← Book details Aure Da Haihuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 22

Sashe 5

Aure Da Haihuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Pain killer yabata,sannan ya d'auketa cak zuwa dakin shi inda ya kwantar da ita yana ta lallab'ata har tai bacci.

Farin cikin da Rayhan yake ciki baze iya misaltashiba,Dan da kyar yay bacci.

Koda gari ya waye safna kunyar Rayhan d'in take ji ba kad'an ba,Dan ko magana ta kasa yi masa,shi ke janta da hira gamida tsokana.

Zaman Rayhan da Safna zamane na tsantsar so da k'aunar juna,danginshi na sonta itama haka.

Rayhan mutum ne meson haihuwa shiyasa ya kwallafa rai kan son ganin Safna tasamu ciki Wanda tsawon shekaru hud'u na auransu hakan be samu ba,

Safna na zuwa university, shekarar k'arshe take tana karantar mass communication, matsalar rashin haihuwarta itama yana damunta.

Hakanne yasa suka fara yawon Neman magani Wanda kullum basa gajiya.

A wannan tsukunne Allah yayiwa mahaifin Safna rasuwa,sosai tai kukan rashin mahaifinta,ga tausayin mahaifiyarta wacce bata da isasshiyar lafiya sakamakon ciwon zuciya dake damunta.

Rayuwar bata mata dad'i,ganin tayi nesa da mahaifiyarta bare ta taimaka mata, a k'ok'arin Rayhan naganin ya kwantar mata da hankaline ya d'aukar ma innar tata y'ar ayki dake kulawa da ita.

To a yawon Neman maganine suka had'u da doctor Amina har k'addarar sauya kwayoyin dashen haihuwar ta fad'a musu.

Muje zuwa

Surbajo for life.
11/14/21, 12:44 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀

*Zahra Surbajo*

*Page 10*

Watanni biyu doctor Amina ta kwashe
Neman Rayhan a waya amma bata shiga,
Ji take yi kamar tai hauka, gaba d'aya ta fice daga hayyacinta,bata gane komai.kullum addu'arta Allah ya basu ikon dawowa gareta.

A nasu B'angaren ko Rayhan da safna,suna can k'asar Germany inda Rayhan yaje domin gudanar da wani kasuwanci.

Tunda doctor Amina ta shaida mishi Safna Nada ciki ya d'auki son duniya ya d'orawa cikin,kulawar da yake ba Safna ko kanshi be bawa ita.

Duk wani fata da burin shi akan cikin ya d'ora shi,hakanne yasa yay alwashim duk ranar daya koma Nigeria ze yiwa doctor Amina kyautar da bazata taba mantawa ba.

Watansu biyu ya kammala abinda ya kaishi,Dan haka suka fara shirin komowa gida,
Safna ce ta matsa kan su koma d'in sabida rashin lafiyar mamanta,amma shi a so samunsane se ta haihu ze maido ta gidan.

Ta Lagos suka sauka,sannan suka hau wani jirgin zuwa Abuja, suna sauka a airport suka tarad da direba yazo d'aukarsu.

'Yan uwan Rayhan sosai sukai murna da dawowar tasu,game da cikin jikin safna kuwa,har walimar samuwarshi suka shirya.

Satin su d'aya da dawowa Rayhan yace Safna ta shirya suje su kaiwa doctor Amina ziyara,sannan aduba masa lafiyarta Dana abun da ke cikinta.

Cikin nishad'i da jin dad'i suke takawa a harabar asibitin zuwa office d'in doctor Amina,
Zaune take a office d'in,tana tunanin hanyar da zata sada ta da Rayhan, taji an matsa k'ararrawar Neman izinin shigowa.

Bata son kowa yazo inda take a halin yanzu,amma rashin sanin ko waye yasa ta bada izinin shigowa,a zatonta Mara lafiya aka kawo.

Shigowarsu office d'in yasa doctor mik'ewa a razane tana kallonsu, bakinta har rawa yake wajan ambatar sunanshi,
"Rayhan!!!"

Murmushi yayi gami da samun guri suka zauna,yace"surprise ko?"

A hankali doctor ta koma ta zauna bakin ta bud'e tana kallonsu kamar a mafarki.

