Sashe 14
Aure Da Haihuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Safna rayuwar bata mata dadi ko kadan,ga Farhan yayi fushi da ita,ga Rayhan yabar kasar,baffa ko magana baya mata,haka matarshi,ita kadai take rayuwa agidan na baffa,se in garin yayi mata zafi taje gun maimuna ta debe mata kewa.
Yau ma da wuri ta kimtsa junior, ta nufi gidan maimunan.
Bayan sun gaisa,maimuna ta dubi Safna cikin damuwa tace"Safna in fa ka rasa mafadi kai kaiwa kanka,ke kinga yadda kika koma kuwa,kinyi baki kin rame, akan namijin daba mijin aurankiba,yakamata fa kiyiwa kanki fada"
Wasu hawayene masu zafi suka zubo mata,ta dubi maimuna cikin raunin murya tace"Maimuna su baffa basu fahimceni bane,Rayhan na bukatar kulawa ta macen shi ta Aure,ki duba kulawar daya ba mahaifiyata tun daga ciwonta har zuwa mutuwarta,Rayhan ya kula da komai nawa,kuma shi wannan abun da yamin shike nuna cewa shi Dan Adam ne,Tara yake be cika goma ba,Rayhan ya bani ilimin da Nike takama dashi,ki duba lamarin nan,yanzu shi Farhan fisabilillahi me yayimin, da ya cancanci in wulakanta Rayhan akanshi,kowanne da na halak fa baya mance halacci kuma duk Wanda ya tallafi mahaifanka kamar nasa ji kake duniya kaf ba kamar sa "ta karasa maganar tana kuka me tsuma zuciya.
Shuru maimuna tayi tana nazarin maganar ta Safna can ta nisa,tace"komai kika fadi Safna gaskiya ne,Rayhan yakai ki soshi,sede abinda nakeso ki gane, Rayhan yana da kazamin kishi Wanda idonsa ke rufewa har ke ya wulakanta,kuma koda yanzu kin koma gareshi bazaku zauna lafiya ba,sabida baze so danki ba,kuma ke bazaki yarda ya nuna masa kiyayyaba,bama haka ba,Farhan amsar dansa zeyi,shin kina da tabbacin haifar wani Dan Bayan junior din,?Rayhan mutumin kirki ne amma beda zuciya me karfin daukar kaddara,yanzu kike rayuwa baasan wacce kaddarace nan gaba zata kara fada miki ba"
"To baki ga shi farhan din wulakancin da yay min ba,tafiya fa yayi ya bar ni, kuma ko nemana baya yi,bare Dan shi"ta yi maganar cikin nuna takaicin abinda yayi matan.
Murmushi maimuna tayi sannan tace "to Safna so kike yasa a daureki asa masa a mota,kefa kika karade gari da ihu kan ba kya sonshi,to laifine Dan ya tafi yabarki da masoyin naki?"
Harara ta jefawa maimuna sannan tace"baki fahimceni ba,ay da ya rarrasheni,da zan bishi,zuciya fa yayi yatafi,da sona yake,ay da ya rarrasheni"
Dariya maimuna takeyi kamar cikinta zeyi ciwo,dakyar ta tsagaita tace"Safna ko de kin fara kewar mijin naki me jajayen kunnuwanne?"
Duka Safna ta kaiwa maimuna sannan tace"to laifine,jiki da jini da lafiya in kasa kewar mijina?"
Wata uwar shewa,Maimuna tayi ta kwashe da dariya gamida rangada guda.
"To ko bikon Farhan ya kama ki,Dan wallahi baze dawo nemanki ba,Dan shima naga alamar akwai kishi,sede me tsabta Dan wlh da Rayhan ne sakin ki zeyi,daga baya yazo yana danasani"
Harara Safna ke zabgawa maimuna kamar idonta ze fado.
Muje zuwa
Surbajo for life.
11/15/21, 12:08 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Number danasa akan littafin nan,ta business ce kamar yadda na fadi,ko anmin mgn kan inturo littafi ko insa mutum a group bazan bada amsa ba,haka nace, amma salon de ace ga abinda kayi aji haushinka wasunku na tamin mgnr da bata shafi kasuwancin ba,pls yakamata kusan uzurin mutum don Allah*
*Page 33*
To tunda Safna tabar gidan maimuna lissafinta ya kubce,sosai take kewar mijin Nata, Dan ta kai ta kawo ko bacci bata iyayi.
