Sashe 5
Gobe Da Nisa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Allahamdulillahi." Mariya ta faɗa tana miƙewa ta wuce ɗakinsu. Babu kowa, hakan yasa ta cire kayan jikinta ta faɗa bathroom.
Kamar kullum ruwa ta watsa ta ɗaura alwala ta fito ta saka doguwar riga ta gabatar da sallah, bayan ta idar ta fita falo. Dining ta nufa ta zuba abinci ta zauna ta hau ci anan saɓanin wani lokaci da take ci a ɗaki.
Tana jin hayaniyar su da surutunsa amma ko a bata tanka ba, sun san ba baki zata saka ba hakan yasa babu wanda yasata a hiran su.
Bayan ta gama cin abincinta ta miƙe ta kai plate ɗin kitchen, ta ɗauki ruwa a fridge ta fita ta wuce ɗakinsu. A bakin gado ta zauna, ta buɗe ruwan hannunta tasha kusan dukka ta ajiye sauran a bedside drawer.
Miƙewa tayi ta ɗauko files din data zo dashi ta haye tsakiyar gado, buɗewa tayi ta fara bin daki-daki na jawabin Isah Hamza tare da tambayoyin da ta rubuta.
Tambayoyi kaɗan ta rubuta cikin abinda ta fahimta ta rubuta, ta ɗauki files ɗin ta ajiye a guri mai kyau.
Kan gado ta kwanta bayan ta ɗauki wayarta ta fara dannawa, a haka har dare ya shiga babu abin da yake ɗagata sai sallah. Yau bayan sallar isha'i bata kwanta ba ta miƙe ta fita falo, duk da ba magana zata yi ba gwara ta zauna cikinsu tana saurara.
Sosai suke hira a tsakaninsu, musamman Ummi Aisha da Maryam da muryarsu yafi na kowa fita, ga Abba da Baba ƙarami ma suna nasu hiran, Haneefa ce take saka baki a rigimar Ummi Aisha da Maryam, Khadeeja ma ba mai yawan surutu bace hakan yasa jifa jifa take saka musu baki. Salim na tare da Umma.
Cak falon ya ɗauki shuru bisa sallamar da aka doka, gaba ɗaya suka zubawa ƙofar ido ganin mai shigowa musamman Mariya da taji muryar mai sallamar har tsakar kanta, wanda ya haddasa mata bugun zuciya.
#vote
#comment
GOBE DA NISA
Page 4
Na Pharty BB
A facing ɗinta ya zauna, yana jifanta da murmushin nan nasa mai tsinka zuciyarta ya amsa gaisuwarta, tare da tambayarta ya aiki.
Mariya kanta kawai ta girgiza alamar lafiya ta ka sa yin magana. Gaba ɗaya a takure take da zaman, hakan yasa ta miƙe tana cewa.
"Sai da safenku."
Umma ta amsa ta bita da kallo, ta juyo ta kalli Abba da ya bita Mariya da kallo ta ce.
"Wannan shegen miskilancin yarinyar nan naka ya ishe ni, ace mutum magana yana ba shi wahala."
Abba da yabi Mariya da kallo harta shige ɗaki ya juyo ya kalli Umma jin abin da ta faɗa, fuskarsa da murmushi ya ce. "Abin gado ne."
Umma baki ta taɓe ta miƙewa.
"Sai dai a wajenka." Tana faɗa tabar wajensa ta nufi fridge ta ɗauko mishi ruwa, sauran yaranma ɗaya bayan ɗaya suka miƙe suka shige ɗaki. Shigowarsa dama yasa gaba ɗaya suka nutsu, sallamarsa ne ta katse musu surutun su.
Ummi Aisha da ta shiga ɗakinsu ta zauna kusa da Mariya da take kwance saman gado idanuwanta rufe, kallonta tayi tana faɗin.
"Kinji kin ƙara taɓa Umma. Wai don Allah bakinki ba ya tsami?"
Mariya idanuwanta ta buɗe tana kallon Ummi Aisha, tamkar ba za ta tanka ba, tayi murmushi da ya bayyana dimples ɗinta sannan tace.
