Sashe 8
Aure Da Haihuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abunka da titin kauye,ba motar dake wucewa,shiyasa tai tafiya me tsayi kanta sare ta nemi guri ta zauna hutawa.
Tunda ta zauna kasan wata bishiya batasan ya akayiba sejin hayaniyar motoci taji,da mutane, da sauri ta bude idonta, bacci ne ya dauketa me nauyi bata sani ba.
Mikewa tayi jiki ba kwari taja akwatin kayanta,zuwa gefen titin,
Wata mota tagani gefen titin an rubuta Daura to Kaduna, asamanta,Karen motar se kwalawa fasinja kira yake,tsallakawa tayi kawai taje tace musu Kaduna zata.
Ayko tashiga akasa kayanta a boot,mota ta cika akajasu zuwa jihar ta jamcy lahirar makwalota.Kaduna.
Jinjirinta daya farka ta sauke,tasa abunta a hijab taciro nono tana bashi kukan daya fara tuni yay shuru.
Sha biyu na safe suka iso Kawo garage dake Kaduna, babu kudi a hannunta sukenan ta biya kudin motar, Dan haka,napep kawai ta dauka tace yakaita kasuwa layin yan Dan kunnen zinari.
Me napep ko ya dauketa,har cikin centre market dake Kaduna, yanuna mata layin masu Dan kunnen,ta Ciro na kunnenta Wanda tun suna tare da Rayhan yasiya mata Wanda tuni tamance zinari ne akunnenta seda ta iso kadunan, badashi tayi aka gwada aka siya take kudinta dubu Dari da hamsin,ta biya me napep kudinsa tai masa godiya.
Ajiyar kayanta ta bada a shagon data saida Dan kunnen,ta dauki kayanta kala daya,da emtyn zani Dan goyo danta,sannan ta karasa gurin masu seda kayan sanyin Yara ta siyawa jinjirin ta,harda pampers.
Itama Audiga da pant tasiyawa kanta,tasiya karamin baho,da zata iya yiwa danta wanka,da sabulu da soso.sannan ta nufi gidan wankan da ta gani tun farkon shigowarsu kasuwar.
Koda taje cinikin ruwan zafi sukayi,aka bata,sannan aka bata bandakim da aka gama wankewa,ta shiga,yaronta ta sakko gwanin tausayi,duk yayi kashi yagama bata jikinshi,, cire masa kayan tayi sannan ta wanke masa kashin, tai masa wanka,da ike wankan yakeso ko kuka beyiba.
Tagama,a bayin ta kimtsashi,tasa masa kayan sanyisa,kyanshi,ya kara,fitowa.azani tasashi sannan ta daure zanin ajikin karfen shower din dake bayi,kamar lilo,sannan itama tai wankan ta gyara kanta,wata niima taji tana shigarta,Dan dama ji take kamar tai kuka sabida takurar da tayi.
Bayan ta kimtsa,ta kwashe kayan da suka cire tasa aleda ta Goya danta dake ta faman bacci,ta fito daga bayin.taje ta sayi abinci taci sannan ta koma ta dauko kayanta,ta dawo bakin titi tana ware ido,Dan ita batasan ina zata nufa ba,tsaye take kawai bakin titin tana karewa mutane da ababan hawa kallo.
Ganin ta rasa madafane,yasa ta yanke shawarar tsallakawa daya bangaren ta tambayi wata me abinci data hango,inda zata samu dakin haya.
Hankalinta gaba daya na kan me abincin Dan haka mancewa tayi titi zata tsallaka,shigarta tsakiyar titin yay Dede da dauketa da wata mota tayi,tai sama sannan ta fado kasa.goye da Dan jinjirin ta.wayyo Allah.
Muje zuwa
Surbajo for life.
11/14/21, 12:47 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Page 18*
Mikewa tayi ta koma dakin ta, kudi ta dauko tasa hijabi,ta nufi gun megadi,yana hango ta nufo shi yataso da sauri yadan risina yace "barka da safiya hajiya,me kike da bukata?"amsawa tayi cikin sakin fuska tace"baba don Allah cefane nakeso kayomin,a wuse market,"
"To badamuwa ranki ya Dade kawo aje ayo miki"
Lissafa masa komai tayi sannan ta bashi kudin kimanin dubu tamanin,yatafi .
