← Book details Cinikin Rai Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 33

Sashe 26

Cinikin Rai Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kenan bai da Rauni?" Shiru yayi kafin yayi kasa kasa da murya ce mata. "Ai bai da shi, sai dai akwai wani Bad side ɗinshi Dan Luwadi ne, abin da yake aikatawa kenan yasa bai yi aure ba, har yau!"
"Me yasa ba fitar da sanarwar haka ba?" Kasa yayi da murya ya ce Mata. "Babu wanda ya isa ya fada, domin mutuwa zai yi!"
"Kana nufin babu wanda isa ya fitar da zancen kashe shi za ayi?" "Eh yar nan!" Mikewa tayi tana faɗin. "Aikin Banza da ace akan wannan labarin zan bata lokaci haka da banzo ba,." Ta saka kai ta wuce tana mita.
Karshe hudu na asuba ta isa gida, bata wani bata lokaci ba, ta wuce daki ta kwanta abinta, dakyar tayi sallah asuba. Karfe tara, ta shiga tare da nufar kamfanin Malik! Tana shiga ta wuce office din Elbashir.
Shiga tayi tana me faɗin. "Na dawo, ina son ganin Malik!" Sake baki yayi yana kallon ta.
"Ke wacce irin taurin kai ne dake? Baki ga ina waya ba ne? " "Da sauki tunda kana raye!" Tayi kanshi da wani karamin wuka ta saka mishi a wuya. "Ina son ganawa da Malik!" Kallon wayar shi tayi taga An daka MMMJ, amsa tayi tana faɗin. "Mayor Malik Menk Jordan! Kana magana da Zeenobia Nasr Hadejia, ina son ganawa da kai na baka nan da kwana uku, ga number ta 0803032....... Idan ka shirya ka kira ni, ni kuma zan iso inda kake! Ka rike sunana Zeenobia Nasr Hadejia, ko Xnoo ko Yar kunama, Zeeno. Duk wanda ya maka kai ka sani. " Katse wayar tayi ta cilla mishi. Tana me faɗin.
"Baka san halina ba ne, ba zaka min taurin kai ba." Ta juya ta fita tana waka, ban da rashin mutuncin irin na Zeenobia an gaya mata waye Malik amma tayi biris tayi abin da take da niyya.
Daga nan kai tsaye kamfahinsu ta wuce, tana shiga office din Mr Amjad taja kujera ta zauna, sannan ta daura kafaffunta a saman teburin gabanshi.
"Me ke tafe dake?" Yadda ta bude kafar tana kallon shi ta ce mishi. "Daga yanzu zuwa wani lokaci, zan gana da Malik!" "What!" Ya mike tsaye, "Tantama kake?" Girgiza kai yayi yana faɗin. "Ban yi ba, amma taya haka ya faru?" "Ikon Allah, waye ya gaya maka, wayo da dabara ce?" Nan ta kwashe kome ta gaya masa, gyada kai yake yana mamakin yadda ta daki sa'a.
"Idan kuma yaƙi gayyatarki fa?" Murmushi tayi ta ce....... Me zata ce? Rigima tana gaba,
_Free pages ya kusan karewa! Saura nawa ma? Muje zuwa...._
*Assalamu alaikum......! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A'ishah. +227 84 50 64 76 500*
[29/08, 12:47 pm] usmanlauratu71: CINIKIN RAI....17
Beauty and the beast.
Mai_Dambu🌚
<<<<<<<<<<<|=|>>>>>>>>>>>

Wani juya idanu tayi, ta ce mishi.
"Sai na saka shi yayi dan danasani, sai na tabbatar ya biya zunubi da ya fara dibarwa kanshi dole ma ya kira ni."
Ta fada tana mikewa, karkad'a key din motarta tayi tana wani irin murmushin gefen baki ta ce mishi.
"Bari mu gani, zai sauke girman kai ne ya nime ni, ko sai na fitar da abin da zai saka shi nima na da kafar shi."

