buƙatar yin tambayoyi duba da yadda wanda yake ƙara an kama yana cell a station.
'To ni ya zan yi.' Ta faɗa a zuci, a zahiri kuma fuskarta ta bayyana damuwar da take ciki. Ta rasa mafita akan wannan abin, hakan yasa ta kasa tabuka komai akai, dole sai ta ƙara tunani akan mafita.
Jinginar da case ɗin ta yi gefe, ta kunna computer gabanta, bincike ta fara anan taga ya turo mata case biyun da ya bata ta email ɗinta kamar na farko. Buɗewa ta yi ta gani ta fita ta kashe computer.
Rasa abin yi yasa ta miƙe tabar office ɗin, masallaci ta nufa ganin ƙarfe ɗaya saura. Alwala ta yi ta shiga ganin akwai ɗaiɗaikun mutane, gefe ta samu inda babu mutane sosai ta zauna. Wayarta ta ciro a jaka tare da earpiece ta saka, ta nemo karatun Alkur'ani ta fara ji.
Idanuwanta lumshe tana saurara, wani nutsuwa da kwanciyar hankali yana shigarta, a hankali zuciyarta ta dawo mata da abin da ta gani ɗazu.
Buɗe idanuwanta ta yi da sauri jin yadda zuciyarta ta buga, sam ta daina fahimtar karatun jin zuciyarta ta faɗa wani tunani daban, hakan yasa ta zare earpiece ɗin kunnenta ta kashe, ta mayar wayar jaka.
Ta jima cikin tunanin abubuwan da suka wuce, ganin za ta haddasawa kanta wani damuwar yasa ta miƙe don fita, sai kuma daidai aka fara ƙiran sallah, dole ta koma ta zauna har aka gama ƙira.
Mintuna biyar da haka aka shiga masallaci don fara sallah, ire-irenta masu alwala suka yi jam'i suka fara bin sallah. Bayan an idar Mariya tayi addu'o'i ta shafa akan Allah ya cika mata burinta, ya bata mafita a kowane case. Miƙewa ta yi ta ɗauki jakarta ta fita a masallacin, wajen cin abinci ta nufa, bayan ta shiga ta zauna tasa aka kawo mata meatpie da drink na orange juice.
Cikin nutsuwa taci ta kammala ta miƙe, ta biya su sannan ta fita. Office ta koma ta samu matan biyu suna nan sauran basu dawo ba, zama ta yi bayan ta ce musu sannu.
Ƴar gefenta ta ce.
"Ke wai ba kya magana?"
Mariya kallonta tayi, tai murmushin da ya bayyana dimples ɗinta tace.
"Ina yi."
Baki ta taɓe jin amsar da ta bata, ta cigaba da aikinta. Haka ita ma Mariya ta ɗauke kanta ta cigaba da aikinta akan yadda za ta ɓullowa case ɗin nan. Murmushi tayi ba ta san lokacin da ya suɓuce mata ba na jin hukuncin da zuciyarta ta yanke mata.
Ƙarfe huɗu da rabi tabar office, kamar jiya napep ta tara ta koma gida. Bayan ta sauƙa ta ba shi kuɗinsa ta wuce cikin gida, da sallama ta tura ƙofar gida ta shiga, nan idanuwanta suka sauƙa samar Abba da yake zaune a bakin balcony nashi, hannunsa ɗauke da jarida.
Ɗauke kanta ta yi ta nuna tamkar ba ta ganshi ba ta nufi falon Umma.
Abba da kallo ya bita har ta shige, sai kuma ya mayar kansa kan abin da yake. Duk yadda yaso kawar da cewa bata ganshi bane ya kasa, zuciyarsa ta kasa gaskata hakan cewa Mariya ta ganshi ta ƙi gaishesa.
...
Mariya tana shiga falon babu kowa alama duk suna islamiyya, kai tsaye ɗakinsu ta wuce, ta samu Haneefa ta dawo suna zaune da Ummi Aisha. Sai hira suke wanda duk Ummi Aisha ce mai hiran. Sannu kawai ta musu suka amsa mata, ta cire hijab ɗinta ta ajiye jakarta ta wuce bathroom.
Wanka tayi ta ɗaura alwala ta fito ɗaure da towel, ta nufi wardrobe ɗinta ta buɗe ta ɗauki riga simple ta saka, ta saka hijab ta gabatar da sallar la'asar. Tana idarwa ta miƙe ta fita don yunwa take ji, dining ta nufa ta buɗe abinci ta zuba ta ɗauka plate ɗin ta koma ɗaki. A bakin gado ta zauna ta ɗaura plate din a cinyarta kafin ta fara ci.
Tayi loma kusan uku ta kalli Ummi Aisha ta ce."Ina Umma?"
Ummi Aisha da take daf da ita kwance ta ce.
"Ta fita gidan Aunti Laila dubawa Salim da Baba ƙarami kaya, wanda aka kawo basu mata ba."
Kai Mariya a ta jinjina ba tace komai ba, ta ci gaba da cin abincinta. Haneefa da take jinsu tabar abin da take ta kalli Mariya.
