Sashe 3
Aure Da Haihuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rayhan ne zaune a kan boot d'in motar yana latsa waya, yayin da abokinsa Haisam ke tsaye a gefenshi yana ta masa dariya yace"Ni wallahi gaba d'aya na raina ajin naka ace ka wuce turai,ka wuce Abuja ka wuce Kaduna ka wuce kano ka wuce katsina wai kazo wannan k'auyen anan ka gano matar aure,se wani kurantata kake yi se mutum ya ganta ya kusa amai" dariya Rayhan yayi sannan yace,"Safna tafi duk 'yanmatan wa'innan guraren daka ambata,ita ta dabance"hango su safnar ne ya katse masa hanzari.
Inda ya diro daga kan motar yana fad'in "tsarki ya tabbata ga mak'agin wannan sura"
Safna na hangoshi yana mata murmushi itama tai k'asa da kai tana masa murmushin,har suka k'araso gurin su bakin Rayhan yak'i rufuwa,sabida tayi masa kyau fiye da yadda ya ganta rannan.
.shi kanshi haisam ya gigita da ganin Safna Dan koda ya hangosu be dauka su bane.
A hankali ya kai dubansa gun Rayhan yace"abokina 1000%tayi"dariya sukai sannan maimuna ta gaida haisam.
Shiko Rayhan yasa Safna a gaba se zagayeta yake yana k'are mata kallo yana yaba kyan da Allah yay mata azuciyarshi,amma afili fad'i yake,"inyenba y'anmatana ta yi kyau"
Duk ya gama bata kunya,Dan haka a d'an shagwab'ance Wanda bata san sanda tayi ba,tace"ya isa haka kuzo mu k'arasa gida mana baffa yana gida yana jiran k'arasowarka"
Kusan suman tsaye yayi jin yadda tai maganar a shagwab'e.
Motar ya buk'aci da ta shiga su k'arasa, mak'ale kafad'a tayi tana murmushi Wanda hakan sosai ya burge Rayhan, Dan haka haisam ke binsu abaya da motar shi kuma suka jero tare da gimbiyar tashi da maimuna zuwa k'ofar gidan.
Muje zuwa
Surbajo for life
11/14/21, 12:43 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Page 6*
Tunda suka jero idon yan garin yayo Kansu,Rayhan ko a jikinshi,shi hakan ma wani alfahari ya k'ara masa.
A k'ofar gidan suka tsaya sannan Safna ta shiga d'akin soro,ta sanar da malam zuwan nashi.
Umarnin ta shigo dashi ciki yayi mata, sannan ya mik'e ya shige cikin gida.
Komowa tayi gunshi kanta a k'asa tace ku shigo ciki inji malam.
Shide kunyar ta na k'ara sa mishi sonta a zuciyarshi, ansawa yayi,sannan suka biyota a baya har zuwa d'akin.
Dardumai ne shimfid'e a ciki,Dan haka zama su kai,Maimuna dama tuni ta nufi gidan su tasa k'aninta ya kwaso kayan abincin shi da abokinshi suka kawo inda su Farhan d'in suke.
A kunyace Safna ta zuba musu abincin,sannan ta mik'a gabansu tace "ga abinci kuci kunsha hanya",
Murmushi Rayhan yayi sannan ya kishingid'a yace"Nide se in a baki za'a bani zanci in ba haka ba nak'oshi"
A kid'ime ta zaro ido tana kallonshi,kan kace kwabo idanun ta sun kawo ruwa,cikin shagwab'a da muryar kuka tace"ka rufamin asiri,bansan ya Nisan garin Ku yake ba, amma ana fad'in se an wuce jihohi uku kan aje,taya zaka yo wannan tafiya kace ba zaka ci abincina ba,kuma fa tun safe nake had'a maka"ta k'arasa maganar cikin turo D'an k'aramin bakinta gaba.
Tunda ta fara magana hankalin Rayhan gaba d'aya ya koma kanta,sonta da sha'awarta ke shawagi a zuciyarsa,yadda yake son matarshi ta aure ta kasance haka safnar sa take.cikin sigar rarrashi yace "is ok baby na,wasa fa nake miki ni na isa in k'i cin abincin gimbiyata,share hawayenki kar haisam ya raina min ke tun yanzu"
Dariyar da haisam ya yine yasa ta mik'e ta fice daga d'akin da D'an gudunta,bin bayanta Rayhan yayi da idanu,ji kake makwat ya had'iye wani miyau daya taru masa abaki.
