← Book details Aure Da Haihuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 22

Sashe 11

Aure Da Haihuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Be sauraretaba yakoma kan kujera rungume da junior din,yana masa wasa,gefe ta koma ta rakube,lokaci bayan lokaci tana wurga masa harara.

Fuskarshi dauke da murmushi ya dago ya kalleta,yace"Tunda kinga next week zan tafi da junior akwai bukatar ki yayeshi yau,kibani abuna,anjima zamuje da doctor asiyo masa madarar da zata dace dashi, so Nike na kware akan kula dashi kan na kaiwa matata shi" yakarasa maganar yana nazarin fuskarta.

Ayko cunkuso baki tayi gaba tafara kunkuninta Wanda ba abinda Farhan bejiba sabida da turanci tayi maganar.

"Tabdijan,naga me kunne iwa Jan kosan daze daukemin yaro yatafi dashi wata kasar,wlh baa haifi mutum ba ehe,,abar ganina shuru shuru wlh nima shegiyar kaina ce akan yarona"🤣

Sosai zancen yaba Farhan dariya amma ko kadan be bari taga hakanba.

Haka ya karaci zamanshi,yatashi yamika mata Junior ya fice ya bar mata dakin.

Gun doctor Amina yakoma ya fadi mata duk yadda sukayi,itama ta sanar dashi yadda suka kare jiya,
Dariya yayi sannan yace "wato tanason yaron kuma tanason komawa gun mijinta,amma bata yarda yaron yay nisa da ita ba"

Dariya doctor tayi sannan tace "Kuruciya ke damun safna da kauyanci,In banda haka taya mutumin daya gujeka sanda kake bukatar taimako kai kace wai gunshi zaka koma?a sannu burinmu ze cika insha Allahu".

"Na shirya ba Safna kulawa da dukkan wata dama da Allah ya bani,ina son Safna doctor amma naga alamun kamar ita bata raayina,ko Dan ni ba bakar fata bane?"

"Ko kadan ba haka bane Farhan,nan gaba zaka tabbatar da hakan, kuma wannan rashin kunya da kaga tanayi,ba halin safna bane wlh ita wai tanayine Dan kar a kwace mata danta, amma safna mace ce me hakuri da biyayya"

Murmushi yayi,sannan yace,"inason rashin kunyar tata ni ay"

Dariya sukayi gaba dayansu.

Koda dare yayi,safna na zaune ta gama ba Junior nono,Tana shirin kwanciya, Farhan yashigo dakin,mikewa zaune tayi tana kallon shi,kai tsaye junior ya dauka,yayi hanyar fita dashi,da sauri Safna ta mike tasha gabanshi tace.
."malam ina zaka kaimin yaro a tsohon darennan?"

"Kin manta dazu nace zaa yayeshi, ay shine nazo in dauke shi."

Be jira me zata ce ba ya raba ta gefenta ya wuce rungume da junior.

Baki ta saki tana kallon shi,Dan ita bata taba ganin Dan rainin hankali ba irinshi.

Kan gado taje tai kwanciyarta,aranta tana fadin"shashancin banza,da kanka zaka dawo dashi in yatashi yanason nono"

Shiko Farhan dakinshi ya shige da junior, yaje ya kwantar dashi ayko baccinshi yake hankali kwance,shima gefenshi ya kwanta yana karewa yaron kallon kaunarsa na kara shiga zuciyarshi.

Safna wacce tuni tai baccinta hankali kwance.

Cikin dare ta farka sakamakon zafin da nononta yake mata,ya wani cicciko har zuba yakeyi.

Duk da Ac dake dakin gumi takeyi,duk yadda taso jurewa ta kasa.

Ga wani zazzabi dake Neman kamata

Ganin tarasa sarki se Allah ne yasa ta mike ta fice a hargitse zuwa bangaren Farhan sabida yabata junior ta bashi nonon yashanye mata.

Koya zata kaya oho

Muje zuwa

Surbajo for life.
11/14/21, 12:49 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀

*Zahra Surbajo*

*in banyi ba gobe to se aymin uzuri,jiki da jini😊*

*Page 26*

A tsorace ta isa bangaren nashi,koda ta taba kofar falon jinta tayi abude Dan haka kutsa kai tayi bakinta dauke da Sallama.

Farhan dake zaune kan darduma,yana lazimi,dagowa yayi adan tsorace yana kallonta.

Dan dedeta natsuwarta tayi sannan tace tana in Ina, "dama.,..dama junior nazo dauka"

Kallonta yayi sannan yayi murmushi yace"junior kuma,meye hadinki dashi a tsohon darennan yaron da tun dare aka yayeshi"yayi maganar yana nazarin fuskarta.

