← Book details Cinikin Rai Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 33

Sashe 28

Cinikin Rai Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Ya ce zaku koma, har da ni amma sai yayi aure domin yadda zaku ji dadin zaman gidan da mace a cikin gidan idan babu mace ai babu magana." Cikin karambani Nadrah. "Jaddah wani auren zai yi?" Take Sayyadah Qudussiyah ta d'ago inda Nadrah ta dosa, gyada mata kai tayi, ajiyar zuciya ta sauke, tana faɗin. "Akwai wani abu ne Nadrah!" Girgiza kai tayi tana faɗin. "Babu kome " ta fada tana mikewa. "Har kin koshi?" "Eh" ta wuce dakinta, ta dauka jakar makarantarta, ta fita daga gidan baki daya, domin tana bukatar shaƙar iska me sanyi don Allah kadai yadda take konewa ta cikinta, Malik yayi rejected ɗin aurenta. Ba tare da wani dalilin ba, kawai yayi dumping ɗinta, ba tare da tasan dalili ba, da farkon da Babanta yace zata auri Malik da kwana biyu su shigar da shi kotu, karshe a raba dukiyarshi a basu, tayi farinciki ko babu kome zata shiga sawun matan da suka shahara, amma once lokacin da aka gama kome suka yi magana da Malik sau biyu akan ta amince zata aure shi, sai da magana tayi ƙamari kowa ya sani, duniya ta dauki al'amarin bawan Allah nan ya kira Babanta ya gaya mishi ya fasa aurenta.
Kuma tsabar girman kai, mutumin naj bai gaya musu dalilin da yasa ya fasa auren ba,sai dai kawai ya ce ya fasa kuma har yau tunda ya ce ya fasa ko da wasa bai kuma nimanta ba, wani bin tana jin zai kira Yaranshi su yi ta waya, amma ba zai tab'a cewa a bata ba, wani abin tashin hankalin tun daga ranar Allah ya daura mata sonshi da kaunarshi.
Kai ko waya yake kamar ta gigice haka take ji, amma shi ko ta kanta baya bi. Wani abin burgewa ita ubanta yake kokarin shigar da ita, amma ita ta tsaya a ina nan bata son cusa kanta tunda dai baya yi da ita no way da zata ce sai yayi da ita, number wayarshi hotonshi da Yaranshi suna wayarta amma ko sau daya bata tab'a gwada kiranshi ba. Tana tsoron kada ta kira ya sake mata gwiwa.