"Doctor ya ayki,ya kuma akaji da jama'a,kin ganmu se yau"cewar Rayhan fuskarshi d'auke da murmushi.
.baki na rawa doctor tace"Alhamdulillahi Rayhan, na kusa haukacewa gurin neman ka"ta 'karasa maganar cikin damuwa.

Maida hankali shi yayi gunta sosai ya gyara zama sannan yace"da akayi ya ya doctor kike nemana?banganeba"

Glass d'in fuskarta ta cire sannan ta share hawayen da suka zubo mata,tace"matsala aka samu yayin gudanar da aykin dashen da aka yiwa safna"

A razane Rayhan da Safna suka d'ago ido suna kallonta,bakin safna har rawa yake tace"doctor wacce irin matsala kuma,?don Allah kimana bayani"

File d'in komai ta d'auko,sannan ta mikawa Rayhan da sauri ya fara dubawa,ita kuma taci gaba da masa bayani.

"Yayin gudanar da aykin aka samu matsalar sakamakon kamanceceniya ta suna da kuke dashi kai da Farhan, cikin dake jikin safna Rayhan ba naka bane na Farhan ne,kai kuma kwayoyinka da a kasa ma matarsa basu sa tayi cikin ba"daga haka de ta kwashe komai ta sanar dashi,gamida had'a hannayenta guri d'aya alamar Neman afuwar kuskuren da aka samun.

D'ago ido yayi yana kallon likitar cikin alamar rashin yadda da abinda tace, ganin hakane yasa doctor d'aukar Qur'anin dake gefenta,kasancewar tana da alwala tace cikin kuka"na rantse da duk wata gaskiya dake cikin wannan littafi me tsarki gaskiya na sanar daku"

Yanke jiki da safna tayi ta fad'ine yasa su waigowa gareta a razane sukai kanta suna kiran sunanta.

Da sauri doctor ta kira ma'aikata aka shigo da gadon d'aukar marasa lafiya aka d'auketa zuwa wani d'akin inda doctor tashiga k'ok'arin ceto rayuwarta.

Rayhan samun Kansa yayi da kasa bin bayansu ya zube a office d'in doctor Aminar yana danasanin amincewa da yin dashen da yayi tun lokacin da aka bashi shawarar yin hakan,wannan wacce irin mummunar k'addara ce tabbas a matsayinsa na musulmi dole ya yarda da hakan.

Runtse idonsa yayi wasu zafafan hawaye suka shiga zubo masa,da ya rasa ta ya ze tsaidasu.

Yana nan zaune doctor ta shigo,tace"ta farfad'o,kai take son gani yanzu"

D'ago ido yayi ya kalli doctor d'in yace a sanyaye,"zanje gida in dawo ki ci gaba da kulawa da ita,"daga haka yasa hannu a aljihu ya d'auko kudi ya ajiyewa doctor d'in,sannan ya juya ya fice daga office d'in.

Cikin rashin fahimta doctor tabi bayansa da kallo har ya fice.

Muje zuwa

Surbajo for life.
11/14/21, 12:44 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀

*Zahra Surbajo*

*Gidan suna naje yau aymin uzuri*

*Page 11*

Jiki a sanyaye doctor ta koma gun Safna ta shaida mata ya fita amma yanzu ze dawo,
Sosai Safna tai mamakin tafiyar Rayhan batare daya zo yaga halin da take ciki ba,
Amma seta boye damuwarta,ta runtse ido tana hango rayuwar da zata yi da cikin da ba na mijinta ba agidan auranta.

A nashi bangaren Rayhan gida ya koma,yana shiga dakinsa ya shige ya kulle kansa aciki,fadawa kan gadonsa yayi sannan ya rushe da kuka tamkar karamin yaro.

Seda yaji kansa ya fara ciwo sannan ya yi shuru,yaso yaje yaga halin da Safna take ciki amma yakasa yin hakan sabida zafin da zuciyarshi ke masa.

Wasa wasa seda Safna ta kwashe sati guda a asibitin ba Rayhan ba dalilinsa,safna tayi kukan har ta godewa Allah, ko wayarshi ta kira be dauka,dole tasa doctor Yi mata allurar bacci akai akai,sabida gudun kar ta haifarwa kanta matsalar da zata shafi Dan dake cikinta.

Doctor ce ke jinyarta da kanta har zuwa ranar da ta warware.

Shigowa dakin doctor tayi fuskarta dauke da murmushi, take kallon Safna dake zaune gefen gadon tayi tagumi.