"Ina yi mana, kawai dai bana saka kaina hiran da bai shafe ni ba, sai kuma wanda bai game ni ba nake ƙin tankawa."
"A wajen aikinma haka kike musu?"
Ummi Aisha ta tambayeta ganin yau ta buɗe baki ta mata magana mai tsayi.
Girgiza kai Mariya tayi ta rufe idanuwanta, tasan idan ta biyewa Ummi Aisha sai su kwana surutu.
Fitowar Haneefa a bathroom yasa Ummi Aisha miƙewa ta shige bathroom don yin wanka. Haneefa bayan ta saka kayan baccinta ta zauna kusa da Mariya, buɗe ido Mariya ta yi ta kalleta ba tace komai ba.
Haneefa ta mata murmushi ta ce.
"Me ya faru naga kamar kina da damuwa."
Girgiza kai Mariya tayi sannan tace.
"Babu komai, gajiya ce."
Jin abin da ta faɗa yasa Haneefa hawa gadon sosai, ta kwanta gefen Mariya bata kara cewa komai ba.
Ita ma Mariya kwanciyarta ta gyara tana matsawa tsakiyar gado ta barwa Ummi Aisha ƙarshe don dama koyaushe ita ce a tsakiya sai idan Haneefa bata nan.
Dalilin yawan mafarkan da take masu firgitata ta farka yasa Haneefa take sakata tsakiyarsu, don da zaran ta farka itama sai taji wani lokaci, watarana kuma bata jinta har ta yi ta koma, shi yasa idan take da night duty kullum tunaninta yar uwartan ta kwana.
Haka Ummi Aisha ta fito ta gama shirin baccinta ta kashe wuta ta haye saman gado ta kwanta. Addu'a suka yi kafin dukkansu su kwanta.
Cikin ikon Allah yau har gari ya waye Mariya ba tayi mafarki ba balle ta farka, hakan ya musu daɗi dukkansu duk da dama takan jera kwanaki uku zuwa huɗu ba tayi ba.
Bayan sun gabatar da sallah kamar kullum suka tattare ɗakin suka shirya suka fito, Umma suka gaishe suka yi breakfast kafin su fita. Ɓangaren Abba suka nufa suka gaishe dashi wanda da farko Mariya kamar kar taje, amma ganin Haneefa yasa ta binta.
Bayan ya musu fatan alheri kafin su fito suka bar gida kowacce ta kama gabanta zuwa wajen aikinta.
Mariya yau ma akan case na Isah Hamza ta wuni, har aka tashi ta musu sallama ta dawo gida.
Haka kwanakin suka tafi a rayuwar ahlin kamar baya.
Mariya ta dage da zuwa aiki da take jajircewa akai don cikar nata burin, basu kara haɗuwa da Barrister Waliy ba.
Bai nemeta ba akan aikin da ya bata, hakan yasa ta kwantar da hankalinta take bin komai daki-daki wanda har ta kusa kammala na zargin Isah Hamza da ake yana sata a unguwar su, saura ɗayan.
A haka har aka shiga weekend, mai maimakon su huta amma Ummi Aisha ta kwakulo musu tafiya gidan ƙanwar Abba yini. Mariya haushinta taji sosai don ita kam burinta ta huta a weekend ɗin nan, kuma idan ta zauna ita ɗaya za a bari domin har su khadeeja da suke yara zasu je.
Dole yasa ta shirya cikin riga da skirt na lace blue da ash, ta yi amfani da ash mayafinta, sai ƙaramin handbags ɗinta kalar takalminta. Tayi kyau sosai domin Mariya akwai kyau da tsarin halitta mai burgewa, wanda da dama shi yake fisgar jama'a.
Haka Haneefa irin lace nata ta saka sai banbancin color, na Haneefa brown da mint green maimakon color irin na Mariya, sai kamminsu ya sake fitowa.
Bayan sun gama shiryawa Abba ya bada mota driver ya kaisu har gidan Aunti Yahanasu, tayi murnan ganin yaran yayan nata sosai, suka haɗu da yaran gidan sai suka cika gidan sosai da hayaniya, kowa ya kama abokinsa suna kuskus abinsu.