Daki Jaddah ta koma, Maidah tana kallon kome, kamar bata san meke faruwa ba. Lokacin da Jaddah ta koma dakinta itama Maidah mikewa tayi ta koma dakin ta kira Lalla Salmah .
"Maamah! Dama Malik aure zai yi?" "Waye ya gaya miki.?"
"Yanzu naji Jaddah tana fadawa Nadrah da ta tambaye ta."
A nan ta shiga gayawa uwar abinda yake faruwa, sosai suka yi gulmarsu, har da zagin Nadrah Khamis Shatima, bata da kamun kai tunda gashi ta iya tambayar ashe wanda ya fasa auren har aure zai yi.
----
Jaddah kuwa kiran Malik tayi, ya kashe wayar cikin girmamawa ya kira ta.
"Babata me kike bukata?"
"Babu kome Malik, kawai ban ji dadin yadda Yarinyar nan Nadrah take ta jiran ka ba." Shiru yayi kafin ya ce mata.
"Anne! Kin san meye? Har ga Allah na so aurenta, amma kuma maganar gaskiya ba zan aure ta ba."
"Malik naga soyayyar gaskiya a tare da ita, idan bar kace ba za a bata damar haka ba, tow babu amfanin zamanta a nan, ka gayawa Mahaifinta ya turo ta koma domin ta haka ne kawai zata cire rai a tsammanin samunka."
"Zan mishi magana, in sha Allah idan kuma akwai abin da take bukata a tambaye ta sai na mata, domin ba zan barta da haushina ba."
"Duk da haka, yana da kyau ka gaya mata gaskiya ta haka zata kara ganin girmanka, ki babu soyayya kai Uba ne mata, balle kuma izuwa wannan lokacin na fahimci girman yadda take sonka. Duk da ban san me ya sauka maka ra'ayinka akanta ba, amma ina son ka sani ta hanyar rarrashi zaka iya wanke abin da ya janyo rashin aurenku, amma ka sani matukar ba wani babban dalili bane, ka juyawa auren Yarinyar nan ba, tow wallahi Allah sai ya kama ka, domin tayi matukar kokarin zaman jiranka, Malik da ace kai kake bin mutum gara shi yake binka kayi tunani sa kyau!"
"Anne, dalilina me karfi ne haka kawai ba zan ki aurenta ba, kawai zan lallabata ta fidda wani mijin tayi aure amma maganar gaskiya, bana son aurenta don Allah Anne ka da ki min dole!" Gyada kai tayi kamar tana gabanshi ta ce mishi. "Ba zan maka dole ba, kana da ikon auren abin da kake muradi, ko dan Yaran Nuratu. Sannan Jalilah mun hadu da ita!" Shiru yayi kafin ya ce mata. "Anne zan duba wasu takardun."
"Malik idan ba zaka auri Nadrah tayi maka wani abu, tow ita Jalilah fa." Kai tsaye ya ce mata. "Kawaliyan ce zan aura na kai gidana? Allah ya gani ba zan iya auren macen da ban isa da ita ba, sannan macen da ina ji ina gani sunanta zai taba Martaba ta da kimata!" "Malik kimar ce da kai?" Ta fada a fusace, dariya yayi ya ce mata. "Anne kima ne dani, da ba ni da kima wacece zata damu da tsoho me farin gashi. Kawai ana bina ne domin kudina da kimata, idan bani da su karen layi sai ya fini daraja. Anne matar da nake son aure wacce bata damu da abin hannuna ba, me tausayi da jin kai, wacce ta dandani irin rayuwar da nayi, ba wacce zata same ni daga sama ba, duk da..!"
"Malik a ina zaka samu irin macen da kaje bukata? A wacce duniya zata zo maka? Malik kayi hakuri da abin da yake hannunka, ka auri Jalilah tunda duk lalacewar masa tafi kashin shanu, Jalilah kaɗai zata iya tsaya maka."
"Anne idan na auri Jalilah, shekarunta arba'in da wani abu, yaushe zata haifa min Yara? Idan na auri Nadrah burin da yake ranta sai ta idda a kaina, idan na auri wata mace daban daga wani waje, tunaninta daban nawa daban. Anne so nake na samu macen da duniya bai dame ta ba, shiru shiru wacce bata da dogon buri" gyad'a kai take fuskartar a murtuke ta ce mishi. "Shiru-shiru ka tafi makarantar Kurame, wacce bata damu da duniya ba, ka auro Aljana kawai, Malik rayuwarka ce ka da kayi auren idan kaso, shashashan wofi" ta kashe wayar dama an saba kwana biyu ba a yi ba.
★★★
A lokacin da Zeeno take wuce babban titin, South Craig. Khamis Shatima yana tsaye a bakin bankin Savanna. Suna tattaunawa da wani mutum kawai taga motar ta, ta wuce. A gurguje yayi sallama yana me bin bayan motar. Duk da tayi mishi nisa amma sai da ya bita, ganin tana shiga wurin wanke kai yasa shi rage karfin gudunshi ya bi bayanta.
Koda ta shiga shima cikin harabar SALOON WORLD din ya shiga, yayi parking, ya jima a zaune a motar kafin ya fito a nutse ba zaka tab'a yarda cewa ya ajiye kamar Nadrah ba, akan idanun Asp Zulfa da ta biyo bayan Zeeno. Tasan haka kawai K Shatima ba zai zo wurin ba, sai dai idan Zeeno wurin ko kuma akwai matar shi a wurin.
Lokacin da Zeeno ta shiga yan mata biyu ne, suka tare ta sannan suka nuna mata wuri ta zauna, suka shiga kawo mata kayan motsa baki, kafin suka ajiye mata menu, shigowar shi yasa suka d'ago kai, kasancewar wuri ne na mata zalla, kuma babu wata babbar mace balle ace matar shi ce, duk yan mata ne a wurin musamman da yake satin biki ne, akwai bukukuwa sosai a garin.
"Yallabai meke tafe da kai!" Murmushi yayi ya zubawa Zeenobia idanu kamar maye.
"Wurinta Princess Zeenobia nazo!" Juyawa tayi tana kallon Zeeno da vata san me suke ciki ba, sai da ta bashi hanya, ya wuce ya tare da zama a gabanta. Kallon shi tayi irin kai kuma daga ina? "Nazo wurinki ne!" Ganin yadda aka zuba mata idanu. "Ko zaka bani dan tazara, irin wannan zaman yayi kusanci da yawa!"
"Duk yadda kika ce Baby!" Sake baki tayi kafin ta kuma maimaita sunan Baby. Galala ta sake baki ta ce. "Baby! "
"Yes you are my baby girl!" Kallon kanta tayi kafin ta ce mishi. "Hala Yarka da ta b'ata me kama dani ce ko?" Girgiza kai yayi ya ce mata. "Ina sonki!" Daga haka ya mike ya nufi inda ake biyan kudi, ya bada katin bankin shi aka zari kudi masu yawan gaske. Sannan ya dawo wurinta. "Ki kula min da kanki, ina bibiye da ke." Daga haka ya juya ya fita, da farkon ganinta da yayi ya so, suyi rayuwar watsewa amma yanzi da ua ganta, ya kuma hango nutsuwar da ba kowa ya dace ya hango ba, ya shirya tsaf domin ya aure ta. Duk da yaji labarinta da kuma ƙoƙarinta, baya fatan ya rasa kuma yaji labarin dabanci ne a gabanta ba karuwanci ba. Shi yasa ya dan bata lokaci kafin ya bayyana kanshi.
Chapter 28 · 0% Book details