Gaba daya tayi baki, ta lalace, bame ganin ta ya dauka itace.
Tayi kuka tayi addua kan Allah ya kawo Farhan din gareta,amma,shuru kamar an shuka dusa.
Tsawon watanni shida kenan,da tafiyarsa,hankalin Safna in yayi dubu ya tashi,yanzu ta yarda Dari bisa Dari tana matukar kaunar mijinta kuma tana kewarshi.
Ganin da tayi shurun baze mata bane yasa ta tuntubi maimuna da Neman shawara.
"Kije gun doctor Amina mana,ko kije gun yar uwarsa Sarah a Kaduna su nemoshi"cewar maimuna.
Cikin damuwa Safna tace"bazan iya zuwa gun Sarah ba maimuna a duniya ba abinda take so sama da Farhan, nasan ranta be mata dadiba kan abinda nai masa,sede ko doctor Amina din"
"To kije gareta nasan insha Allahu zata karbeki,ta kuma hadaki da mijin ki"
Da wannan shawarar suka rabu,zuciyar Safna cike da kwarin guiwa, tabbas gobe zata tafi Abuja Dan haduwa da doctor Amina.
A nashi bangaren Farhan kusan kullum seya kira doctor Amina yaji,ko Safna ta fara nemansa,"doctor ina kewar matata bazan boye miki ba"cewar Farhan cikin damuwa.
"Kayi hakuri ka daure, kabar,komai har zuwa ta nemeka,"cewar doctor
Tsaki yayi sannan yace"yarinyar fa Sam bata da hankali kina fa ganin abinda tamin"cewar Farhan cikin damuwa.
"A kara hakuri yallabai,duk inda Safna take nasan tana cike da kewarka"
Da irin wainnan kalamun doctor ke rarrashin Farhan Dan bata so yafara sakkowa Safna ta raina shi.
Yau Safna tun asuba ta gama shirya kayanta,ta kimtsa junior itama ta kimtsa, sannan ta nufi dakin baffa tai sallama ya amsa mata gami da bada izinin shigowa.
Koda tashi ga gaisheshi tayi,sannan ta ce "baffa dama kudin mota nakeso abani,zani Abuja gun doctor Amina, inason magana da ita"ta fadi cike da tsoron me ze biyo baya.
Murmushi baffa yayi,sannan yace"zaki gun doctor Amina ko de zaki Neman Farhan?"
Da sauri Safna ta cukuikuye fuskarta cikin hijabi,Dan sosai taji kunya.
"A baya kin batamin rai amma yau kin farantamin kuma naji dadi,Allah yay miki albarka,kizamo me biyayya da hakuri da mijinki,rashin kunya duk ba naki bane,a ka ida Safna senayi bincike kan in aurar dake ga Farhan amma gamsuwa da nayi da hankalin sa yasa nabashi ke,kuma insha Allahu babu danasani awannan auran,Safna kiyi wa Aure biyayya.kuma yanzu ki kiramin innar taki tazo ta shirya mu biki Abujar Dan ganin gidan doctor Aminar"
Safna sabida tsananin farin ciki har kuka takeyi,bata taba tsammanin baffa zema saurareta ba.
Godiya tai masa sosai,sannan, ta mike taje ta kira masa matar tasa.
Da misalin karfe biyu na rana,Safna suka isa Asibitin doctor Amina,
Basu jima da zuwa ba doctor ta fito daga zagayen marasa lafiya, sanda taga Safna dasu baffa ba karamin dadine yakamata ba,Safna ko se kunyar hada ido takeyi da ita.
Bata ko zauna ba,ta kwashe su a mota zuwa gidan ta,ji take kamar tai tsalle Dan murna.
Koda suka isa gidan sosai kan safna ya kwance,ganin hotunan Farhan ta ko ina acikin gidan,wai meye alakar Farhan da doctor Amina ne?tana son sanin wannan amsar.
Abinci doctor ta gabatar musu,me rai da lafiya, Bayan sun ci sun sha, taba su baffa masaukinsu,sannan taba Safna ma Nata.
Seda dare yayi suka samu damar zantawa da doctor inda baffa yafara da cewa"mude Amina,ke muka Sani dangin Farhan, amanar Safna gaba daya mun baki, Safna ta gane kurenta,gatanan munkawota ki sada ta da mijin ta"
Murmushi doctor tayi,sannan ta dubi Safna cikin sigar zolaya tace"baffa banaso ayi mata dole,ya kamata ayi hakuri Ku koma da ita Dan da bakinta ta shaida mishi bata sonshi,kaga.."safna ce ta katseta da hanzari tana kuka tana fadin.