Kumburo baki tayi,sannan ta kauda kai gefe cikin sigar rashin kunya,tace"tunda a garin gaba gaba muke ba,ni kabani shi in wuce"

Sosai tsiwar ta safna ke sashi nishadi,Dan haka kara kunnota yayi.da cewa"kinga Malama ki ficemin daga daki,yarode ay nawa ne kuma na amshi abuna,kamar yadda kika bukata to menene na zuwa kuma yanzu?"

Safna ganin ba sarki se Allah ne yasa ta sakko daga rashin kunyar Dan taga bazata kaita ba,tace cikin siririyar muryar,"Na fasa baka shi Ku tafi,zan rikeshi ay"

"To dama ni ay base kin baniba,inada ikon kwace kayana,tunda nawane,kinga bacci zanyi,kuma kina hayaniya karki tayar min da yaro"Farhan ya fadi sanda ya mike ya wuce bedroom dinsa yabarta tsaye tana rawar sanyi Dan zuwa lokacin tuni zazzabi ya rufeta.

Durkushewa tayi agurin,ta dunkule,hawaye nabin fuskarta,tama kasa magana.

Farhan jin shuru bata biyoshi ba kuma beji karar bude kofar fitarta bane yasa ya leko Dan yaga me takeyi.

Dardumar daya tashi akai ita take lullube da ita tana rawar sanyi,da sauri ya karasa inda take,yana tambayarta ko lafiya.

Shuru ba amsa se rawar sanyin da takeyi,a hankali yakai hannu ya yaye dardumar,gaba daya breast dinta awaje suke,sabida cikar da sukayi,ruwan nonon duk ya jika mata jiki,ga wasu jijiyoyi dasuka fito akan nonon,rudu rudu dasu.

Cirosu tayi daga cikin rigar ko zata samu sassaucin azabar da suke mata.

Tausayinta ne ya mamaye duk wani sashe na jikinshi,ba na wasa ba,koda yakai hannu goshinta,zafine rau kamar wuta.

A hankali yasa hannu ya kamata ya mikar da ita, Ina ko tsayawa bata iyawa,sabida jirin dake daukarta,idanuwanta a lumshe.

Daukarta yayi gaba dayanta,yaje ya kwantar da ita akan gadon da junior yake,Dan yafahimci dama lalurarce tasa tazo amsar yaron amma rashin kunyarta ya hana tai masa bayani.

Koda ya kwantar da ita hannu yasa ya dauki junior din,ya Dan jijjigashi ayko ya farka ya fara tsala kuka,a hankali ya mika shi setin kan nonon,ayko carab ya kama,

Safna kamar a mafarki taji yana shan nonon,duk da zafin da takeji amma haka ta tallafoshi da kyau Dan yaji dadin shan nonon.

Ganin ta rikeshi ne yasa ya sake ta,yaja bargo ya lullubesu,sannan yakashe Ac dakin,ya kunna heater Dan tasamu dumi.

Kan kujera ya koma ya zauna tausayinta na kara shigarshi,ji yake kamar ya cire mata ciwon.

Duk da ruwan nonon ya masa yawa amma yasha sosai,kuma tuni nonon ya rage kumburin dayayi.

Bacci ne me nauyi yayi awon gaba da ita,yayin da Farhan yasasu agaba yana gadinsu,aransa yana ayyana irin Kulawar da yake mafarkin basu.

Ba Safna ce ta farka ba seda asuba,koda ta farka,Farhan bayanan yaje masallaci,Dan haka da sauri ta mike dauke da danta ta fice daga sashin.

Koda taje daki,wanka tafarayi,sabida gaba daya karnin nonon takeyi. Sannan tayiwa junior, ta kimtsa shi,itama ta kimtsa,Akwatin kayansu ta janyo,ta zuba musu kayansu aciki ta zuge,sannan tasa hijab dinta, taja akwatin cikin sanda ta fice daga dakinta.

Dan tasha alwashin gwanda ta koma kauyensu data bari Farhan ya raba ta da danta tanaji tana gani.

Sede cikin rashin saa tana isowa falon gidan Farhan na shigowa daga masallaci.

Tsayawa yayi kikam yana kallonta, itama shi take kallo, cikin tsoro da firgici.

Shi kanshi Farhan din ya tsorata da ganin shirin nata na son guduwa,amma haka yay ta maza yace cikin daurewar fuska.