Koda suka gama cin abincin alwala su kai suka je masallaci su kai sallah sannan suka jero da malam zuwa cikin gidan.d'akin soron suka shiga.
Cikin girmamawa suka gaisa da malam sannan suka gabatar da Kansu Wanda haisam ne kewa malam bayani shi Rayhan yayi shuru alamun jin kunya.
Bayan dogon bayani malam ya gano gidan kakannin Rayhan dake daura farin sani ya sansu,amma sabida jawa y'arsa k'ima se yace.
"Naji duk bayanin ku kuma na gamsu da shi,zan yi bincike game da hakan in na ga ba wata matsalar na amince in daura aurenka da mamana kamar yadda ka buk'ata zan sa ka turo magabatan ka bayan na kammala binciken,Allah yay muku albarka"
Amsawa sukai da "Amin baba mungode Allah ya k'ara girma"sallama yay musu sannan ya fice daga d'akin,
Bayan fitar malam ba'a jima ba safna ta shigo kanta a k'asa alamar jin kunya,fuskarta d'auke da murmushi.
Guri ta samu ta zauna,bata jima da zama ba maimuna ta shigo,suka shiga hira dasu haisam,cike da wayewa haisam yace"maimuna muje ki nunamin kan garinnan naku,ko nima zanyi arba da y'ar fillon da zata saci tawa zuciyar "murmushi maimuna tayi sannan ta mik:e suka fice daga d'akin.
Shuru ne ta ratsa d'akin tun bayan ficewar su haisam,Safna tayi k'asa da kanta se wasa take da abun hannunta.
Cikin tattausar murya yace"na takura ki da yawa ko baby na?"cikin murmushi ta girgiza kanta alamar ba haka bane,murmushi yayi ya mik'e daga inda yake ya dawo kusa da ita ya zauna Wanda har jikinsu na tab'a juna,tsorone da firgici tsababa a idon safna,ya lura da hakan.
Murmushi yayi sannan ya sa hannu ya kamo hannunta,da sauri ta d'ago ido tana kallonshi,tana k'ok'arin kwace hannun Nata amma be bata damar hakan ba,a hankali ya furta,"Safna bazan tab'a cutar dake ba,ni din masoyinkine,amma naga ke kamar baki yarda dani ba,ko me yasa?"a hankali tace a d'an daburce "ba haka bane"
Matso da fuskarshi yayi sosai kusa da ta ta yana kallon idanuwan ta da shanyanyun idanuwan sa yace can k'asan mak'oshi "to yaya ne?"
Kasa magana tayi illa runtse idanun ta da tayi,Dan bazata iya jure kallon kwayar idanuwan sa ba
.murmushi yayi sannan ya saketa ya Dan matsa daga kusa da itan sannan yace "to oya bud'e idanun naki dodon ya matsa daga kusa dake"
Haka de yay ta jan ta da hira tun tana kin amsawa har tazo ta saki jiki dashi suka sha,hira.
Sai da aka idar da sallar isha'i sannan yay mata sallama bayan ya jibge mata kwalayen tsarabar da yayo mata,gami da bandir din kud'i dubu ashirin.duk yadda taso ya tafi da kud'in fafur yak'i,dole tasa ta amsa Dan har yayi fushi,.
Haka suka rabu cike da kewar juna,daura zasu su Kwana da safe su wuce abuja.
Muje zuwa
Surbajo for life
11/14/21, 12:43 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Page 7*
Cikin k'ank'anin lokaci Malam shi da Amininsa Baban maimuna suka je binciken waye Rayhan har garin Abuja.bayan sun gama binciken usulinsa na Daura.
Cikin ikon Allah ko ina beda nakasu,hakan sosai yayiwa malam dad'i Dan yana son Rayhan d'in.ya yaba da natsuwarsa.