"Wallahi bazan koma Sara ba,ni gurin mijina zaki kaini,ay kece kika zugashi ya aureni shine zaku wani tafi Ku barni sekace bazawara,wlh se kin kaini gun mijina,nagaji"ta karasa maganar cikin kuka.
Ba doctor ba,hatta baffa da inna dariya suke mata,se alokacin Safna ta kula da katobarar da tayi Dan haka da gudu tabar gurin zuwa dakinta da doctor ta sauketa..
Haka de su baffa suka gama magana da doctor karshe Farhan ta kira,suka yi magana dashi,sosai,yaji dadin sakkowar Safna godiya yakewa su baffa, doctor na fassara musu.
Makudan kudi yasa doctor ta basu in zasu koma.
Washegari da wuri su baffa suka tafi,Safna har kuka tayi na rabuwarsu.
Muje zuwa
Surbajo for life.
11/16/21, 11:09 PM - Ummi Tandama😇: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Page 34*
Bayan doctor Amina takai su baffa airport kamar yadda Farhan ya bukata,kai tsaye gida ta dawo gurin Safna.
A dakinta ta sameta,Safna na ganinta kunya ta kamata tayi kasa da kanta,murmushi doctor tayi sannan ta karasa kusa da ita ta zauna,sannan ta dafo kafadarta,ta fara magana cikin tattausan lafazi.
"Safna tun da wannan kaddara ta fada miki Allah ya jarabceni da sonki,ina kallonki tamkar kanwata wacce muka fito ciki daya,batu na gaskiya Safna kin bata ran Farhan fiye da tunanin ki,dami ne kika tsinta a kala amma kikeso ki banzatar,ta koina Farhan ba tsaranki bane,amma ya nuna miki ke yake kauna kika watsa masa kasa a ido,akwai ayki agabanki,Dan gaskiya in yayi fushi irin haka yana da wiyar sakkowa"
Idon safna ne ya kawo kwalla,cikin hardewar murya tace"ki bashi hakuri ,ni wlh bansan meyasa nayi hakanba,amma yanzu na gane kuskurena"ta karasa maganar cikin kuka.
Murmushi doctor tayi sannan tace "ze sakko amma bada wuri ba,se kin zage damtse sosai sannan kinyi hakuri kamin kiyi Nasara,bama wannan ba,kinga Farhan yana da mata,maana kina da kishiya,kuma itama Balarabiyace, Dan haka bazan kaiki gareshi ba har se na kimtsaki,Dan kanki har yanzu akwai kura,dole a kakkabeta".
Shuru Safna tayi tana nazarin maganganun doctor din,Farhan Nada mata wayyo Allah ita ta shiga uku,taya zata iya kishi da Balarabiya,anya ba hakura zatayi da auran ba kuwa?
Haka de doctor taita kokarin wayar mata da kai akan lamarin zama da kishiya,da kuma abubuwa da tasan Farhan din naso da Wanda be so.
Wasa wasa Safna seda ta kwashe tsawon watanni biyu a gidan doctor tana tsumata da magunguna,sannan tana koyar da ita darussan aure.
Sosai Safna tayi kyau ta murje tayi wata kiba, ta musamman wacce ta kara fito da kyanta.
Ga wani fari da tayi,Wanda in ba magana tayi ba dauka zakayi itama Balarabiyarce.
Babu ta inda doctor bata gyara Safna ba ciki da waje,ita kanta bata gajiya da kallon safnar.
Yau da wuri ta dawo daga Asibiti, zamanta a falo kenan,wayar ta ta hau kara da sauri ta daga ganin Farhan ne ke kiranta,
Gaisawa suka yi cikin girmamawa,kamar yadda suka saba,sannan Farhan yace"wai Amina ko de ke na aurowa yarinyar nan ne,?nasa miki ido inga iya gudun ruwanki,amma naga baki gane ba,kinga ki sakomin matata a jirgi,tazo tasameni,ina kewar yarona,sosai"
Dariya doctor tayi,sannan tace"tuba nake yallabai,last week da mukayi waya cewa kayi private jet zaka turo mana in mun shirya, to kai muke jira"
"Na kira Abdallah(mijin doctor) a waya dazu yace yana Lagos,so nakira Taufeeq nasa yashirya muku komai,gobe jirgin zezo mun samu izinin haka,Dan haka banda bata lokaci jirgin safene"cewar Farhan a tsanake.
