Sashe 2
Aure Da Haihuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Safna Habu Sara shine sunanta,d'iyace ga malam habu,dake zaune a k'auyen Sara dake Zangon Daura ta Jihar Katsina,
Malam habu shine limamin garin sabida yana da tarin ilimin addini Dede gwargwado yasa dagacin garin nad'ashi limamin garin
Matanshi uku,inna hansai itace uwargida,se inna fure,se Amaryarsu jamila amma suna kiranta da Sabuwa.
Tunda malam habu ya auro jamila take fuskantar matsi da takura agurin sauran abokan zamanta,sun had'e mata kai sun wareta Wanda hakan ko kad'an be mata dad'i biyayya Dede gwargwado tana musu amma su Sam basa gani,acewa da ganin su duk na munafunci ne.
Inna hansai Nada Yara biyu,jummai,da Ladidi,se inna fure itama guda biyu gareta,akwai Abu se Zabba'u,inna sabuwa ce me guda d'aya wacce malam ya sawa sunan mahaifiyarshi Safina,
Yaran malam habu biyar duka mata Allah be bashi haihuwar d'a namiji ba,shi yasa ya duk'ufa wajen ganin ya basu tarbiya da ilimi ta yadda za ay alfahari da su.
Duk wani cin kashi na gidan akan jamila da 'yarta ake yinsa,an maidasu tamkar bayi,da ike jamila irin mutanen nan ne masu hak'uri ko kad'an bata cewa komai akan abinda ake musu ita da 'yarta.
Tun tasowar 'yanmatan na malam habu Allah yay musu farin jini, kasancewar dukan su da mahaifinsu suke kama,kyau kamar su sukai Kansu,kasancewarshi bafulatani,Safna ce ta kerewa kowa kyau acikinsu kasancewar ita ba iya kamannin malam d'in ta d'ebo ba harda na mahaifiyarta.Wanda hakan yasa ta fice zakka acikinsu.
Duk da tafisu kyau,wani ikon Allah ko kad'an ita bata da farin jinin samarin, kamar wata me bak'in jini,hakan ya sanya su inna fure yiwa sabuwa gorin 'yarta ba mashinshini.
Ita sabuwa abin be damunta Dan tasan aure lokacine,in yazo za ayi.
Wasa wasa har an kawo kud'in sauran 'ya'yan gidan amma Safna har yanzu ba me cewa yana sonta.
Suna Aji biyar a secondary school aka sha bikin sauran 'yan uwanta,inda kowacce ta tare a gidanta,aka bar Safna ita kad'ai a gida.
Zuwa lokacin lamarin yafara tab'a zuciyar sabuwa,amma ta duk'ufa da addu'a.
To bayan aurar da 'yanmatan gidan ne wahalhalu suka k'aru akan Safna, ita ce d'ebo ruwa,ba dabbobi abinci,shara wanke_wanke,girki,yo itace ,acewar matan gidan in bata yiba Wa ze mata.
Duk ta fice hayyacinta kullum mahaifiyarta kwarin guiwa take bata da cewa watarana se labari.
Muje zuwa
Surbajo for life.
11/14/21, 12:43 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*page 4*
Yau tun asuba ta mik'e tayi duk aykace aykacenta,sabida yau ake taron sunan 'yar gidan inna hansai jummai ta haihu.
Ko da ta gama shiryawa,tuni su sabuwa da inna fure da sauran makwabtansu sun tafi gidan sunan,da ike a zango tai auren, Dan haka fitowa tayi cikin kwalliyarta ta nufi gidan su k'awarta Maimuna,dama tare zasu tafi gidan sunan.
Tana zuwa ta samu Maimunan ta shirya ita kawai take jira,Dan haka rankayawa sukai suka nufi titi Dan samun abun hawa da ze kaisu garin na zango.
Tsaye suke a bakin titin amma babu abun hawa,cikin damuwa Maimuna tace"yau fa alamu sun gwada 'yarfillo a k'afa zamuje zangon nan,kuma wallahi ga rana"
Murmushi Safna tayi daya k'ara fito da kyawun fuskarta,tace cikin siririyar muryarta,"da alama kuwa,kawai mu fara takawa,tunda ba wani nisa bane sosai,watak'ila a gaba mu samu"bata k'arasa maganar ba taji k'arar taka burki a gabansu,a tsorace dukan su suka dubi kan titin,wata shirgegiyar mota suka gani tana k'ok'arin gyara parking a gaban su,
Tana gama tsayawa na cikin motar ya fito,matashine kyakkyawa ajin farko,Wanda Hutu da ilimi suka samu masauki a jikinshi,sanye ike cikin farar shadda,tasha d'inkin zamani,kanshi ba hula se sumar daya Tara data dace da tsarin kwalliyar tashi.