Mariya, Haneefa da Ummi Aisha su ma gefe ɗaya suka haɗe da ƴan biyun Aunti Yahanasu suka kafa cafta. Hira suke sosai, da ƙyar Mariya tayi ƙoƙarin sakewa take saka baki gudun su kafa nata chapter na rashin son magana.
Hakan ko ya musu daɗi har Hassana sai da ta tanka ta ce.
"Yau za ayi ruwa da kankara."
"Ko kuma gwamna zai zo gidanku ba."
Ummi Aisha ta faɗa, fahimtar zacen sauran suka kwashe da dariya, ban da Mariya data murmusa tana cije lips ɗinta, tasan da ita suke.
Suna wannan yanayi aka yi sallama aka shigo, tuni Haneefa ta haɗa rai jin mai yin sallamar, shi ko ganinta yasa ya ƙara faɗaɗa fara'ar fuskarsa ya ƙarasa wajensu.
Zama yayi facing ɗinta yana jifanta da murmushi, ita ko ta haɗa rai tamkar ba ita ba.
Ummi Aisha ce ta fara gaishe dashi ya juya yana amsawa, haka Mariya ma ta gaishe dashi, ya amsa sannan ya juya kan Haneefa.
"Ke ba za ki gaishe dani ba."
"Ina wuni."
Ta faɗa ƙasa ƙasa tana sake haɗa rai. Sam baya burgeta saboda halayensa, duk yadda ya matsa mata da ƙoƙon barar soyayyarsa, kuma rabi da kwata Mariya ke ƙara karfafa mata guiwar ƙin sa, daɗinta ɗaya babu wanda ya sani a iyayen don tasan zasu iya amincewa tuni.
Maganarsa yasa ta kalle shi ta ɗauke kanta, gaba ɗaya gani tayi ya ƙara lalacewa ya rame. Girgiza kanta tayi ta miƙe tabar wajen gaba ɗaya don yafi mata alheri.
Nafiq ya bita da kallo sannan ya juyo kan Mariya itama ta haɗa ran da yafi na Haneefa, hakan yasa ta sake mishi kwarjini fiye da kullum.
Ka sa mata magana yayi ya miƙe yabar wajen, hakan ya basu damar cigaba da hiransu ban da Mariya da zuciyarta da ƙwaƙwalwarta suka faɗa wani tunanin daban.
Tashinsu tsaye yasa ta dawo hankalinta, ta kallesu ba ta iya tambayarsu ba. Ummi Aisha da tasan halinta ta ce.
"Da kika kasa tambayar to ɗaki zamu je."
Babu musu ita ma ta miƙe suka shiga daƙi wajen Haneefa, kwance suka sameta suka ƙarasa suka zauna gefenta. Anan suka ci gaba da hiransu har azahar, suka yi sallah kafin su haɗu su fita zuwa kitchen suka haɗa hannu suka ɗaura abincin rana.
Wajen ƙarfe biyu da rabi suka gama suka fitarwa kowa nashi, suka ƙira yaran suka karɓa sauran nasu, sauran suka jera a dining bayan sun zuba nasu suka wuce ɗaki dashi.
Ranar sunyi wunin daɗi, sun yi hira, sun ci sun sha sun kawar da kewa, hatta Mariya sai daga baya taji daɗin zuwa.
Ƙarfe biyar da rabi driver yazo ɗaukar su cewa Abba ne yace ya zo. Babu musu suka shirya suka yiwa Aunty Yahanasu sallama, ta basu tsarabar turaruka suka tafi.
Suna komawa gida yaran suka zagaye Umma suna nuna mata tsarabar da bata labarin hirar su, su Mariya kam suna nuna mata ɗaki suka wuce kowacce ta canza kaya zuwa doguwar rigar shan iska na zaman gida.
Har dare basu fito ba sai bayan sallar isha'i, Ummi Aisha da Haneefa suka fita suka bar Mariya wacce sai da ta tabbatar Abba ba ya falon ta fita ta zauna, duk da ba hira zata yi ba gwara ta zauna don ɗebe kewa tana sauraron su, na murmushin tayi wanda bai mata ba ta ƙi yi.