Kulle gidan tayi ta ciki sannan ta koma cikin gida,wanka ta shiga sannan ta shirya ta dawo falo zaman jiran akawo mata cefanen.
Baa jima sosai ba megadi yashigo mata da sakonta bayan ta bude masa gidan,sosai tai masa godiya sannan ta kwashe komai takai dakinta.
Dan karamin gas din datasa ya siyo mata ta kunna ta daurayo tukunyar daya siyo mata tazo ta hada komai ta Dora indomie acikin dakin Nata.
Dan duk abinda zata bukata seda tasa ya siyo mata.
Haka taci gaba da gudanar da rayuwarta a kulle acikin daki,koda wasa batason ganin Rayhan, shiyasa ta kulle kanta aciki,sabida akwai toilet acikin dakin Nata,
A nashi bangaren Rayhan ko tunda ya fice yabar gidan,kotu yaje ya shigar da karar doctor Amina sakamakon abinda sukawa matarsa,inda alkali yabada sati biyu su hallara agabansa.
Lokacin da sakon ya riski doctor Amina,tashin hankalin data shiga,bashida adadi.Neman Farhan take a waya tun lokacin data ga su Rayhan din amma bata shiga,wannan shine yakara daga hankalinta.
Ranar shiga kotun da safe Rayhan yaje kofar dakin na safna yace cikin dakewar murya.
"Ki bude kofa ki fito mu tafi kotu Dan yau alkali yabada mu hallara agabanshi ina jiranki a mota"yana kaiwa nan yayi fucewarsa abunsa
Safna jin maganar tayi kamar saukar Aradu,yau itace Rayhan yakai kara kotu?wannan wacce irin masiface.
Tunda ya fada tasan dagaske yakeyi,Dan karya bata daya daga cikin halayensa.
Jiki asanyaye ta janyo hijab tasaka,ta zura takalmi ta fito.bayan ta kulle dakinta.
A motar ta sameshi yana cika yana batsewa,ba me cewa shine Rayhan din ta me yawan murmushi.
A harabar kotun suka samu doctor Amina ma ta iso ita da maaikatan da suka gudanar da aykin.
Karasawa gunta Safna tayi suka gaisa,inda doctor Amina tace"Safna kinga kaddara ko?"
Hawaye ne suka gangaro daga idon Safna masu zafi sannan tace"doctor ina cikin tashin hankali"
Karasowar Rayhan gurin ne ya katse musu hirar,inda ya dakawa Safna tsawa da cewa "wuce mutafi".ba musu tabishi abaya suka shiga cikin kotun.
Bayan kowa ya hallara ne me gabatar da kara yatashi ya gabatar da karar da Rayhan Hashim ya shigar agabanta,yana me kalubalantar doctor Amina,da sauya kwayoyin halittarsa Dana wani ta sawa matarsa,Wanda hakan ya janyo matarsa ta dauki ciki,yana me rokon kotu datasa matarsa ta zubar da cikin,kuma yanaso kotu me adalci da ta bi masa hakkinsa.
Bayan an gabatar da kara ne alkali ya bukaci ganin doctor Amina,jiki asanyaye ta karasa inda aka tanada domun tsayuwar Wanda ake tuhuma taje ta tsaya.
"Munaso ki gabatar mana da kanki"cewar alkali,
"Sunana Amina Galadima,likita,kuma mamallakiyar Asibitin Galadima special hospital"
"Kinji korafin da aka shigar akanki shin haka akayi koko kina da ja game da hakan?"alkali yasake jefo mata tambayar.