Yau ma da wuri ta kimtsa junior, ta nufi gidan maimunan.
Bayan sun gaisa,maimuna ta dubi Safna cikin damuwa tace"Safna in fa ka rasa mafadi kai kaiwa kanka,ke kinga yadda kika koma kuwa,kinyi baki kin rame, akan namijin daba mijin aurankiba,yakamata fa kiyiwa kanki fada"
Wasu hawayene masu zafi suka zubo mata,ta dubi maimuna cikin raunin murya tace"Maimuna su baffa basu fahimceni bane,Rayhan na bukatar kulawa ta macen shi ta Aure,ki duba kulawar daya ba mahaifiyata tun daga ciwonta har zuwa mutuwarta,Rayhan ya kula da komai nawa,kuma shi wannan abun da yamin shike nuna cewa shi Dan Adam ne,Tara yake be cika goma ba,Rayhan ya bani ilimin da Nike takama dashi,ki duba lamarin nan,yanzu shi Farhan fisabilillahi me yayimin, da ya cancanci in wulakanta Rayhan akanshi,kowanne da na halak fa baya mance halacci kuma duk Wanda ya tallafi mahaifanka kamar nasa ji kake duniya kaf ba kamar sa "ta karasa maganar tana kuka me tsuma zuciya.
Shuru maimuna tayi tana nazarin maganar ta Safna can ta nisa,tace"komai kika fadi Safna gaskiya ne,Rayhan yakai ki soshi,sede abinda nakeso ki gane, Rayhan yana da kazamin kishi Wanda idonsa ke rufewa har ke ya wulakanta,kuma koda yanzu kin koma gareshi bazaku zauna lafiya ba,sabida baze so danki ba,kuma ke bazaki yarda ya nuna masa kiyayyaba,bama haka ba,Farhan amsar dansa zeyi,shin kina da tabbacin haifar wani Dan Bayan junior din,?Rayhan mutumin kirki ne amma beda zuciya me karfin daukar kaddara,yanzu kike rayuwa baasan wacce kaddarace nan gaba zata kara fada miki ba"
"To baki ga shi farhan din wulakancin da yay min ba,tafiya fa yayi ya bar ni, kuma ko nemana baya yi,bare Dan shi"ta yi maganar cikin nuna takaicin abinda yayi matan.
Murmushi maimuna tayi sannan tace "to Safna so kike yasa a daureki asa masa a mota,kefa kika karade gari da ihu kan ba kya sonshi,to laifine Dan ya tafi yabarki da masoyin naki?"
Harara ta jefawa maimuna sannan tace"baki fahimceni ba,ay da ya rarrasheni,da zan bishi,zuciya fa yayi yatafi,da sona yake,ay da ya rarrasheni"
Dariya maimuna takeyi kamar cikinta zeyi ciwo,dakyar ta tsagaita tace"Safna ko de kin fara kewar mijin naki me jajayen kunnuwanne?"
Duka Safna ta kaiwa maimuna sannan tace"to laifine,jiki da jini da lafiya in kasa kewar mijina?"
Wata uwar shewa,Maimuna tayi ta kwashe da dariya gamida rangada guda.
"To ko bikon Farhan ya kama ki,Dan wallahi baze dawo nemanki ba,Dan shima naga alamar akwai kishi,sede me tsabta Dan wlh da Rayhan ne sakin ki zeyi,daga baya yazo yana danasani"
Harara Safna ke zabgawa maimuna kamar idonta ze fado.
Muje zuwa
Surbajo for life.
11/15/21, 12:08 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Number danasa akan littafin nan,ta business ce kamar yadda na fadi,ko anmin mgn kan inturo littafi ko insa mutum a group bazan bada amsa ba,haka nace, amma salon de ace ga abinda kayi aji haushinka wasunku na tamin mgnr da bata shafi kasuwancin ba,pls yakamata kusan uzurin mutum don Allah*
*Page 33*
To tunda Safna tabar gidan maimuna lissafinta ya kubce,sosai take kewar mijin Nata, Dan ta kai ta kawo ko bacci bata iyayi.
Gaba daya tayi baki, ta lalace, bame ganin ta ya dauka itace.
Tayi kuka tayi addua kan Allah ya kawo Farhan din gareta,amma,shuru kamar an shuka dusa.