Ƙarfe goma da rabi kowa ya nemi makwancinsa domin cikin yaran wasu har sunyi bacci a falon.
Kamar kullum ruwa ta watsa ta ɗaura alwala ta fito ta saka doguwar riga ta gabatar da sallah, bayan ta idar ta fita falo. Dining ta nufa ta zuba abinci ta zauna ta hau ci anan saɓanin wani lokaci da take ci a ɗaki.
Tana jin hayaniyar su da surutunsa amma ko a bata tanka ba, sun san ba baki zata saka ba hakan yasa babu wanda yasata a hiran su.
Bayan ta gama cin abincinta ta miƙe ta kai plate ɗin kitchen, ta ɗauki ruwa a fridge ta fita ta wuce ɗakinsu. A bakin gado ta zauna, ta buɗe ruwan hannunta tasha kusan dukka ta ajiye sauran a bedside drawer.
Miƙewa tayi ta ɗauko files din data zo dashi ta haye tsakiyar gado, buɗewa tayi ta fara bin daki-daki na jawabin Isah Hamza tare da tambayoyin da ta rubuta.
Tambayoyi kaɗan ta rubuta cikin abinda ta fahimta ta rubuta, ta ɗauki files ɗin ta ajiye a guri mai kyau.
Kan gado ta kwanta bayan ta ɗauki wayarta ta fara dannawa, a haka har dare ya shiga babu abin da yake ɗagata sai sallah. Yau bayan sallar isha'i bata kwanta ba ta miƙe ta fita falo, duk da ba magana zata yi ba gwara ta zauna cikinsu tana saurara.
Sosai suke hira a tsakaninsu, musamman Ummi Aisha da Maryam da muryarsu yafi na kowa fita, ga Abba da Baba ƙarami ma suna nasu hiran, Haneefa ce take saka baki a rigimar Ummi Aisha da Maryam, Khadeeja ma ba mai yawan surutu bace hakan yasa jifa jifa take saka musu baki. Salim na tare da Umma.
Cak falon ya ɗauki shuru bisa sallamar da aka doka, gaba ɗaya suka zubawa ƙofar ido ganin mai shigowa musamman Mariya da taji muryar mai sallamar har tsakar kanta, wanda ya haddasa mata bugun zuciya.
#vote
#comment
GOBE DA NISA
Page 4
Na Pharty BB
A facing ɗinta ya zauna, yana jifanta da murmushin nan nasa mai tsinka zuciyarta ya amsa gaisuwarta, tare da tambayarta ya aiki.
Mariya kanta kawai ta girgiza alamar lafiya ta ka sa yin magana. Gaba ɗaya a takure take da zaman, hakan yasa ta miƙe tana cewa.
"Sai da safenku."
Umma ta amsa ta bita da kallo, ta juyo ta kalli Abba da ya bita Mariya da kallo ta ce.
"Wannan shegen miskilancin yarinyar nan naka ya ishe ni, ace mutum magana yana ba shi wahala."
Abba da yabi Mariya da kallo harta shige ɗaki ya juyo ya kalli Umma jin abin da ta faɗa, fuskarsa da murmushi ya ce. "Abin gado ne."
Umma baki ta taɓe ta miƙewa.
"Sai dai a wajenka." Tana faɗa tabar wajensa ta nufi fridge ta ɗauko mishi ruwa, sauran yaranma ɗaya bayan ɗaya suka miƙe suka shige ɗaki. Shigowarsa dama yasa gaba ɗaya suka nutsu, sallamarsa ne ta katse musu surutun su.
Ummi Aisha da ta shiga ɗakinsu ta zauna kusa da Mariya da take kwance saman gado idanuwanta rufe, kallonta tayi tana faɗin.
"Kinji kin ƙara taɓa Umma. Wai don Allah bakinki ba ya tsami?"
Mariya idanuwanta ta buɗe tana kallon Ummi Aisha, tamkar ba za ta tanka ba, tayi murmushi da ya bayyana dimples ɗinta sannan tace.
"Ina yi mana, kawai dai bana saka kaina hiran da bai shafe ni ba, sai kuma wanda bai game ni ba nake ƙin tankawa."