Cikin takun burgewa ya k'araso gabansu fuskarshi d'auke da murmushi,yace"Amincin Allah ya tabbata a gareku,Ku gafarce ni firgitaku da nayi"ya k'arasa maganar yana had'e hannayensa guri guda.
Safna sarkin kunya,sunkuyar da kai tayi tana murmushi,yayin da maimuna tace"amin,mungode ba komai"
"In bazaki damuba Dan Allah kitaimaka min da sunan k'awar taki Dan naga kamar rowar magana gareta "yayi tambayar yana kallon fuskar Safna wacce har yanzu murmushi kawai take yi ba tace komai ba.
Murmushi maimuna tayi sannan tace "Safna sunanta dafatan ba zuwa sace ta kayi ba?"
Murmushi yayi yace"ita ta fara satoni,so shine nima nake so da taimakon ki ki tallafamin in saceta zuwa gidana na aure"
Da sauri Safna ta b'oye a bayan Maimuna,alamun taji kunya sosai,har zuwa lokacin murmushi be bar fuskarta ba.
"Se mun bincika tukuna in nagartarka ta kai a baka se ayi hakan sabida komai nufin Allah ne"
"Sunana Rayhan Hashim Daura,mahaifina Dan daura ne amma muna zaune a Abuja sabida yanayin Ayki,nazo bikin abokina ne nan yardaje,se kuma Allah ya had'ani da tawa amaryar a hanya"
Haka yay ta jansu da hira amma Safna ta gaza furta komai,har suka samu abun hawa,fafur suka k'i yarda su hau motarshi,gashi dukan su bame waya,Rayhan ganin zata kubce masa ne yasa ya d'auko wayarshi dank'areriya a gaban motarshi ya mik'awa Safna, yace "ba Dan na isa ba Dan Alfarmar Annabi ki amshi wayarnan,in muka rabu yanzu ban san ina zan sake ganinki ba,sabida yau zamu wuce gida,amma inda wayar a hannunki zan kira kimin kwatance"
Jiki a sanyaye Safna tasa hannu ta amshi wayar,se alokacin tace a tsorace murya na rawa,"zan zan...ajiyema in...muka had'u zaka amshi abunka"wani sanyine ya ratsa zuciyar Rayhan sakamakon jin muryarta da yayi.
"Na amince beauty semun had'un,"
Daga haka sukai sallama suka shiga mota shima ya shiga tashi,da ike hanya dayace haka yay ta bin su a baya har aka sauke su a zangon sannan yay musu hon yayi gaba.
Jikin Safna a sanyaye suka isa gidan sunan daya cika da jama'a.
Ko a gidan sunan seda aka mata habaicin ba mashinshini,ayko carab maimuna ta amshe zancen da cewa,"mashinshini de kam Safna Allah ya nufa ya shinshino ta,kuma insha Allahu se ya tsone idon mak'iyanta"
Ayko gaba d'aya gurin aka sa shewar zancen Nata.
Basu baro gidan sunan ba se isha'i sabida seda suka gyarawa mejego gida tukuna suka tafi.
A gajiye Safna take,Dan haka tana zuwa gida wanka tayi ta kintsa sannan ta Ciro wayar ta samu innarta tai mata bayanin komai game da had'uwarta da Rayhan yau.
Farincikine ya mamaye zuciyar innar ta,gami da yiwa Allah godiya daya fara haska tauraruwar 'yarta a idon manema sabida itama ta samu tai aure ta huta.
Nasiha da Jan kunne tai mata kan tade kama kanta da mutuncinta banda giggiwa,daga k'arshe tai fatan alkha'iri.
