← Book details Aure Da Haihuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 22

Sashe 12

Aure Da Haihuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dukawa yayi da yaron a hannunsa,yana kuka yakai goshinsa kasa yayiwa Allah sujjada,yana masa kirari,ya jima kamin ya dago daga sujjadar,yakai dubansa gun Safna wacce takasa banbance bacci take ko idonta biyu.

A hankali ya furta"ina kika shiga nake kokarin karade duniya Dan nemanki?"

Kasa magana tayi,hakanne yasa ta durkushe agurin tana kuka.

Ta jima tana kukan,ba Wanda yay kokarin tsaida ita,seda tagaji Dan kanta,sannan ta dago,tana share hawayen ta.

Ga mamakin ta Farhan ne durkushe agaban ta ya kureta da ido,fuskarshi dauke da alamar tausayawa, suna hada ido,tai kasa da kanta,Dan bata iya jure kallon shi.

Hannu yasa ya dago habarta,yace cikin muryar rarrashi"duk abinda ya faru dake na samu labari,ranar da kukaje kotu,na ji komai agun doctor, adaren ranar na iso kasarnan,sede koda nazo munje gidan auranki,munsamu labarin yasakeki shikuma yabar garin,nayi iya bakin kokarina insan gidan iyayenki abun ya faskara,yanzu ma wannan dawowar da nayi labarin dawowar mijinki nasamu shine nazo muje mu rokeshi yasanar damu inda zamu sameki,"yakai maganar yana share mata hawayen dake bin idonta tunda yafara maganar.

Cikin tattausar murya ya furta "Safna ban kyaleku a wahala Dan bana sonku ba hasalima komai inayi ne domun jin dadinku"

Da haka yasamu ta dena kuka.Sarah ce taje jikin Farhan dauke da junior ta rungume shi tana kukan murna,cikin kukan take fadin"Dan uwa Ashe zamuga wannan rana,nasan yau Abi in yaji labarin nan baze iya barci ba"rungume ta yayi shima yana murmushi yace "karki sanar dashi,ganinsu,so Nike na mai bazata dasu"

Safna da farinciki yagama rufewa mikewa tayi ahankali tabar falon zuwa dakin ta.

Farhan da gaba daya hankalinshi na kanta,mikewa yayi rungume da junior yabi ta abaya.

Muje zuwa

Surbajo for life.
11/14/21, 12:49 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀

*Zahra Surbajo*

*Page 28*

Tana shiga dakin kan gadonta ta fada ta saki wani kuka Mara sauti,ta rasa kukan ko na menene.

Farhan Wanda batasan ya biyota ba,A sanyaye ya zauna kusa da kafafunta,Azabure ta mike zaune jin mutum akusa da ita.

Cikin yanayin damuwa data bayyana a fuskarshi, yace"Safna komai ya faru da bawa fa da sanin Allah, kaddararki kenan ba yadda za ayi ki goge ta ko ki canja ta,yakamata ki dawo cikin hankalinki, ki rungumi rayuwarki a yadda tazo miki, bana jin dadin ganinki cikin damuwa,se in kasance cikin zargin kaina"ya karasa maganar yana kallonta.

A sanyaye ta dago tana kallon shi,sannan,tace"kawai nima na tuno rayuwa ta da Rayhan ne a baya kamin faruwar kaddatata"

A natse yake kallonta yanason ya gano menene aynihin abinda ke cikin zuciyarta.nisawa yayi sannan yace"ki daukeni,a matsayin Dan uwanki,ni kuma insha Allahu bazan barki kiyi kuka ba,sabida haka ki fadamin aynihin abinda ke zuciyarki"

A hankali ta dago ta kalleshi sannan tace "dama so Nike ka sasanta ni dashi in koma dakina sabida Aure shine darajata,kuma mun rabu ne dalilin junior tunda yanzu ba cikin a jikina nasan ze maida ni dakina"

Ko da wasa Farhan be dauka abinda zata ce ba kenan,sosai ta bashi mamaki, kuruciyarta takara bayyana agareshi,murmushi yayi sannan yace "kin daukeni a matsayin Dan uwanki?"

Gyada masa kai tayi cikin nuna amincewa.

Mikewa yayi ya mika mata junior sannan yace"To yanzu jego kikeyi,ki maida hankali ki shayar min da yarona da kyau nan da shekara biyu se ayi zancan komawarki gidan mijin naki ko"ya daga mata gira yana murmushi.