"Duk abinda aka fadi ranka ya Dade haka ne,sede ba nice da kaina na gudanar da aykinba, kuma kuskuren suna aka samu ta hanyar kamanceceniyar suna,ina me rokon kotu datai mana sassauci".ta kwashe komai ta sanar da kotu gamida mika takaddu na bincike da kuma duk wani Abu daya shafi dashen tun kan ayi har zuwa bayan anyi,
Alkali ya bukaci maaikatan da suka gudanar da aykin dasu gabato gabansa,suma suka amsa sune suka yi,
Bayan dogon rubutu alkali yafara magana,"Bayan nazari da bincike,wainda ake tuhuma basu wahalar da sharia ba kotu ta gamsu da duk bayanan kowanne bangare,kuskurene babba suka aykata,Wanda dole ay musu hukunci,Na farko,kotu ta yankewa doctor Amina hukuncin biyan Tara ta dubu Dari,bisa laifin daukar maaikatan da suke sakaci da aykinsu,su kuma wainda suka aykata laifin,kotu na umartar da akaisu gidan gyaran hali na tsawon wata guda,ko zabin Tara,ta dubu goma goma"kotunce ta hargitse da surutu,kamin alkali ya tsawatar akai shuru, sannan yaci gaba
"Kotu na kira ga Rayhan da yayi hakuri bisa faruwar wannan Lamari,sabida kotu bazata sa Safna ta zubar da cikiba, Wanda aykata hakan zunubine,kuma shi wannan Abu daya faru,shima kuskuren ne babba, duba da tabbaci da aka samu daga bakunan maaikatan na cewa cikin an sameshi bada kwayoyin halittarka ba,kuma kamin ayi an tabbatar da bata da ciki,bayan anyi kuma baka kusanceta ba seda aka tabbatar da ta samu cikin,hakan ya tabbatar da cewa cikin jikinta ba naka bane,Dan haka kotu ta sallami wannan karar"
Gaba daya kotun ta kaure da hayaniya,Safna kuka take kamar ranta ze fita, wannan kaddara dame tai kama.
Haka ta mike tabi bayan Rayhan din daya fita afusace,
Sede kamin ta karaso tuni yaja motar sa yabar harabar gurin,Dan shi Sam ba haka yaso ba,so yayi asa safna ta zubar da cikin, sannan adaure doctor Amina, amma gaba daya ba hakan akayiba,
Hakanne yasa shi tunanin anya ma kuwa alkalin yasan aykinshi?
Muje zuwa
Surbajo for life.
11/14/21, 12:47 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Inna Ibrahim kime alkhairin Allah yakai miki, ina alfahari da haduwa dake arayuwata.*
*19*
Doctor Amina ce ta karaso inda take ta dafata, da sauri ta waiga taga waye,
Ganinta ne yasa ta rushe da kuka ta fada jikinta tana fadin,"doctor ki taimakeni banason rasa aurena,Ina son mijina sosai"tayi shuru sakamakon kukan dayaci karfinta.
Jan ta zuwa mota doctor tayi sabida jamaa sun fara taruwa akansu,da gudu ta fice daga harabar kotun.
Safna ko se aykin kuka take,har suka iso kofar gidan Rayhan din,bude mata kofa tayi ta fito,sannan tace"gobe zan dawo in mijinki ya fita Dan musan yadda zaa bullowa da abun ki kwantar da hankalin ki"
Jiki ba kwari ta tura kofar get din tashiga ita kuma doctor taja motarta ta bar gurin.
A harabar gidan tasameshi tsaye yana huci,kamar wani maciji,bata bi takanshi ba tayi hanyar shiga ciki,wata tsawa ya daka mata sai da cikinta yayi juyi ta waigo a firgice,.
Tsayawa tayi cak a inda take,har ya karaso,cikin fushi yake magana "Safna koda wasa ban dauka zaki ketare maganata ba,nadauka son da kikemin na gaskene,shiyasa na baki umarnin zubar da ciki amma kika ki,to ni bazan iya zama dake ina kwasar bakin ciki ba,Dan haka zan baki zabi wallahi sede ki zaba ni ko cikin jikin ki?"ya wurga mata tambayar batare da shayin komai ba,
Cikin kuka Safna ta tsuguna agabanshi tafara bashi hakuri"don Allah Rayhan kayi hakuri, kasan ina sonka, wlh nafi sonka akan cikin jikina,fushin Allah ne kawai banason na fada,sakamakon zubar da cikin,don Allah ka fahimceni"ta karasa maganar cikin kuka.
"Zabi na baki malama ni ko cikin jikin ki?"yafadi batare daya tausaya mata ba.
Rokonshi take da duk iyawarta kan yayi hakuri amma fafur ya kafe,ganin bata da mafitane yasa ta mike tsaye ta share hawayen ta tace asanyaye "na zabi cikin jikina Rayhan"
Kallon mamaki yay mata sannan yace "to kije na sauwake miki aurena dake kanki,na sakeki saki daya"ya yi saurin barin gurin sakamakon kukan dakeson kubce masa,yana son matarsa,yayi iya yinsa Dan yaso abinda ke cikinta amma yakasa,shiyasa ya sake ta gudun kar zuciya takai shi halaka.