Muje zuwa
Surbajo for life
11/14/21, 12:43 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Page 5*
Safna shirin bacci tayi,tayi addu'a ta tofa tana kwanciya taji wani sauti me dad'i na tashi ak'asan fulonta,da har ta firgita can kuma ta tuna da wayar da Rayhan ya bata,Dan haka a tsanake ta d'auko wayar,bata wahalar gane kanta ba,sabida tana karatu,a hankali ta d'aga wayar ta kara a kunnenta,wata sassanyar ajiyar zuciya Rayhan ya saki wacce ta haddasawa Safna wani bak'on lamari ajikinta,sosai jikinta ya mutu,a hankali ta jiyo muryarshi yace a kasalance "beauty"sosai sunan da muryar da yay amfani da ita gurin kiran sunan Nata sukai mata dad'i,
ahankali cikin siririyar muryarta tace "ranka ya dad'e"
Rayhan kusan mirginowa yayi daga kan gadonshi Dan dad'in sunan da ta kira shi da shi,k'ara k'asa yay da murya sannan yace
"Kinyi kewa ta kuwa?"
Murmushi tayi me sauti sannan tace"gaskiya zan fad'ima ko k'arya?"
Yace "gaskiya"tace "to gaskiya d'aya banyi ba"
Shuru ya danyi sannan yace,"Ina sonki Safna shin kema kina sona kuwa?wallahi in har za'a bani ke safna nan da sati biyu na shirya auren ki,ba yaudarar ki nazo yi ba"
A hankali safna tace "Komai nufine na Allah, ganin farko zuciyata ta yarda da kai,ina fatan Allah ya baka ikon rik'eni amana,yasa akwai alkha'iri a tsakaninmu"
Cike da zumud'i yace "Amin beauty na"
Daga haka hira su kai ta abinda ya shafi karatu da nasaba,har zuwa sha d'ayan dare sannan su kai sallama yakashe.
Wasa wasa soyayya ce suke yinta me tsabta tsakanin Safna da Rayhan, sosai take jin son sa a zuciyarta,shima haka.
Tuni Inna Sabuwa ta sanar da Malam Habu komai sabida Safna bata b'oye mata komai tsakaninsu.
Yau Rayhan na hanyar zuwa gun masoyiyar tashi,shi murna ita murna,tun safe taje gidansu maimuna suka shiga girka abincin da zasu tarbe shi,Wanda Inna Sabuwace ta amso dubu uku gun malam ta bata,ayko wainar shinkafa sukai masa da miyar kaji Wanda malam yasa aka yanka zakaru manya guda biyu na tarbar sirikin nasa
Zob'o suka had'a suka siyo k'ank'ara suka sa,yayi sanyi gashi se k'amshin kayan k'amshi yake,fura da nono me kyau ta dama masa tasa k'ank'ara,sannan ta gurza kwakwa ta zuba aciki.
Acikin kulolin tarin auren maimuna aka jera komai,wanka tayi agidan su maimunan sannan tasa doguwar rigarta ta shadda me ruwan hanta,wacce k'anwar innarta ta d'inko mata a daura d'inki ya dace da jikinta, bata d'aura d'ankwalin ba,illa kama gashinta me yawan gaske da tayi da ribbon sannan ta fesa turare,bame kallonta yace awannan kauyen take,sosai kyanta ya fito,bin jikinta da doguwar rigar tayi shi ya bayyana asirin kyawun dirinta,domin duk inda akeson mace safna takai.
Tana tsaka da fesa turaren ne wayarta tai k'ara a hankali tasa hannu ta d'aga Dan tasan me kiran,cikin siririyar muryarta tace"ranka ya Dad'e ya hanyar?"
"Hanya Alhamdulillahi beauty gani na iso inda muka had'u daku ranar farko "
"Barka da zuwa bari in turo a k'araso da ku,"sabida yashaida mata tare da abokinsa suka zo.
Cikin shagwab'a yace"beauty ke nake son fara gani please babu D'an ayke a tsakaninmu kizo da kanki"
Murmushi tayi sannan tace "to ganinan zuwa"daga haka suka kashe wayar.
Dubanta ta kai gun maimuna tace" taso muje mu iso dasu mutumim naki kwai rigima wai sede inzo da kaina in mai iso"
Dariya maimuna tayi sannan tace "wallahi k'awata Ina tayaki murnar samun Rayhan amatsayin masoyi Allah yasa har aure,nima kuma Allah ya bani nawa masoyin muyi aure mu huta da gorin garinnan"
Murmushi Safna tayi tace"amin k'awata"
Mayafi maimuna ta yafa bayan ta dan murza hoda,da ike itama farace kyakkyawa,Tass ta fito,bakin titin suka nufa.