Ware idanu yayi yana faɗin. "Me kike nufi? Akwai wani abu ne?" Murmusa mishi tayi tana faɗin. "Dan luwaɗi!" A firgice ya ce mata "Ke!" Ya daka mata tsawa, yana faɗin. "Kina hauka ne? Da zaki janyo mana masifa, wallahi ki rufa mana asiri!"
Dariya ta saka tana faɗin. "Cabdijan, aikin gama ya gama sai dai kuma kada a kuma !" Ta fada tare da mike zata bar Office din,
------
A can office din Elbashir kuwa, zufa me yake karyo mishi, asalima wani azazzben tsoro ne ya kama shi, muryanshi yana rawa d kira Malik. Zubewa yayi akan gwiwarshi. "Malik don Allah ka bani izini na saka a mata yankar rago." "Hmmm!" Ya faɗa ta wayar. "Malik ka bani izini na kashe ta. Ko na saka a batar da ita, Malik ka bani izini a aikata mata kome!" "Me take bukata?" Ya tambaye shi a sanyayye, wata irin kamilalliyar murya, mara amo da hayaniya. "Wai." Inji Elbashir. "Baka tabbatar da abin da take bukata ba kenan? Bashir?" Ya tambaye shi, sake zubewa yayi akan gwiwarshi. "A'a Malik so take ta gana da kai!" Ya fada kamar ya rushe da kuka. "Shekarunta nawa?" "Yarinya ce, bata wuce 19 zuwa 20 ba" kashe wayar yayi, sai a lokacin Elbashir ya sauke ajiyar zuciya. Sako ne ya shigo wayar Elbashir. *Ka jaraba hakurinta?* Da sauri ya tura mishi. _Kusan wata guda tana bibiyar kamfanin domin ta samu gani na_
Bai kuma turo mishi da sako ba, sai dai zuwa can ya turo mishi, *a kawo ta Waterfall island sau uku muga yadda zata yi idan bata samu gani na ba, kafin nan kasa a mata barazana sau uku muga yadda karfinta yake!*

_Done* ya tura mishi. Mikewa yayi yana share zufa da guntun hawayenshi da suka cika mishi idanu. "Shegiyar yarinya sai na saka an zakulo min ita" kiran wani number yayi ya ce mishi. "Maza ka zo kamfani akwai hoton wata yarinya, ku ci min Ubanta " "Yes sir!"

Bayan kamar awa biyu, wasu kartin yan maza suka tawo, "Yes gamu mun ga hotonta, sannan a bisa binciken da nayi yarinyar yar hannu ce, tasan darajar kwanji!" Cike da takaici ya ce. "Ku razana min ita!" Gyada kai yayi yana faɗin. "a gaban jama'a zamu bata tsoro! Ku muje!"

Barin kamfanin suka yi, ya turawa Malik sakon. *Na bawa su Boddi aikin firgitatta.* Yana ajiye wayar ana turo mishi sakon. _Ayi min recording din kome, idan da hali a saka musu bididdigi tracking!_ gyada kai yayi kamar yana gaban Malik.
______
Da la'asar sakaliya, ita da Yara sun fita cikin kasuwa, abaya ne a saman 3qrt din jikin. Sai riga armless kanta mayafi ta yane kanta da shi, tun da ta nufi cikin kasuwan Yara nata nuna mata abin da suke so, tana cewa. "Ku ɗauka Yarana!" Suna cikin tafiya daya daga cikin Yaran Elbashir ya bangajeta, bata wani damu ba ta ce mishi. "Sannu ko" zata wuce ya janyo ta, tare da dawo da ita gabanshi. Kallon hannunshi tayi a kafad'arta. A hankali ta juya tare da cewa.
"Kayi hakuri!" Sake dukar kafad'arta yayi, yana faɗin. "Karamar karuwa, waye Ubanki?" Fashewa da dariya Yaran suka yi, suna faɗin. "Didi koya mishi yadda ake ladbatarwa." "A'a Amir kaga Chu-chu tana jin tsoro muje na saka ku a mota!" Ta riko hannun Yaran suka juya wurin motarta, ta bude musu suka shiga, sannan ta juya tare da shiga mazauninta. Kafin su ce sun dakatar da ita ta bawa motat wani Mahaukacin wuta, a guje ta bar wurin, haka suka biyo bayanta, har zuwa Al'umma Charity House. Kafin ta isa dama ta kira Black, tana parking yana budewa Yaran kofa, suka fita da sauri. Shi kuma ya watsa mata wasu karafuna a mazaunin pasinja, da gudu ta taka motar, suka rufa mata, har zuwa filin sai da naka ko aci Ubanka.