"Ya aikin? Akwai wahala?"
Murmushi Mariya ta yi, ta furzar numfashi a hankali sannan ta ce.
"Babu laifi."
Sanin iyakacin amsar yasa Haneefa ƙin cigaba da zancen, tasan yanzu ko ta matsa mata da tambaya amsar zai koma eh ko a'a.
Mariya sauran ragowar abincinta ta ƙarasa cinyewa ta miƙe, ta fitar plate ta dawo ɗakin lokacin an fara kiran sallar magriba. Sanin alwalarta yana nam kawai ta gabatar da sallah, bayan ta idar ta ɗauki wayarta jin yana ƙara.
Zakiyya ce ƴar Aunti Babie, ɗauka ta yi ta kafa a kunne tana mata sallama.
Daga can ta amsa tana tambayarta aiki. Mariya ita ma dai ce mata ta yi Allahamdulillahi kawai babu wani dogon zance. Sanin halinta yasa Zakiyyah yi mata sallama ta kashe wayarta.
Haka suka zauna har dare lokacin cin abinci, basu fita ba duk da suna jin hayaniyar su Ikhlas da Maryam, sai Baba ƙarami da Abba da Khadeeja, ga kukan Salim ɗan shekaru huɗu, Hassan da Hussain da Faruq suna makaranta a hostel.
Haneefa da Ummi Aisha sai ƙarfe takwas suka fita cin abinci. Mariya kam tace ta ƙoshi yanzu taci.
Ganin su biyu Umma da take bawa Salim abinci ta tambayesu.
"Ina Mariya?"
Ummi Aisha ta sanar mata cewa.
"Ai yanzu taci abinci."
Hakan yasa ta ci gaba da bawa Salim nashi, sauran wasu suna kallo wasu su wuce ɗakin baccinsu.
Bangaren Mariya miƙewa ta yi ta gabatar da sallar isha'i, ta canza kaya zuwa na bacci ta haye gado, addu'a tayi ta rufe idanuwanta don so take bacci ya ɗauketa.
A hankali kuma abin da ya faru tsakaninta da Barrister Waliy ya faɗo mata. Kamar yana kallonta ta taɓe baki, tana mamakin wasu da idan suka ga sunfi mutum su dinga nuna isa. Kawar da tunaninsa ta yi gefe, ta faɗa na yadda za ta ɓullowa case din, nanma kawarwa tayi ta shiga na wanda tayi lokacin tana masallaci.
Motsin taji yasa ta buɗe ido taga Haneefa ce ta shigo, mayar idanuwanta tayi ta rufe, a haka bacci ya ɗauketa ba tasan lokacin da dukkansu suka kwanta ba.
Ƙarfe ɗayan dare da minti goma.
A mugun firgice Mariya ta farka dalilin mafarkin da ta yi gamo dashi a baccinta, ta dafe kirjinta jin yadda yake bugu da ƙarfi gaske tamkar yau ta fara. Ganin ba gaske bane kamar kullum yasa ta karanto addu'a na neman cigaba da tsarin mafarkinta a gaske da mafarki.
Bayan ta gama ta kwanta tana matsawa jikin Haneefa sosai tamkar za ta shige mata. Ƙarshe ma ta ɗaga hannun Haneefa ta ɗaura a jikinta yadda ko me zai faru za taji itama. Daga haka wani baccin mai daɗi ya kwasheta.
#vote
#comment
GOBE DA NISA
Page 3
Na Pharty BB
Motsi da Mariya ta yi ne ya farkar da Haneefa, ta ji Mariya ta rumgumeta, ba ta iya hanata ba ta sake ƙarfin riƙeta a jikinta da kyau, domin mafarkin da Mariya take yi ta fara sabawa dashi, sai dai har yau ta ka sa tambayarta dalili, ta bar abin a mummunar mafarki ne da kowa yana yi. Haka suka koma bacci.
Da asubanin bayan sun gabatar da sallah basu koma ba, Mariya ta hau gyara kayanta, Haneefa ta tattare ɗakin tas, suka barwa Ummi Aisha shara tunda tana gida ita.
Wanka suka yi suka shirya zuwa aiki suka fita, a falo suka samu Umma da sauran yara da suka shirya zuwa makaranta. Gaishe da ita suka yi yaranma suka gaishe dasu, daga nan suka yi breakfast suka mata sallama suka fita a gidan.
A hanya suka rabu kowacce ta hau napep ta wuce wajen aikinta.
Mariya kasancewar yau tayi sauri sai bata damu ba, a cikin nutsuwa ta ƙarasa cikin office ɗinsu. Wayam ta gani alamar babu kowa amma kuma a buɗe. Agogon ɗaure a tsintsiyar hannunta ta duba taga takwas da kwata saura mintuna kafin tayi latti. Abin ne ya ɗaure mata kai da tunanin ko basu zo bane ganin lokaci yaja.
Rasa mai bata amsa yasa ta taɓe bakinta ta fara ƙoƙarin zama, kamar daga sama taji maganarsa. "Me ya hanaki zuwa meeting?"