Cikin sati guda mahaifin Rayhan da aminansa suka zo nemawa Rayhan d'in auren Safna, duk wani Abu na al'ada sun gabatar dashi inda aka sa ranar auren sati uku masu zuwa,Wanda shi Rayhan d'in Sam be so asa da nisa haka ba,Dan amatse yake da son mallakar matarshi.
Suko matan malam habaici da zagi da mugun fata game da auren na Safna ba Wanda basu yi ba,ita de Inna sabuwa ido tasa musu,a zuciyarta kuma ta na bin y'ar tata da addu'a.
Duk wani gyaran Amarya k'anwar innarta da ke daura ne tai mata,
Tuni Amarya ta fito a amaryarta.
Ko ina a garin na Sara gulmar auren na Safna ake yi,inda ake ta yamad'id'in auren kud'ine,shi yasa aka yi saurin tsaida lokaci.
Malam ma toshe kunnensa kawai yayi Dan maza ma ba'a barsu a baya ba gurin gulmar auren na 'yarsa
*********
Rayhan matashine D'an kimanin shekaru 33 da haihuwa,farine amma ba tas ba, dogo ne, me D'an jiki Wanda ba za'a kirashishi lukuti ba,dirarrene ta kowanne tsagi,
Fuskarshi zagaye take da kwantaccen sajen daya dace da zubin fuskarsa,
Rayhan mutum ne me ilimin boko da islamiyya sabida yayi dace da iyaye nagari Wanda suka bashi tarbiyya.
Ko kad'an sharholiya bata cikin tsarinsa a natse yake,shiyasa yake yawaita yin azumi Dan kame kansa
Mahaifinsa Alhaji Hashim D'an kwangilane,Wanda ya tara dukiya me yawa,matar sa D'aya,Hajiya Hafsa wacce takasance y'ar kasuwa dake saro kaya daga k'asashen waje ta kawo gida Nigeria ta siyar.
'Ya'yan su uku biyu mata d'aya namiji Wanda shine Rayhan d'in,kuma shine babba,sauran k'annensa ne,nuzula da jawahir,Wanda yanzu haka suna jami'a suna karatu.
Rayhan yayi karatu a k'asar England, inda yayi karatu a fannin kasuwanci,Wanda shine abinda yafi burgeshi shiyasa ya zabi fannin.
Koda ya kammala ya dawo gida, mahaifinshi mak'udan kud'ad'e ya bashi Dan ya fara gudanar da kasuwancin,in da be yi k'asa a guiwa ba yasa hannun jari a harkar saida man petur,sannan ya gina gidajen mai guda uku nashi nakanshi Dan jin dad'in gudanar da kasuwancin.
Tunda ya kammala karatu kullum burin iyayensa yayi Aure sabida shekarunsa na tafiya,shima yana da burin hakan se de wacce ze aura d'inne be gani ba.
Mahaifiyarsa da k'annensa sunfi kowa murna da jin ze yi aure,Dan haka suka shiga shirya lefe nagani na fad'a Wanda za'a kai gidan su Safna.
Wannan kenan
************
Ranar jumma'a dubban mutane suka halarci garin na Sara domin shaida auren Safna da Rayhan, Wanda ya kafa tarihi a garin na Sara.
.Wanda manyan 'yan kasuwa da jami'an gomnati,da masu fad'a aji suka halarci d'aurin Auren.
An d'aura auren akan sadaki naira dubu D'ari,Wanda ango Rayhan bakinsa Sam yak'i rufuwa ko ina ka waiga makad'a da marok'a ne ke ta aykinsu.
Tuni an gama shirya Amarya wacce tai kuka har ta godewa Allah, Dan tare da 'yan d'aurin Aure za'a tafi da ita,bayan malam yay mata nasiha game da zaman Aure.
Kuma malam ya hana kowa zuwa rakata,a cewarshi d'orawa mijinta d'awainiya za'a yi,
Haka aka fito da ita tana ta rusa kuka,motar da ango ke ciki aka sa ta,direba ya ja sauran motoci suka Mara musu baya.
Koda ta shiga motar d'ago ido tayi Dan taga waye a kusa da ita,carab idonta ya shiga nashi yana mata murmushi, fad'awa jikinshi tayi ta ci gaba da kukanta.