Tsawon watanni shida kenan,da tafiyarsa,hankalin Safna in yayi dubu ya tashi,yanzu ta yarda Dari bisa Dari tana matukar kaunar mijinta kuma tana kewarshi.
Ganin da tayi shurun baze mata bane yasa ta tuntubi maimuna da Neman shawara.
"Kije gun doctor Amina mana,ko kije gun yar uwarsa Sarah a Kaduna su nemoshi"cewar maimuna.
Cikin damuwa Safna tace"bazan iya zuwa gun Sarah ba maimuna a duniya ba abinda take so sama da Farhan, nasan ranta be mata dadiba kan abinda nai masa,sede ko doctor Amina din"
"To kije gareta nasan insha Allahu zata karbeki,ta kuma hadaki da mijin ki"
Da wannan shawarar suka rabu,zuciyar Safna cike da kwarin guiwa, tabbas gobe zata tafi Abuja Dan haduwa da doctor Amina.
A nashi bangaren Farhan kusan kullum seya kira doctor Amina yaji,ko Safna ta fara nemansa,"doctor ina kewar matata bazan boye miki ba"cewar Farhan cikin damuwa.
"Kayi hakuri ka daure, kabar,komai har zuwa ta nemeka,"cewar doctor
Tsaki yayi sannan yace"yarinyar fa Sam bata da hankali kina fa ganin abinda tamin"cewar Farhan cikin damuwa.
"A kara hakuri yallabai,duk inda Safna take nasan tana cike da kewarka"
Da irin wainnan kalamun doctor ke rarrashin Farhan Dan bata so yafara sakkowa Safna ta raina shi.
Yau Safna tun asuba ta gama shirya kayanta,ta kimtsa junior itama ta kimtsa, sannan ta nufi dakin baffa tai sallama ya amsa mata gami da bada izinin shigowa.
Koda tashi ga gaisheshi tayi,sannan ta ce "baffa dama kudin mota nakeso abani,zani Abuja gun doctor Amina, inason magana da ita"ta fadi cike da tsoron me ze biyo baya.
Murmushi baffa yayi,sannan yace"zaki gun doctor Amina ko de zaki Neman Farhan?"
Da sauri Safna ta cukuikuye fuskarta cikin hijabi,Dan sosai taji kunya.
"A baya kin batamin rai amma yau kin farantamin kuma naji dadi,Allah yay miki albarka,kizamo me biyayya da hakuri da mijinki,rashin kunya duk ba naki bane,a ka ida Safna senayi bincike kan in aurar dake ga Farhan amma gamsuwa da nayi da hankalin sa yasa nabashi ke,kuma insha Allahu babu danasani awannan auran,Safna kiyi wa Aure biyayya.kuma yanzu ki kiramin innar taki tazo ta shirya mu biki Abujar Dan ganin gidan doctor Aminar"
Safna sabida tsananin farin ciki har kuka takeyi,bata taba tsammanin baffa zema saurareta ba.
Godiya tai masa sosai,sannan, ta mike taje ta kira masa matar tasa.
Da misalin karfe biyu na rana,Safna suka isa Asibitin doctor Amina,
Basu jima da zuwa ba doctor ta fito daga zagayen marasa lafiya, sanda taga Safna dasu baffa ba karamin dadine yakamata ba,Safna ko se kunyar hada ido takeyi da ita.
Bata ko zauna ba,ta kwashe su a mota zuwa gidan ta,ji take kamar tai tsalle Dan murna.
Koda suka isa gidan sosai kan safna ya kwance,ganin hotunan Farhan ta ko ina acikin gidan,wai meye alakar Farhan da doctor Amina ne?tana son sanin wannan amsar.
Abinci doctor ta gabatar musu,me rai da lafiya, Bayan sun ci sun sha, taba su baffa masaukinsu,sannan taba Safna ma Nata.
Seda dare yayi suka samu damar zantawa da doctor inda baffa yafara da cewa"mude Amina,ke muka Sani dangin Farhan, amanar Safna gaba daya mun baki, Safna ta gane kurenta,gatanan munkawota ki sada ta da mijin ta"
Murmushi doctor tayi,sannan ta dubi Safna cikin sigar zolaya tace"baffa banaso ayi mata dole,ya kamata ayi hakuri Ku koma da ita Dan da bakinta ta shaida mishi bata sonshi,kaga.."safna ce ta katseta da hanzari tana kuka tana fadin.