Da sauri Safna tace"Shekara biyu fa kace,?"

"Yes shekara biyu fa,ko tayi kadanne?"Farhan ya tambaya yana murmushi.

Sakkowa tayi daga kan gadon,rike da junior, tace bakinta na rawa."Dama ay so Nike in hadu da baban junior din se in bashi abunshi ni kuma in koma gun mijina,ni base na yaye shi ba,ko yanzu ma ni na shirya bada shi"

Se yanzu ya sake tabbatarwa Safna yarinya ce,danya sharab,Dan haka murmushi yayi,yace"to badamuwa wani satin zan koma Dubai zan tafi dashi,wannan ba matsala bane"yana kaiwa nan ya juya ze fice daga dakin,da sauri Safna tace.

"To yaushe zaka sasanta ni da mijin nawa,sabida Sarah tamin alkawarin zaka sasanta da mijina da zaran kaji labarina"

Kureta yayi da shanyanyun idanuwanshi na tsawon lokaci bece komai ba,a hankali Safna ta sauke idonta daga nashi,ta kasa jure kallon shi,

Ficewa yayi daga dakin yaje yasamu doctor Amina ya shaida mata bukatar Safna ta son komawa gidan mijinta.

Dariya doctor take harda hawaye, sannan tace"kuruci dangin hauka,"

Muje zuwa

Surbajo for life.
11/14/21, 12:51 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀

*Zahra Surbajo*

*Page 29*

Duk wata matsala da yadda zasu shawo kanta suka shirya shida doctor Amina,sosai ya yaba da hankalin doctor shiyasa duk tsayin lokaci be mance taba.

Doctor A gidan zata Kwana,Dan haka dakin Safna tai masaukinta.

Koda dare yayi suna zaune akan gadon Safna, doctor na sawa junior Pampers, takalli Safna tace tana murmushi.

"Abun Allah safna kinga yadda komai yazo mana cikin sauki,naji Baban junior na cewa next week ze tafi da junior kasarsu ko?"ta fadi tana nazarin safnar.

Shuru safna tayi kamar me tunani zuwa can tace"to doctor in ya tafi dashi ba kya ganin kamar ze cutu,sabida jinjirine?"

"Kema de safna da wani zance kike, to ke ina ruwanki da cutuwarsa ko akasin hakan,ay gyagijewa zakiyi ki gyara kan ki kuma ki komawarki gidan Rayhan shima nasan dole zeso ki dawo"

Da sauri safna takai dubanta gun doctor, cikin sanyin murya tace"Doctor don Allah ki amshi Junior ke ki rikemin shi,sabida in dinga zuwa ina ganinshi kuma nasan babanshi ze baki shi,ina tsoron yayi nisa dani."safna tay maganar hawaye na bin idonta.

Kallon uku saura kwata doctor tai mata,sannan tace"ke da kike uwarshi kin gujeshi sabida bukatar ki tason komawa gidan mijin da be nemi komenki ba,ni awa dazan dauki renon Dan da ba nawa ba,kinga safna mubar zancannan,tunda Allah yasa ubansa ya bayyana kuma ze tafi da abunsa ke meye naki na damuwa"doctor takai karshen zancen sanda ta gyara filo ta kwanta

Safna shuru tayi tana kallon doctor, sosai zancen doctor ya taba zuciyarta,kuma ta bata haushi,Dan haka cikin kunkuni murya kasa kasa tace"kada Allah yasa ki rikemin din mana, ay ba Neman kai nake dashi ba"🤣komai carab akunnen doctor, wacce dariya ta kusa kubce mata na tsiwar safnar.

Harara safna tai ta dokawa doctor Amina,sannan ta dauke hannun doctor daga kan junior dake bacci kusa da ita,ta dawo da abunta kusa da ita🤣se kunkuni takewa doctor din,

Shuru tai mata tayi kamar tana bacci,amma dariya aranta ko tayi ta ba adadi.

Koda gari ya waye safna cika take tana batsewa,tayiwa junior wanka ta bashi nono yasha,ta goye abunta abaya,Dan aranta take fadin "tunda ba sa sonka har sukeson kaika wata duniyar to ba zan ba kowa kai ba."