Rungumeta yayi sosai a jikinshi yana sakin wata ajiyar zuciya, wani Abu ke taso masa tun daga tafin k'afarsa zuwa tsakiyar kansa, a hankali ya shiga rarrashinta cikin murya me dad'i,yace"kukan na menene baby,haka?"cikin kukan take kai masa k'arar malam kan hana rakota da yayi.
Inda ya diro daga kan motar yana fad'in "tsarki ya tabbata ga mak'agin wannan sura"
Safna na hangoshi yana mata murmushi itama tai k'asa da kai tana masa murmushin,har suka k'araso gurin su bakin Rayhan yak'i rufuwa,sabida tayi masa kyau fiye da yadda ya ganta rannan.
.shi kanshi haisam ya gigita da ganin Safna Dan koda ya hangosu be dauka su bane.
A hankali ya kai dubansa gun Rayhan yace"abokina 1000%tayi"dariya sukai sannan maimuna ta gaida haisam.
Shiko Rayhan yasa Safna a gaba se zagayeta yake yana k'are mata kallo yana yaba kyan da Allah yay mata azuciyarshi,amma afili fad'i yake,"inyenba y'anmatana ta yi kyau"
Duk ya gama bata kunya,Dan haka a d'an shagwab'ance Wanda bata san sanda tayi ba,tace"ya isa haka kuzo mu k'arasa gida mana baffa yana gida yana jiran k'arasowarka"
Kusan suman tsaye yayi jin yadda tai maganar a shagwab'e.
Motar ya buk'aci da ta shiga su k'arasa, mak'ale kafad'a tayi tana murmushi Wanda hakan sosai ya burge Rayhan, Dan haka haisam ke binsu abaya da motar shi kuma suka jero tare da gimbiyar tashi da maimuna zuwa k'ofar gidan.
Muje zuwa
Surbajo for life
11/14/21, 12:43 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Page 6*
Tunda suka jero idon yan garin yayo Kansu,Rayhan ko a jikinshi,shi hakan ma wani alfahari ya k'ara masa.
A k'ofar gidan suka tsaya sannan Safna ta shiga d'akin soro,ta sanar da malam zuwan nashi.
Umarnin ta shigo dashi ciki yayi mata, sannan ya mik'e ya shige cikin gida.
Komowa tayi gunshi kanta a k'asa tace ku shigo ciki inji malam.
Shide kunyar ta na k'ara sa mishi sonta a zuciyarshi, ansawa yayi,sannan suka biyota a baya har zuwa d'akin.
Dardumai ne shimfid'e a ciki,Dan haka zama su kai,Maimuna dama tuni ta nufi gidan su tasa k'aninta ya kwaso kayan abincin shi da abokinshi suka kawo inda su Farhan d'in suke.
A kunyace Safna ta zuba musu abincin,sannan ta mik'a gabansu tace "ga abinci kuci kunsha hanya",
Murmushi Rayhan yayi sannan ya kishingid'a yace"Nide se in a baki za'a bani zanci in ba haka ba nak'oshi"
A kid'ime ta zaro ido tana kallonshi,kan kace kwabo idanun ta sun kawo ruwa,cikin shagwab'a da muryar kuka tace"ka rufamin asiri,bansan ya Nisan garin Ku yake ba, amma ana fad'in se an wuce jihohi uku kan aje,taya zaka yo wannan tafiya kace ba zaka ci abincina ba,kuma fa tun safe nake had'a maka"ta k'arasa maganar cikin turo D'an k'aramin bakinta gaba.
Tunda ta fara magana hankalin Rayhan gaba d'aya ya koma kanta,sonta da sha'awarta ke shawagi a zuciyarsa,yadda yake son matarshi ta aure ta kasance haka safnar sa take.cikin sigar rarrashi yace "is ok baby na,wasa fa nake miki ni na isa in k'i cin abincin gimbiyata,share hawayenki kar haisam ya raina min ke tun yanzu"
Dariyar da haisam ya yine yasa ta mik'e ta fice daga d'akin da D'an gudunta,bin bayanta Rayhan yayi da idanu,ji kake makwat ya had'iye wani miyau daya taru masa abaki.