Malam habu shine limamin garin sabida yana da tarin ilimin addini Dede gwargwado yasa dagacin garin nad'ashi limamin garin
Matanshi uku,inna hansai itace uwargida,se inna fure,se Amaryarsu jamila amma suna kiranta da Sabuwa.
Tunda malam habu ya auro jamila take fuskantar matsi da takura agurin sauran abokan zamanta,sun had'e mata kai sun wareta Wanda hakan ko kad'an be mata dad'i biyayya Dede gwargwado tana musu amma su Sam basa gani,acewa da ganin su duk na munafunci ne.
Inna hansai Nada Yara biyu,jummai,da Ladidi,se inna fure itama guda biyu gareta,akwai Abu se Zabba'u,inna sabuwa ce me guda d'aya wacce malam ya sawa sunan mahaifiyarshi Safina,
Yaran malam habu biyar duka mata Allah be bashi haihuwar d'a namiji ba,shi yasa ya duk'ufa wajen ganin ya basu tarbiya da ilimi ta yadda za ay alfahari da su.
Duk wani cin kashi na gidan akan jamila da 'yarta ake yinsa,an maidasu tamkar bayi,da ike jamila irin mutanen nan ne masu hak'uri ko kad'an bata cewa komai akan abinda ake musu ita da 'yarta.
Tun tasowar 'yanmatan na malam habu Allah yay musu farin jini, kasancewar dukan su da mahaifinsu suke kama,kyau kamar su sukai Kansu,kasancewarshi bafulatani,Safna ce ta kerewa kowa kyau acikinsu kasancewar ita ba iya kamannin malam d'in ta d'ebo ba harda na mahaifiyarta.Wanda hakan yasa ta fice zakka acikinsu.
Duk da tafisu kyau,wani ikon Allah ko kad'an ita bata da farin jinin samarin, kamar wata me bak'in jini,hakan ya sanya su inna fure yiwa sabuwa gorin 'yarta ba mashinshini.
Ita sabuwa abin be damunta Dan tasan aure lokacine,in yazo za ayi.
Wasa wasa har an kawo kud'in sauran 'ya'yan gidan amma Safna har yanzu ba me cewa yana sonta.
Suna Aji biyar a secondary school aka sha bikin sauran 'yan uwanta,inda kowacce ta tare a gidanta,aka bar Safna ita kad'ai a gida.
Zuwa lokacin lamarin yafara tab'a zuciyar sabuwa,amma ta duk'ufa da addu'a.
To bayan aurar da 'yanmatan gidan ne wahalhalu suka k'aru akan Safna, ita ce d'ebo ruwa,ba dabbobi abinci,shara wanke_wanke,girki,yo itace ,acewar matan gidan in bata yiba Wa ze mata.
Duk ta fice hayyacinta kullum mahaifiyarta kwarin guiwa take bata da cewa watarana se labari.
Muje zuwa
Surbajo for life.
11/14/21, 12:43 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*page 4*
Yau tun asuba ta mik'e tayi duk aykace aykacenta,sabida yau ake taron sunan 'yar gidan inna hansai jummai ta haihu.
Ko da ta gama shiryawa,tuni su sabuwa da inna fure da sauran makwabtansu sun tafi gidan sunan,da ike a zango tai auren, Dan haka fitowa tayi cikin kwalliyarta ta nufi gidan su k'awarta Maimuna,dama tare zasu tafi gidan sunan.
Tana zuwa ta samu Maimunan ta shirya ita kawai take jira,Dan haka rankayawa sukai suka nufi titi Dan samun abun hawa da ze kaisu garin na zango.
Tsaye suke a bakin titin amma babu abun hawa,cikin damuwa Maimuna tace"yau fa alamu sun gwada 'yarfillo a k'afa zamuje zangon nan,kuma wallahi ga rana"
Murmushi Safna tayi daya k'ara fito da kyawun fuskarta,tace cikin siririyar muryarta,"da alama kuwa,kawai mu fara takawa,tunda ba wani nisa bane sosai,watak'ila a gaba mu samu"bata k'arasa maganar ba taji k'arar taka burki a gabansu,a tsorace dukan su suka dubi kan titin,wata shirgegiyar mota suka gani tana k'ok'arin gyara parking a gaban su,
Tana gama tsayawa na cikin motar ya fito,matashine kyakkyawa ajin farko,Wanda Hutu da ilimi suka samu masauki a jikinshi,sanye ike cikin farar shadda,tasha d'inkin zamani,kanshi ba hula se sumar daya Tara data dace da tsarin kwalliyar tashi.