Karasowa tayi ta zame mata hannun sannan tace,"madam tunani ba kyau ayanayin da kike, komai yay zafi maganinsa Allah"

Share hawayen da suka zubo mata tayi sannan tace a raunane"doctor rayuwata na gab da rushewa,a sakamakon wannan kaddarar,mijina fishi yake dani kan abinda bani da masaniya akai doctor ya zanyi"takarasa maganar cikin kuka.

"Ki kwantar da hankalin ki Rayhan ba fushi yake dake ba da mune yake fushin Wanda nasan sannu a hankali ze huce,yanzu ki taso in saukeki agida yamma nayi,kuma an sallameki"tayi maganar cikin sigar rarrashi.

A hankali Safna ta sakko akan gadon tasa takalminta tayi hanyar fita batare da tace komai ba,bin bayanta doctor tayi suka fice.

A hanya doctor ta Dan fara Jan ta da hira da cewa"karki damu safna kowa da jarabawarshi a rayuwa,insha Allah komai ze zama kamar baayiba,mubar komai zuwa lokacin da zaki haihu"

Itade Safna ta tafasa batace ba hankalinta nagun Rayhan.

A haka ta dinga nunawa doctor Amina hanya,har suka iso gidan.doctor na sauketa ta juya ta wuce,da sauri.

A hankali ta shiga cikin gidan me gadi na mata barka da zuwa.

Kofar falon ta tura ta shiga a hankali bakinta dauke da sallama.

Zaune yake a falon yana kallon TV,a hankali ya dago ido yana kallonta,take yanke yaji kunyar duniya ta lullubeshi,tabbas be kyauta ba,mikewa yayi tsaye yana kallonta itama shi take kallo.

Gangarowar hawayen da ke idontq ne yasa ta kauda kanta ta wuce zuwa cikin dakinta.
Kan gado ta zauna hawayen na ci gaba da zubo mata,ko a mafarki aka ce mata Rayhan ze mata haka zata karyata.

Wai yau ita Rayhan ke wulakantawa sabida mummunar kaddarar data fada mata.

Tana tsaka da wannan tunanin ya turo kofar dakin ya shigo.
Daga bakin kofar dakin ya tsaya,yay mata ya jiki sannan ya Dora da abinda ya kawoshi.

"Safna,wannan de ya Riga ya faru se muyi fatan Allah kyauta gaba,ni abinda nake ganin shine masalaha a lamarinnan,shine azubar da wannan shegen cikin kowa ya huta,Dan da a haifeshi gwanda azubar da Dan banza,ko kema se kinfi samun kwanciyar hankali"yayi maganar batare da damuwar komai ba.

A razane ta dago jajayen idanuwanta tana bin sa da wani kallo,kamin ta numfasa tace"Rayhan Dan dake cikin nawa kake kira shege a gaban idona?"tayi maganar wasu hawayen na zubo mata

Cikin halin ko in kula yace "To in ban kirashi shege ba da na kikeso in kirashi?"

Muje zuwa

Surbajo for life
11/14/21, 12:44 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀

*Zahra Surbajo*

Watanni biyu doctor Amina ta kwashe wajen Neman Rayhan a waya amma bata shiga,
Ji take yi kamar tai hauka, gaba d'aya ta fice daga hayyacinta,bata gane komai.kullum addu'arta Allah ya basu ikon dawowa gareta.

A nasu B'angaren ko Rayhan da safna,suna can k'asar Germany inda Rayhan yaje domin gudanar da wani kasuwanci.

Tunda doctor Amina ta shaida mishi Safna Nada ciki ya d'auki son duniya ya d'orawa cikin,kulawar da yake ba Safna ko kanshi be bawa ita.

Duk wani fata da burin shi akan cikin ya d'ora shi,hakanne yasa yay alwashim duk ranar daya koma Nigeria ze yiwa doctor Amina kyautar da bazata taba mantawa ba.

Watansu biyu ya kammala abinda ya kaishi,Dan haka suka fara shirin komowa gida,
Safna ce ta matsa kan su koma d'in sabida rashin lafiyar mamanta,amma shi a so samunsane se ta haihu ze maido ta gidan.

Ta Lagos suka sauka,sannan suka hau wani jirgin zuwa Abuja, suna sauka a airport suka tarad da direba yazo d'aukarsu.
Chapter 5 · 0% Book details