"A wajen aikinma haka kike musu?"
Ummi Aisha ta tambayeta ganin yau ta buɗe baki ta mata magana mai tsayi.
Girgiza kai Mariya tayi ta rufe idanuwanta, tasan idan ta biyewa Ummi Aisha sai su kwana surutu.
Fitowar Haneefa a bathroom yasa Ummi Aisha miƙewa ta shige bathroom don yin wanka. Haneefa bayan ta saka kayan baccinta ta zauna kusa da Mariya, buɗe ido Mariya ta yi ta kalleta ba tace komai ba.
Haneefa ta mata murmushi ta ce.
"Me ya faru naga kamar kina da damuwa."
Girgiza kai Mariya tayi sannan tace.
"Babu komai, gajiya ce."
Jin abin da ta faɗa yasa Haneefa hawa gadon sosai, ta kwanta gefen Mariya bata kara cewa komai ba.
Ita ma Mariya kwanciyarta ta gyara tana matsawa tsakiyar gado ta barwa Ummi Aisha ƙarshe don dama koyaushe ita ce a tsakiya sai idan Haneefa bata nan.
Dalilin yawan mafarkan da take masu firgitata ta farka yasa Haneefa take sakata tsakiyarsu, don da zaran ta farka itama sai taji wani lokaci, watarana kuma bata jinta har ta yi ta koma, shi yasa idan take da night duty kullum tunaninta yar uwartan ta kwana.
Haka Ummi Aisha ta fito ta gama shirin baccinta ta kashe wuta ta haye saman gado ta kwanta. Addu'a suka yi kafin dukkansu su kwanta.
Cikin ikon Allah yau har gari ya waye Mariya ba tayi mafarki ba balle ta farka, hakan ya musu daɗi dukkansu duk da dama takan jera kwanaki uku zuwa huɗu ba tayi ba.
Bayan sun gabatar da sallah kamar kullum suka tattare ɗakin suka shirya suka fito, Umma suka gaishe suka yi breakfast kafin su fita. Ɓangaren Abba suka nufa suka gaishe dashi wanda da farko Mariya kamar kar taje, amma ganin Haneefa yasa ta binta.
Bayan ya musu fatan alheri kafin su fito suka bar gida kowacce ta kama gabanta zuwa wajen aikinta.
Mariya yau ma akan case na Isah Hamza ta wuni, har aka tashi ta musu sallama ta dawo gida.
Haka kwanakin suka tafi a rayuwar ahlin kamar baya.
Mariya ta dage da zuwa aiki da take jajircewa akai don cikar nata burin, basu kara haɗuwa da Barrister Waliy ba.
Bai nemeta ba akan aikin da ya bata, hakan yasa ta kwantar da hankalinta take bin komai daki-daki wanda har ta kusa kammala na zargin Isah Hamza da ake yana sata a unguwar su, saura ɗayan.
A haka har aka shiga weekend, mai maimakon su huta amma Ummi Aisha ta kwakulo musu tafiya gidan ƙanwar Abba yini. Mariya haushinta taji sosai don ita kam burinta ta huta a weekend ɗin nan, kuma idan ta zauna ita ɗaya za a bari domin har su khadeeja da suke yara zasu je.
Dole yasa ta shirya cikin riga da skirt na lace blue da ash, ta yi amfani da ash mayafinta, sai ƙaramin handbags ɗinta kalar takalminta. Tayi kyau sosai domin Mariya akwai kyau da tsarin halitta mai burgewa, wanda da dama shi yake fisgar jama'a.
Haka Haneefa irin lace nata ta saka sai banbancin color, na Haneefa brown da mint green maimakon color irin na Mariya, sai kamminsu ya sake fitowa.
Bayan sun gama shiryawa Abba ya bada mota driver ya kaisu har gidan Aunti Yahanasu, tayi murnan ganin yaran yayan nata sosai, suka haɗu da yaran gidan sai suka cika gidan sosai da hayaniya, kowa ya kama abokinsa suna kuskus abinsu.