Cikin takun burgewa ya k'araso gabansu fuskarshi d'auke da murmushi,yace"Amincin Allah ya tabbata a gareku,Ku gafarce ni firgitaku da nayi"ya k'arasa maganar yana had'e hannayensa guri guda.
Safna sarkin kunya,sunkuyar da kai tayi tana murmushi,yayin da maimuna tace"amin,mungode ba komai"
"In bazaki damuba Dan Allah kitaimaka min da sunan k'awar taki Dan naga kamar rowar magana gareta "yayi tambayar yana kallon fuskar Safna wacce har yanzu murmushi kawai take yi ba tace komai ba.
Murmushi maimuna tayi sannan tace "Safna sunanta dafatan ba zuwa sace ta kayi ba?"
Murmushi yayi yace"ita ta fara satoni,so shine nima nake so da taimakon ki ki tallafamin in saceta zuwa gidana na aure"
Da sauri Safna ta b'oye a bayan Maimuna,alamun taji kunya sosai,har zuwa lokacin murmushi be bar fuskarta ba.
"Se mun bincika tukuna in nagartarka ta kai a baka se ayi hakan sabida komai nufin Allah ne"
"Sunana Rayhan Hashim Daura,mahaifina Dan daura ne amma muna zaune a Abuja sabida yanayin Ayki,nazo bikin abokina ne nan yardaje,se kuma Allah ya had'ani da tawa amaryar a hanya"
Haka yay ta jansu da hira amma Safna ta gaza furta komai,har suka samu abun hawa,fafur suka k'i yarda su hau motarshi,gashi dukan su bame waya,Rayhan ganin zata kubce masa ne yasa ya d'auko wayarshi dank'areriya a gaban motarshi ya mik'awa Safna, yace "ba Dan na isa ba Dan Alfarmar Annabi ki amshi wayarnan,in muka rabu yanzu ban san ina zan sake ganinki ba,sabida yau zamu wuce gida,amma inda wayar a hannunki zan kira kimin kwatance"
Jiki a sanyaye Safna tasa hannu ta amshi wayar,se alokacin tace a tsorace murya na rawa,"zan zan...ajiyema in...muka had'u zaka amshi abunka"wani sanyine ya ratsa zuciyar Rayhan sakamakon jin muryarta da yayi.
"Na amince beauty semun had'un,"
Daga haka sukai sallama suka shiga mota shima ya shiga tashi,da ike hanya dayace haka yay ta bin su a baya har aka sauke su a zangon sannan yay musu hon yayi gaba.
Jikin Safna a sanyaye suka isa gidan sunan daya cika da jama'a.
Ko a gidan sunan seda aka mata habaicin ba mashinshini,ayko carab maimuna ta amshe zancen da cewa,"mashinshini de kam Safna Allah ya nufa ya shinshino ta,kuma insha Allahu se ya tsone idon mak'iyanta"
Ayko gaba d'aya gurin aka sa shewar zancen Nata.
Basu baro gidan sunan ba se isha'i sabida seda suka gyarawa mejego gida tukuna suka tafi.
A gajiye Safna take,Dan haka tana zuwa gida wanka tayi ta kintsa sannan ta Ciro wayar ta samu innarta tai mata bayanin komai game da had'uwarta da Rayhan yau.
Farincikine ya mamaye zuciyar innar ta,gami da yiwa Allah godiya daya fara haska tauraruwar 'yarta a idon manema sabida itama ta samu tai aure ta huta.
Nasiha da Jan kunne tai mata kan tade kama kanta da mutuncinta banda giggiwa,daga k'arshe tai fatan alkha'iri.