"Wallahi bazan koma Sara ba,ni gurin mijina zaki kaini,ay kece kika zugashi ya aureni shine zaku wani tafi Ku barni sekace bazawara,wlh se kin kaini gun mijina,nagaji"ta karasa maganar cikin kuka.
Ba doctor ba,hatta baffa da inna dariya suke mata,se alokacin Safna ta kula da katobarar da tayi Dan haka da gudu tabar gurin zuwa dakinta da doctor ta sauketa..
Haka de su baffa suka gama magana da doctor karshe Farhan ta kira,suka yi magana dashi,sosai,yaji dadin sakkowar Safna godiya yakewa su baffa, doctor na fassara musu.
Makudan kudi yasa doctor ta basu in zasu koma.
Washegari da wuri su baffa suka tafi,Safna har kuka tayi na rabuwarsu.
Muje zuwa
Surbajo for life.
11/16/21, 11:09 PM - Ummi Tandama😇: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Zahra Surbajo*
*Page 34*
Bayan doctor Amina takai su baffa airport kamar yadda Farhan ya bukata,kai tsaye gida ta dawo gurin Safna.
A dakinta ta sameta,Safna na ganinta kunya ta kamata tayi kasa da kanta,murmushi doctor tayi sannan ta karasa kusa da ita ta zauna,sannan ta dafo kafadarta,ta fara magana cikin tattausan lafazi.
"Safna tun da wannan kaddara ta fada miki Allah ya jarabceni da sonki,ina kallonki tamkar kanwata wacce muka fito ciki daya,batu na gaskiya Safna kin bata ran Farhan fiye da tunanin ki,dami ne kika tsinta a kala amma kikeso ki banzatar,ta koina Farhan ba tsaranki bane,amma ya nuna miki ke yake kauna kika watsa masa kasa a ido,akwai ayki agabanki,Dan gaskiya in yayi fushi irin haka yana da wiyar sakkowa"
Idon safna ne ya kawo kwalla,cikin hardewar murya tace"ki bashi hakuri ,ni wlh bansan meyasa nayi hakanba,amma yanzu na gane kuskurena"ta karasa maganar cikin kuka.
Murmushi doctor tayi sannan tace "ze sakko amma bada wuri ba,se kin zage damtse sosai sannan kinyi hakuri kamin kiyi Nasara,bama wannan ba,kinga Farhan yana da mata,maana kina da kishiya,kuma itama Balarabiyace, Dan haka bazan kaiki gareshi ba har se na kimtsaki,Dan kanki har yanzu akwai kura,dole a kakkabeta".
Shuru Safna tayi tana nazarin maganganun doctor din,Farhan Nada mata wayyo Allah ita ta shiga uku,taya zata iya kishi da Balarabiya,anya ba hakura zatayi da auran ba kuwa?
Haka de doctor taita kokarin wayar mata da kai akan lamarin zama da kishiya,da kuma abubuwa da tasan Farhan din naso da Wanda be so.
Wasa wasa Safna seda ta kwashe tsawon watanni biyu a gidan doctor tana tsumata da magunguna,sannan tana koyar da ita darussan aure.
Sosai Safna tayi kyau ta murje tayi wata kiba, ta musamman wacce ta kara fito da kyanta.
Ga wani fari da tayi,Wanda in ba magana tayi ba dauka zakayi itama Balarabiyarce.
Babu ta inda doctor bata gyara Safna ba ciki da waje,ita kanta bata gajiya da kallon safnar.
Yau da wuri ta dawo daga Asibiti, zamanta a falo kenan,wayar ta ta hau kara da sauri ta daga ganin Farhan ne ke kiranta,
Gaisawa suka yi cikin girmamawa,kamar yadda suka saba,sannan Farhan yace"wai Amina ko de ke na aurowa yarinyar nan ne,?nasa miki ido inga iya gudun ruwanki,amma naga baki gane ba,kinga ki sakomin matata a jirgi,tazo tasameni,ina kewar yarona,sosai"
Dariya doctor tayi,sannan tace"tuba nake yallabai,last week da mukayi waya cewa kayi private jet zaka turo mana in mun shirya, to kai muke jira"
"Na kira Abdallah(mijin doctor) a waya dazu yace yana Lagos,so nakira Taufeeq nasa yashirya muku komai,gobe jirgin zezo mun samu izinin haka,Dan haka banda bata lokaci jirgin safene"cewar Farhan a tsanake.