Mariya, Haneefa da Ummi Aisha su ma gefe ɗaya suka haɗe da ƴan biyun Aunti Yahanasu suka kafa cafta. Hira suke sosai, da ƙyar Mariya tayi ƙoƙarin sakewa take saka baki gudun su kafa nata chapter na rashin son magana.
Hakan ko ya musu daɗi har Hassana sai da ta tanka ta ce.
"Yau za ayi ruwa da kankara."
"Ko kuma gwamna zai zo gidanku ba."
Ummi Aisha ta faɗa, fahimtar zacen sauran suka kwashe da dariya, ban da Mariya data murmusa tana cije lips ɗinta, tasan da ita suke.
Suna wannan yanayi aka yi sallama aka shigo, tuni Haneefa ta haɗa rai jin mai yin sallamar, shi ko ganinta yasa ya ƙara faɗaɗa fara'ar fuskarsa ya ƙarasa wajensu.
Zama yayi facing ɗinta yana jifanta da murmushi, ita ko ta haɗa rai tamkar ba ita ba.
Ummi Aisha ce ta fara gaishe dashi ya juya yana amsawa, haka Mariya ma ta gaishe dashi, ya amsa sannan ya juya kan Haneefa.
"Ke ba za ki gaishe dani ba."
"Ina wuni."
Ta faɗa ƙasa ƙasa tana sake haɗa rai. Sam baya burgeta saboda halayensa, duk yadda ya matsa mata da ƙoƙon barar soyayyarsa, kuma rabi da kwata Mariya ke ƙara karfafa mata guiwar ƙin sa, daɗinta ɗaya babu wanda ya sani a iyayen don tasan zasu iya amincewa tuni.
Maganarsa yasa ta kalle shi ta ɗauke kanta, gaba ɗaya gani tayi ya ƙara lalacewa ya rame. Girgiza kanta tayi ta miƙe tabar wajen gaba ɗaya don yafi mata alheri.
Nafiq ya bita da kallo sannan ya juyo kan Mariya itama ta haɗa ran da yafi na Haneefa, hakan yasa ta sake mishi kwarjini fiye da kullum.
Ka sa mata magana yayi ya miƙe yabar wajen, hakan ya basu damar cigaba da hiransu ban da Mariya da zuciyarta da ƙwaƙwalwarta suka faɗa wani tunanin daban.
Tashinsu tsaye yasa ta dawo hankalinta, ta kallesu ba ta iya tambayarsu ba. Ummi Aisha da tasan halinta ta ce.
"Da kika kasa tambayar to ɗaki zamu je."
Babu musu ita ma ta miƙe suka shiga daƙi wajen Haneefa, kwance suka sameta suka ƙarasa suka zauna gefenta. Anan suka ci gaba da hiransu har azahar, suka yi sallah kafin su haɗu su fita zuwa kitchen suka haɗa hannu suka ɗaura abincin rana.
Wajen ƙarfe biyu da rabi suka gama suka fitarwa kowa nashi, suka ƙira yaran suka karɓa sauran nasu, sauran suka jera a dining bayan sun zuba nasu suka wuce ɗaki dashi.
Ranar sunyi wunin daɗi, sun yi hira, sun ci sun sha sun kawar da kewa, hatta Mariya sai daga baya taji daɗin zuwa.
Ƙarfe biyar da rabi driver yazo ɗaukar su cewa Abba ne yace ya zo. Babu musu suka shirya suka yiwa Aunty Yahanasu sallama, ta basu tsarabar turaruka suka tafi.
Suna komawa gida yaran suka zagaye Umma suna nuna mata tsarabar da bata labarin hirar su, su Mariya kam suna nuna mata ɗaki suka wuce kowacce ta canza kaya zuwa doguwar rigar shan iska na zaman gida.
Har dare basu fito ba sai bayan sallar isha'i, Ummi Aisha da Haneefa suka fita suka bar Mariya wacce sai da ta tabbatar Abba ba ya falon ta fita ta zauna, duk da ba hira zata yi ba gwara ta zauna don ɗebe kewa tana sauraron su, na murmushin tayi wanda bai mata ba ta ƙi yi.
Ƙarfe goma da rabi kowa ya nemi makwancinsa domin cikin yaran wasu har sunyi bacci a falon.