Tunda ta zauna kasan wata bishiya batasan ya akayiba sejin hayaniyar motoci taji,da mutane, da sauri ta bude idonta, bacci ne ya dauketa me nauyi bata sani ba.
Mikewa tayi jiki ba kwari taja akwatin kayanta,zuwa gefen titin,
Wata mota tagani gefen titin an rubuta Daura to Kaduna, asamanta,Karen motar se kwalawa fasinja kira yake,tsallakawa tayi kawai taje tace musu Kaduna zata.
Ayko tashiga akasa kayanta a boot,mota ta cika akajasu zuwa jihar ta jamcy lahirar makwalota.Kaduna.
Jinjirinta daya farka ta sauke,tasa abunta a hijab taciro nono tana bashi kukan daya fara tuni yay shuru.
Sha biyu na safe suka iso Kawo garage dake Kaduna, babu kudi a hannunta sukenan ta biya kudin motar, Dan haka,napep kawai ta dauka tace yakaita kasuwa layin yan Dan kunnen zinari.
Me napep ko ya dauketa,har cikin centre market dake Kaduna, yanuna mata layin masu Dan kunnen,ta Ciro na kunnenta Wanda tun suna tare da Rayhan yasiya mata Wanda tuni tamance zinari ne akunnenta seda ta iso kadunan, badashi tayi aka gwada aka siya take kudinta dubu Dari da hamsin,ta biya me napep kudinsa tai masa godiya.
Ajiyar kayanta ta bada a shagon data saida Dan kunnen,ta dauki kayanta kala daya,da emtyn zani Dan goyo danta,sannan ta karasa gurin masu seda kayan sanyin Yara ta siyawa jinjirin ta,harda pampers.
Itama Audiga da pant tasiyawa kanta,tasiya karamin baho,da zata iya yiwa danta wanka,da sabulu da soso.sannan ta nufi gidan wankan da ta gani tun farkon shigowarsu kasuwar.
Koda taje cinikin ruwan zafi sukayi,aka bata,sannan aka bata bandakim da aka gama wankewa,ta shiga,yaronta ta sakko gwanin tausayi,duk yayi kashi yagama bata jikinshi,, cire masa kayan tayi sannan ta wanke masa kashin, tai masa wanka,da ike wankan yakeso ko kuka beyiba.
Tagama,a bayin ta kimtsashi,tasa masa kayan sanyisa,kyanshi,ya kara,fitowa.azani tasashi sannan ta daure zanin ajikin karfen shower din dake bayi,kamar lilo,sannan itama tai wankan ta gyara kanta,wata niima taji tana shigarta,Dan dama ji take kamar tai kuka sabida takurar da tayi.
Bayan ta kimtsa,ta kwashe kayan da suka cire tasa aleda ta Goya danta dake ta faman bacci,ta fito daga bayin.taje ta sayi abinci taci sannan ta koma ta dauko kayanta,ta dawo bakin titi tana ware ido,Dan ita batasan ina zata nufa ba,tsaye take kawai bakin titin tana karewa mutane da ababan hawa kallo.
Ganin ta rasa madafane,yasa ta yanke shawarar tsallakawa daya bangaren ta tambayi wata me abinci data hango,inda zata samu dakin haya.
Hankalinta gaba daya na kan me abincin Dan haka mancewa tayi titi zata tsallaka,shigarta tsakiyar titin yay Dede da dauketa da wata mota tayi,tai sama sannan ta fado kasa.goye da Dan jinjirin ta.wayyo Allah.
Muje zuwa
Surbajo for life.
11/14/21, 12:47 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Page 18*
Mikewa tayi ta koma dakin ta, kudi ta dauko tasa hijabi,ta nufi gun megadi,yana hango ta nufo shi yataso da sauri yadan risina yace "barka da safiya hajiya,me kike da bukata?"amsawa tayi cikin sakin fuska tace"baba don Allah cefane nakeso kayomin,a wuse market,"
"To badamuwa ranki ya Dade kawo aje ayo miki"
Lissafa masa komai tayi sannan ta bashi kudin kimanin dubu tamanin,yatafi .
Kulle gidan tayi ta ciki sannan ta koma cikin gida,wanka ta shiga sannan ta shirya ta dawo falo zaman jiran akawo mata cefanen.