Koda suka gama cin abincin alwala su kai suka je masallaci su kai sallah sannan suka jero da malam zuwa cikin gidan.d'akin soron suka shiga.
Cikin girmamawa suka gaisa da malam sannan suka gabatar da Kansu Wanda haisam ne kewa malam bayani shi Rayhan yayi shuru alamun jin kunya.
Bayan dogon bayani malam ya gano gidan kakannin Rayhan dake daura farin sani ya sansu,amma sabida jawa y'arsa k'ima se yace.
"Naji duk bayanin ku kuma na gamsu da shi,zan yi bincike game da hakan in na ga ba wata matsalar na amince in daura aurenka da mamana kamar yadda ka buk'ata zan sa ka turo magabatan ka bayan na kammala binciken,Allah yay muku albarka"
Amsawa sukai da "Amin baba mungode Allah ya k'ara girma"sallama yay musu sannan ya fice daga d'akin,
Bayan fitar malam ba'a jima ba safna ta shigo kanta a k'asa alamar jin kunya,fuskarta d'auke da murmushi.
Guri ta samu ta zauna,bata jima da zama ba maimuna ta shigo,suka shiga hira dasu haisam,cike da wayewa haisam yace"maimuna muje ki nunamin kan garinnan naku,ko nima zanyi arba da y'ar fillon da zata saci tawa zuciyar "murmushi maimuna tayi sannan ta mik:e suka fice daga d'akin.
Shuru ne ta ratsa d'akin tun bayan ficewar su haisam,Safna tayi k'asa da kanta se wasa take da abun hannunta.
Cikin tattausar murya yace"na takura ki da yawa ko baby na?"cikin murmushi ta girgiza kanta alamar ba haka bane,murmushi yayi ya mik'e daga inda yake ya dawo kusa da ita ya zauna Wanda har jikinsu na tab'a juna,tsorone da firgici tsababa a idon safna,ya lura da hakan.
Murmushi yayi sannan ya sa hannu ya kamo hannunta,da sauri ta d'ago ido tana kallonshi,tana k'ok'arin kwace hannun Nata amma be bata damar hakan ba,a hankali ya furta,"Safna bazan tab'a cutar dake ba,ni din masoyinkine,amma naga ke kamar baki yarda dani ba,ko me yasa?"a hankali tace a d'an daburce "ba haka bane"
Matso da fuskarshi yayi sosai kusa da ta ta yana kallon idanuwan ta da shanyanyun idanuwan sa yace can k'asan mak'oshi "to yaya ne?"
Kasa magana tayi illa runtse idanun ta da tayi,Dan bazata iya jure kallon kwayar idanuwan sa ba
.murmushi yayi sannan ya saketa ya Dan matsa daga kusa da itan sannan yace "to oya bud'e idanun naki dodon ya matsa daga kusa dake"
Haka de yay ta jan ta da hira tun tana kin amsawa har tazo ta saki jiki dashi suka sha,hira.
Sai da aka idar da sallar isha'i sannan yay mata sallama bayan ya jibge mata kwalayen tsarabar da yayo mata,gami da bandir din kud'i dubu ashirin.duk yadda taso ya tafi da kud'in fafur yak'i,dole tasa ta amsa Dan har yayi fushi,.
Haka suka rabu cike da kewar juna,daura zasu su Kwana da safe su wuce abuja.
Muje zuwa
Surbajo for life
11/14/21, 12:43 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Page 7*
Cikin k'ank'anin lokaci Malam shi da Amininsa Baban maimuna suka je binciken waye Rayhan har garin Abuja.bayan sun gama binciken usulinsa na Daura.
Cikin ikon Allah ko ina beda nakasu,hakan sosai yayiwa malam dad'i Dan yana son Rayhan d'in.ya yaba da natsuwarsa.
Cikin sati guda mahaifin Rayhan da aminansa suka zo nemawa Rayhan d'in auren Safna, duk wani Abu na al'ada sun gabatar dashi inda aka sa ranar auren sati uku masu zuwa,Wanda shi Rayhan d'in Sam be so asa da nisa haka ba,Dan amatse yake da son mallakar matarshi.