Muje zuwa
Surbajo for life
11/14/21, 12:43 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Page 5*
Safna shirin bacci tayi,tayi addu'a ta tofa tana kwanciya taji wani sauti me dad'i na tashi ak'asan fulonta,da har ta firgita can kuma ta tuna da wayar da Rayhan ya bata,Dan haka a tsanake ta d'auko wayar,bata wahalar gane kanta ba,sabida tana karatu,a hankali ta d'aga wayar ta kara a kunnenta,wata sassanyar ajiyar zuciya Rayhan ya saki wacce ta haddasawa Safna wani bak'on lamari ajikinta,sosai jikinta ya mutu,a hankali ta jiyo muryarshi yace a kasalance "beauty"sosai sunan da muryar da yay amfani da ita gurin kiran sunan Nata sukai mata dad'i,
ahankali cikin siririyar muryarta tace "ranka ya dad'e"
Rayhan kusan mirginowa yayi daga kan gadonshi Dan dad'in sunan da ta kira shi da shi,k'ara k'asa yay da murya sannan yace
"Kinyi kewa ta kuwa?"
Murmushi tayi me sauti sannan tace"gaskiya zan fad'ima ko k'arya?"
Yace "gaskiya"tace "to gaskiya d'aya banyi ba"
Shuru ya danyi sannan yace,"Ina sonki Safna shin kema kina sona kuwa?wallahi in har za'a bani ke safna nan da sati biyu na shirya auren ki,ba yaudarar ki nazo yi ba"
A hankali safna tace "Komai nufine na Allah, ganin farko zuciyata ta yarda da kai,ina fatan Allah ya baka ikon rik'eni amana,yasa akwai alkha'iri a tsakaninmu"
Cike da zumud'i yace "Amin beauty na"
Daga haka hira su kai ta abinda ya shafi karatu da nasaba,har zuwa sha d'ayan dare sannan su kai sallama yakashe.
Wasa wasa soyayya ce suke yinta me tsabta tsakanin Safna da Rayhan, sosai take jin son sa a zuciyarta,shima haka.
Tuni Inna Sabuwa ta sanar da Malam Habu komai sabida Safna bata b'oye mata komai tsakaninsu.
Yau Rayhan na hanyar zuwa gun masoyiyar tashi,shi murna ita murna,tun safe taje gidansu maimuna suka shiga girka abincin da zasu tarbe shi,Wanda Inna Sabuwace ta amso dubu uku gun malam ta bata,ayko wainar shinkafa sukai masa da miyar kaji Wanda malam yasa aka yanka zakaru manya guda biyu na tarbar sirikin nasa
Zob'o suka had'a suka siyo k'ank'ara suka sa,yayi sanyi gashi se k'amshin kayan k'amshi yake,fura da nono me kyau ta dama masa tasa k'ank'ara,sannan ta gurza kwakwa ta zuba aciki.
Acikin kulolin tarin auren maimuna aka jera komai,wanka tayi agidan su maimunan sannan tasa doguwar rigarta ta shadda me ruwan hanta,wacce k'anwar innarta ta d'inko mata a daura d'inki ya dace da jikinta, bata d'aura d'ankwalin ba,illa kama gashinta me yawan gaske da tayi da ribbon sannan ta fesa turare,bame kallonta yace awannan kauyen take,sosai kyanta ya fito,bin jikinta da doguwar rigar tayi shi ya bayyana asirin kyawun dirinta,domin duk inda akeson mace safna takai.
Tana tsaka da fesa turaren ne wayarta tai k'ara a hankali tasa hannu ta d'aga Dan tasan me kiran,cikin siririyar muryarta tace"ranka ya Dad'e ya hanyar?"
"Hanya Alhamdulillahi beauty gani na iso inda muka had'u daku ranar farko "
"Barka da zuwa bari in turo a k'araso da ku,"sabida yashaida mata tare da abokinsa suka zo.
Cikin shagwab'a yace"beauty ke nake son fara gani please babu D'an ayke a tsakaninmu kizo da kanki"
Murmushi tayi sannan tace "to ganinan zuwa"daga haka suka kashe wayar.
Dubanta ta kai gun maimuna tace" taso muje mu iso dasu mutumim naki kwai rigima wai sede inzo da kaina in mai iso"
Dariya maimuna tayi sannan tace "wallahi k'awata Ina tayaki murnar samun Rayhan amatsayin masoyi Allah yasa har aure,nima kuma Allah ya bani nawa masoyin muyi aure mu huta da gorin garinnan"
Murmushi Safna tayi tace"amin k'awata"
Mayafi maimuna ta yafa bayan ta dan murza hoda,da ike itama farace kyakkyawa,Tass ta fito,bakin titin suka nufa.