Baa jima sosai ba megadi yashigo mata da sakonta bayan ta bude masa gidan,sosai tai masa godiya sannan ta kwashe komai takai dakinta.
Dan karamin gas din datasa ya siyo mata ta kunna ta daurayo tukunyar daya siyo mata tazo ta hada komai ta Dora indomie acikin dakin Nata.
Dan duk abinda zata bukata seda tasa ya siyo mata.
Haka taci gaba da gudanar da rayuwarta a kulle acikin daki,koda wasa batason ganin Rayhan, shiyasa ta kulle kanta aciki,sabida akwai toilet acikin dakin Nata,
A nashi bangaren Rayhan ko tunda ya fice yabar gidan,kotu yaje ya shigar da karar doctor Amina sakamakon abinda sukawa matarsa,inda alkali yabada sati biyu su hallara agabansa.
Lokacin da sakon ya riski doctor Amina,tashin hankalin data shiga,bashida adadi.Neman Farhan take a waya tun lokacin data ga su Rayhan din amma bata shiga,wannan shine yakara daga hankalinta.
Ranar shiga kotun da safe Rayhan yaje kofar dakin na safna yace cikin dakewar murya.
"Ki bude kofa ki fito mu tafi kotu Dan yau alkali yabada mu hallara agabanshi ina jiranki a mota"yana kaiwa nan yayi fucewarsa abunsa
Safna jin maganar tayi kamar saukar Aradu,yau itace Rayhan yakai kara kotu?wannan wacce irin masiface.
Tunda ya fada tasan dagaske yakeyi,Dan karya bata daya daga cikin halayensa.
Jiki asanyaye ta janyo hijab tasaka,ta zura takalmi ta fito.bayan ta kulle dakinta.
A motar ta sameshi yana cika yana batsewa,ba me cewa shine Rayhan din ta me yawan murmushi.
A harabar kotun suka samu doctor Amina ma ta iso ita da maaikatan da suka gudanar da aykin.
Karasawa gunta Safna tayi suka gaisa,inda doctor Amina tace"Safna kinga kaddara ko?"
Hawaye ne suka gangaro daga idon Safna masu zafi sannan tace"doctor ina cikin tashin hankali"
Karasowar Rayhan gurin ne ya katse musu hirar,inda ya dakawa Safna tsawa da cewa "wuce mutafi".ba musu tabishi abaya suka shiga cikin kotun.
Bayan kowa ya hallara ne me gabatar da kara yatashi ya gabatar da karar da Rayhan Hashim ya shigar agabanta,yana me kalubalantar doctor Amina,da sauya kwayoyin halittarsa Dana wani ta sawa matarsa,Wanda hakan ya janyo matarsa ta dauki ciki,yana me rokon kotu datasa matarsa ta zubar da cikin,kuma yanaso kotu me adalci da ta bi masa hakkinsa.
Bayan an gabatar da kara ne alkali ya bukaci ganin doctor Amina,jiki asanyaye ta karasa inda aka tanada domun tsayuwar Wanda ake tuhuma taje ta tsaya.
"Munaso ki gabatar mana da kanki"cewar alkali,
"Sunana Amina Galadima,likita,kuma mamallakiyar Asibitin Galadima special hospital"
"Kinji korafin da aka shigar akanki shin haka akayi koko kina da ja game da hakan?"alkali yasake jefo mata tambayar.