Karfe Tara na safe Farhan yafito falo,yaga kowa ya hallara amma banda safna, Dan haka me renon junior din ya tura yace taje ta kirata,

Dawo da ita tayi tace ace azumi take😄

Ba Farhan ba hatta su Sarah dariya suke,me jegon da ko sati biyu batayi ba da haihuwa da azumi😄

Murmushi Farhan yayi sannan yace to taje tace ta bada junior zasu gaisa,

Dawo da ita tayi tace ace masa na karfin bugi da kwaci ne.😄

Ah ah,lamarin na safna ya dauko daki,Dan haka mikewa yayi ya nufi dakin da kanshi,

Zumbur ta mike data ganshi,gaba daya ta rude,kasa tai da kai tana Sosa keya,

Murmushi yayi sannan yace"nazo mu gaisa da junior ne,in an bani dama"

Bata da niyyar kwance shi a bayanta Dan haka juyo masa fuskarshi tayi azuwan su gaisa a hakan.

Murmushi yayi me kayatarwa sannan ya taka ya isa inda take,be jira komai ba,yasa hannunshi setin kirjinta ya kwanto goyon na Junior, A razane tai baya jin hannunshi saman kirjinta,

Be sauraretaba yakoma kan kujera rungume da junior din,yana masa wasa,gefe ta koma ta rakube,lokaci bayan lokaci tana wurga masa harara.

Fuskarshi dauke da murmushi ya dago ya kalleta,yace"Tunda kinga next week zan tafi da junior akwai bukatar ki yayeshi yau,kibani abuna,anjima zamuje da doctor asiyo masa madarar da zata dace dashi, so Nike na kware akan kula dashi kan na kaiwa matata shi" yakarasa maganar yana nazarin fuskarta.

Ayko cunkuso baki tayi gaba tafara kunkuninta Wanda ba abinda Farhan bejiba sabida da turanci tayi maganar.

"Tabdijan,naga me kunne iwa Jan kosan daze daukemin yaro yatafi dashi wata kasar,wlh baa haifi mutum ba ehe,,abar ganina shuru shuru wlh nima shegiyar kaina ce akan yarona"🤣

Sosai zancen yaba Farhan dariya amma ko kadan be bari taga hakanba.

Haka ya karaci zamanshi,yatashi yamika mata Junior ya fice ya bar mata dakin.

Gun doctor Amina yakoma ya fadi mata duk yadda sukayi,itama ta sanar dashi yadda suka kare jiya,
Dariya yayi sannan yace "wato tanason yaron kuma tanason komawa gun mijinta,amma bata yarda yaron yay nisa da ita ba"

Dariya doctor tayi sannan tace "Kuruciya ke damun safna da kauyanci,In banda haka taya mutumin daya gujeka sanda kake bukatar taimako kai kace wai gunshi zaka koma?a sannu burinmu ze cika insha Allahu".

"Na shirya ba Safna kulawa da dukkan wata dama da Allah ya bani,ina son Safna doctor amma naga alamun kamar ita bata raayina,ko Dan ni ba bakar fata bane?"

"Ko kadan ba haka bane Farhan,nan gaba zaka tabbatar da hakan, kuma wannan rashin kunya da kaga tanayi,ba halin safna bane wlh ita wai tanayine Dan kar a kwace mata danta, amma safna mace ce me hakuri da biyayya"

Murmushi yayi,sannan yace,"inason rashin kunyar tata ni ay"

Dariya sukayi gaba dayansu.

Koda dare yayi,safna na zaune ta gama ba Junior nono,Tana shirin kwanciya, Farhan yashigo dakin,mikewa zaune tayi tana kallon shi,kai tsaye junior ya dauka,yayi hanyar fita dashi,da sauri Safna ta mike tasha gabanshi tace.
."malam ina zaka kaimin yaro a tsohon darennan?"

"Kin manta dazu nace zaa yayeshi, ay shine nazo in dauke shi."

Be jira me zata ce ba ya raba ta gefenta ya wuce rungume da junior.

Baki ta saki tana kallon shi,Dan ita bata taba ganin Dan rainin hankali ba irinshi.

Kan gado taje tai kwanciyarta,aranta tana fadin"shashancin banza,da kanka zaka dawo dashi in yatashi yanason nono"

Shiko Farhan dakinshi ya shige da junior, yaje ya kwantar dashi ayko baccinshi yake hankali kwance,shima gefenshi ya kwanta yana karewa yaron kallon kaunarsa na kara shiga zuciyarshi.

Safna wacce tuni tai baccinta hankali kwance.
Chapter 12 · 0% Book details