Suko matan malam habaici da zagi da mugun fata game da auren na Safna ba Wanda basu yi ba,ita de Inna sabuwa ido tasa musu,a zuciyarta kuma ta na bin y'ar tata da addu'a.
Duk wani gyaran Amarya k'anwar innarta da ke daura ne tai mata,
Tuni Amarya ta fito a amaryarta.
Ko ina a garin na Sara gulmar auren na Safna ake yi,inda ake ta yamad'id'in auren kud'ine,shi yasa aka yi saurin tsaida lokaci.
Malam ma toshe kunnensa kawai yayi Dan maza ma ba'a barsu a baya ba gurin gulmar auren na 'yarsa
*********
Rayhan matashine D'an kimanin shekaru 33 da haihuwa,farine amma ba tas ba, dogo ne, me D'an jiki Wanda ba za'a kirashishi lukuti ba,dirarrene ta kowanne tsagi,
Fuskarshi zagaye take da kwantaccen sajen daya dace da zubin fuskarsa,
Rayhan mutum ne me ilimin boko da islamiyya sabida yayi dace da iyaye nagari Wanda suka bashi tarbiyya.
Ko kad'an sharholiya bata cikin tsarinsa a natse yake,shiyasa yake yawaita yin azumi Dan kame kansa
Mahaifinsa Alhaji Hashim D'an kwangilane,Wanda ya tara dukiya me yawa,matar sa D'aya,Hajiya Hafsa wacce takasance y'ar kasuwa dake saro kaya daga k'asashen waje ta kawo gida Nigeria ta siyar.
'Ya'yan su uku biyu mata d'aya namiji Wanda shine Rayhan d'in,kuma shine babba,sauran k'annensa ne,nuzula da jawahir,Wanda yanzu haka suna jami'a suna karatu.
Rayhan yayi karatu a k'asar England, inda yayi karatu a fannin kasuwanci,Wanda shine abinda yafi burgeshi shiyasa ya zabi fannin.
Koda ya kammala ya dawo gida, mahaifinshi mak'udan kud'ad'e ya bashi Dan ya fara gudanar da kasuwancin,in da be yi k'asa a guiwa ba yasa hannun jari a harkar saida man petur,sannan ya gina gidajen mai guda uku nashi nakanshi Dan jin dad'in gudanar da kasuwancin.
Tunda ya kammala karatu kullum burin iyayensa yayi Aure sabida shekarunsa na tafiya,shima yana da burin hakan se de wacce ze aura d'inne be gani ba.
Mahaifiyarsa da k'annensa sunfi kowa murna da jin ze yi aure,Dan haka suka shiga shirya lefe nagani na fad'a Wanda za'a kai gidan su Safna.
Wannan kenan
************
Ranar jumma'a dubban mutane suka halarci garin na Sara domin shaida auren Safna da Rayhan, Wanda ya kafa tarihi a garin na Sara.
.Wanda manyan 'yan kasuwa da jami'an gomnati,da masu fad'a aji suka halarci d'aurin Auren.
An d'aura auren akan sadaki naira dubu D'ari,Wanda ango Rayhan bakinsa Sam yak'i rufuwa ko ina ka waiga makad'a da marok'a ne ke ta aykinsu.
Tuni an gama shirya Amarya wacce tai kuka har ta godewa Allah, Dan tare da 'yan d'aurin Aure za'a tafi da ita,bayan malam yay mata nasiha game da zaman Aure.
Kuma malam ya hana kowa zuwa rakata,a cewarshi d'orawa mijinta d'awainiya za'a yi,
Haka aka fito da ita tana ta rusa kuka,motar da ango ke ciki aka sa ta,direba ya ja sauran motoci suka Mara musu baya.
Koda ta shiga motar d'ago ido tayi Dan taga waye a kusa da ita,carab idonta ya shiga nashi yana mata murmushi, fad'awa jikinshi tayi ta ci gaba da kukanta.
Rungumeta yayi sosai a jikinshi yana sakin wata ajiyar zuciya, wani Abu ke taso masa tun daga tafin k'afarsa zuwa tsakiyar kansa, a hankali ya shiga rarrashinta cikin murya me dad'i,yace"kukan na menene baby,haka?"cikin kukan take kai masa k'arar malam kan hana rakota da yayi.