"Duk abinda aka fadi ranka ya Dade haka ne,sede ba nice da kaina na gudanar da aykinba, kuma kuskuren suna aka samu ta hanyar kamanceceniyar suna,ina me rokon kotu datai mana sassauci".ta kwashe komai ta sanar da kotu gamida mika takaddu na bincike da kuma duk wani Abu daya shafi dashen tun kan ayi har zuwa bayan anyi,
Alkali ya bukaci maaikatan da suka gudanar da aykin dasu gabato gabansa,suma suka amsa sune suka yi,
Bayan dogon rubutu alkali yafara magana,"Bayan nazari da bincike,wainda ake tuhuma basu wahalar da sharia ba kotu ta gamsu da duk bayanan kowanne bangare,kuskurene babba suka aykata,Wanda dole ay musu hukunci,Na farko,kotu ta yankewa doctor Amina hukuncin biyan Tara ta dubu Dari,bisa laifin daukar maaikatan da suke sakaci da aykinsu,su kuma wainda suka aykata laifin,kotu na umartar da akaisu gidan gyaran hali na tsawon wata guda,ko zabin Tara,ta dubu goma goma"kotunce ta hargitse da surutu,kamin alkali ya tsawatar akai shuru, sannan yaci gaba
"Kotu na kira ga Rayhan da yayi hakuri bisa faruwar wannan Lamari,sabida kotu bazata sa Safna ta zubar da cikiba, Wanda aykata hakan zunubine,kuma shi wannan Abu daya faru,shima kuskuren ne babba, duba da tabbaci da aka samu daga bakunan maaikatan na cewa cikin an sameshi bada kwayoyin halittarka ba,kuma kamin ayi an tabbatar da bata da ciki,bayan anyi kuma baka kusanceta ba seda aka tabbatar da ta samu cikin,hakan ya tabbatar da cewa cikin jikinta ba naka bane,Dan haka kotu ta sallami wannan karar"
Gaba daya kotun ta kaure da hayaniya,Safna kuka take kamar ranta ze fita, wannan kaddara dame tai kama.
Haka ta mike tabi bayan Rayhan din daya fita afusace,
Sede kamin ta karaso tuni yaja motar sa yabar harabar gurin,Dan shi Sam ba haka yaso ba,so yayi asa safna ta zubar da cikin, sannan adaure doctor Amina, amma gaba daya ba hakan akayiba,
Hakanne yasa shi tunanin anya ma kuwa alkalin yasan aykinshi?
Muje zuwa
Surbajo for life.
11/14/21, 12:47 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Inna Ibrahim kime alkhairin Allah yakai miki, ina alfahari da haduwa dake arayuwata.*
*19*
Doctor Amina ce ta karaso inda take ta dafata, da sauri ta waiga taga waye,
Ganinta ne yasa ta rushe da kuka ta fada jikinta tana fadin,"doctor ki taimakeni banason rasa aurena,Ina son mijina sosai"tayi shuru sakamakon kukan dayaci karfinta.
Jan ta zuwa mota doctor tayi sabida jamaa sun fara taruwa akansu,da gudu ta fice daga harabar kotun.
Safna ko se aykin kuka take,har suka iso kofar gidan Rayhan din,bude mata kofa tayi ta fito,sannan tace"gobe zan dawo in mijinki ya fita Dan musan yadda zaa bullowa da abun ki kwantar da hankalin ki"
Jiki ba kwari ta tura kofar get din tashiga ita kuma doctor taja motarta ta bar gurin.
A harabar gidan tasameshi tsaye yana huci,kamar wani maciji,bata bi takanshi ba tayi hanyar shiga ciki,wata tsawa ya daka mata sai da cikinta yayi juyi ta waigo a firgice,.
Tsayawa tayi cak a inda take,har ya karaso,cikin fushi yake magana "Safna koda wasa ban dauka zaki ketare maganata ba,nadauka son da kikemin na gaskene,shiyasa na baki umarnin zubar da ciki amma kika ki,to ni bazan iya zama dake ina kwasar bakin ciki ba,Dan haka zan baki zabi wallahi sede ki zaba ni ko cikin jikin ki?"ya wurga mata tambayar batare da shayin komai ba,
Cikin kuka Safna ta tsuguna agabanshi tafara bashi hakuri"don Allah Rayhan kayi hakuri, kasan ina sonka, wlh nafi sonka akan cikin jikina,fushin Allah ne kawai banason na fada,sakamakon zubar da cikin,don Allah ka fahimceni"ta karasa maganar cikin kuka.
"Zabi na baki malama ni ko cikin jikin ki?"yafadi batare daya tausaya mata ba.
Rokonshi take da duk iyawarta kan yayi hakuri amma fafur ya kafe,ganin bata da mafitane yasa ta mike tsaye ta share hawayen ta tace asanyaye "na zabi cikin jikina Rayhan"
Kallon mamaki yay mata sannan yace "to kije na sauwake miki aurena dake kanki,na sakeki saki daya"ya yi saurin barin gurin sakamakon kukan dakeson kubce masa,yana son matarsa,yayi iya yinsa Dan yaso abinda ke cikinta amma yakasa,shiyasa ya sake ta gudun kar zuciya takai shi halaka.