Murmushi tayi tana kallon filin babu kowa, sannan ta sauka bayan ta dauki karafunan ta saka a hannunta. A hankali ta bude motar bayan ta cire abayar jikinta, kama gashin kanta tayi ta daure shi a baya, tare da yin gammo da shi ya zauna damar, sannan ta saka ƙafarta me dauke da canvas white and pink, kalar wandonta.

Murmushi tayi tana me kiran su, da gudun tsiya mutumin da ya bangajeta ya zo, kafin yayi wani tunani ta dake shi da hannunta me dauke da karfen, sannan ta saka kafad'arta ta kai mishi wani jahilin duka sai da ya watse a kasa, kamar yadda ake watsar da kayan wanki, yana shure -shure. Mai da kafarta baya tayi tare da yin tsayuwar dambe sosai, sai kace Kungfu girl. Ko nace jinin Mr IP. Kai zata fi dacewa da yar kabilar mandarin, Black ninja blender, wanda suka yi zamani da ibni batuta. Da mugun nufi suka nufe ta, kamar zasu yi rugu-rugu da namarta danye. Yarinyar nan, tana shiga tsakiyarsu. Ta shiga musu duka da karfen da yake yatsunta. Kafin kace kwabo, ta karkarya musu kasusuwan su, ta jibge su.

Dukar kanta Boddi yayi ta fadi can, ta kasa motsi, sake zuwa yayi ya buga mata karfen, ta hantsila ko motsin kirki bata iyawa. So take ta mike amma yadda kanta yake mata barazanar fashewa, yasa ta damke gashin kanta. Jini ne ya shiga bulbulowa daga hancinta. Kamar an bude famfo, ɗauke wuta tayi bata jin kome a duniyarta. Harbinta yayi da kafa ta cilla can gefe, baki daya bata kuma motsawa.
"Yar shegiya, har kin isa ki min wannan barnan na kyale ki." Wayar shi ya dauko ya fara danna number, ya saka a kunne. "Yallabai Elbashir mun ga..." "Kammmmmmm!" Yayi wani irin kara daga tsakiyar kwandilarshi, zubewa yayi akan gwiwarshi shi. Kafin ya zube sumamme, wayar ta dauka tare goge jinin hancinta. "Elbashir na baka nan da awa ashirin da hudu, ka hada ni zama da Malik Menk Jordan! Ko kuma garin Keivroto city ya mana kaɗan! Nasan kuna bibiyata, don Allah zan kara maimaita maka ka haɗa ni da shi ko na nuna maka salon ukubata!" Ta taka gangan jikin Boddi ta isa gaban motar shi, da aka saka camera, a wurin zaman madubin motar. Dukar gaban motar tayi. "ku karo ashirin, ku kara su zama arba'in na baku nan da awa ashirin da hudu, sai na kakkabe su a garin nan!"
Duka ta kaiwa camera din ya dauke, sannan tayi tafiyarta.
--------
Ajiyar zuciya Elbashir yayi yana faɗin, "wannan mahaifarta ya wuce misali!" Zai kira Malik ya ga sakonshi ya ce mishi. *Darkness's killer za a tura mata*
_Ok_
Kamar yadda ya fada, haka Elbashir ya basu umarnin su kai mata hari, cikin dare tunda an kundume Boddi,

Lokacin da ta dawo wanka tayi, sannan ta kwanta, kanta na mata azazzben ciwo. Bude kofar aka yi ta bude Idanunta.
"Ba zaki sha magani ba?"
"Ko daya, kaje ka kwanta ka kula." Sannan ta juya ta wankata,
Chapter 26 · 0% Book details