"Ina kuma zakije min da da,da sanyin safiyarnan?"

Murguda baki tayi sannan ta kauda kai gefe tace"nima ay danane garinmu kuma zan tafi dashi".

"Da izinin wa?"ya wurgo mata tambayar.

"Izini kuma?to da izinina"ta bashi amsa lokacin da take rike kugunta.

"To ban amince ki fitar min da yaro ba,amma ke zaki iya tafiya,bazan hanaki ba"cewar Farhan yana kare mata kallo.

"Zancan kake so"tace sannan ta kada kanta,ta yi hanyar fita.

"Ikon da kike nunawa akan yaronnan na alamta min kamar ba nine ubansa ba,tunda yana da wani uban bayan ni zaki iya tafiya dashi danki ne"

Chak taja ta tsaya,sannan ta waigo a firgice tace,"bangane ba,nufinka ba danka bane?"

"Kwarai kuwa,tunda da da nane duk dokar da zansa akan sa zata zauna ay ayki da ita,to kinsan ba nawa bane shiyasa kike zubar da duk dokar danasa akansa"cewar Farhan cikin daurewar fuska.

Da gudu ta runtumo gabanshi,ta kwanto junior tana mika masa tace,cikin kuka"nasha wahala gun Neman ubansa,gori da zagi duk anmin akan Neman mahaifinsa,Don Allah karka musanya farincikin ganin mahaifinsa da nayi da bakin ciki,junior danka ne,ko baka ga kuna kama ba"

Murmushi yayi yasa hannu ya riko junior din hade da hannayenta yace cikin siririyar murya wacce ita kadai taji me yace.

"Rigimarki na burgeni Safna, kidena tsiwa,kar wataran kisa nai miki duka"

Murmushi ta tsinci kanta da yi masa tai kasa da kanta.

Amsar junior din yayi,ya lakace mata hanci yabar gurin dauke da Dan sa .

Bin bayan shi tayi da kallo,aranta tace "ni ban taba ganin farar fata me she gen iyayi irinshi ba,komai se yayi iyayi,"

Muje zuwa

Surbajo for life.
11/14/21, 12:49 PM - MY MTN 2: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*AURE DA HAIHUWA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀

*Zahra Surbajo*

*27*

Ba Farhan ba hatta Taufeeq mikewa yayi yana kallonsu,Dan gaba daya Kansu ya kulle.

Safna da gudu ta karasa jikin doctor Amina,ta rungume ta sannan ta rushe da kuka, Wanda tun bayan rabuwarta da Rayhan batayi irinshi ba.

Cikin kuka Safna ke fadin"doctor gaba daya rayuwata ta lalace sanadin wannan cikin,gashi na haihu har yanzu ba wani sauyi,kitaimakeni ki nemo uban dannan in bashi abunshi na huta,doctor nagaji"ta karasa maganar cikin matsanancin kuka.

Doctor Amina wacce itama kukan take,ahankali ta dago Safna daga jikinta,sannan tasa hannu ta amshi Farhan junior, daga hannunta ta bude fuskarshi ta kalla,wasu hawayen suka sake biyo fuskarta,yayin da murmushi ya mamaye fuskarta.

Dagowa tayi ta kalli Safna dake ta faman risgar kuka,tace"kuka ya kare Safna,uban danki na tare dake yanzu haka,akan nemanki,ni dashi ba irin wahalar da bamu sha ba,amma yanzu tazama labari"

Cikin rashin fahimta,Safna ke kallon doctor, alamun bata fahimceta ba.

Murmushi tai mata sannan taja hannunta zuwa gaban Farhan dake tsaye kikam,cikin rashin fahimta.

Suna zuwa gabanshi,ta miko masa Farhan junior, fuskarta dauke da murmushi tace"Bayan tsayin lokacin nema da cigiya,bayan yawan salloli,da sadaka,yau Allah ya amshi rokonmu,ya hadamu da safna Farhan ina me gabatar da danka a gareka"ta karasa mika masa yaron.

Baki da jikin Farhan gaba daya rawa yakeyi,hannunsa na karkarwa ya amshi Farhan junior, yana duban doctor Amina hawaye na bin idonsa, yace cikin dabarbarcewa
"Doctor ni dake akwai amana,wasa makamancin wannan be taba shiga tsakaninmu ba,da gaske kike wannan gudan jinina ne?"ya wurga mata tambayar yana kara kankame Farhan junior ajikinshi.

"Jininka ne Farhan, ko tantama babu"cewar doctor Amina tana murmushi.
Chapter 11 · 0% Book details