← Book details Abdurrahim Matukin Jirgin Ruwa Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 18

Sashe 8

Abdurrahim Matukin Jirgin Ruwa Complete Hausa Novel · about 8 min read

Na'ima zaune take tana shan sauran tea d'in da yarage dakyar ma take shan tea d'in sabo da ya huce.
Alheri ko da ya ke tana da key d'in gidan Abdurrahim yasa tana zuwa ta bud'e ta shiga zaune ta iske Na'ima tana shan tea abin ta. "Keee alheri ta kira sunanta da gurb'atacciyar hausar ta ta ce"Wayasaka kasa wannan rigar? " Shiru Na'ima ta yi dan ba ta san amsar da zata ba ta ba.
Alheri jin Na'ima tayi shiru ta kuma cewa"Kai na ce ubanwa ya saka kasa wannan rigar? " Na'ima da duk ta gama daburcewa sai cewa tayi"Shima ya ganni da ita rannan bai ce ko mai ba kuma d...... " Marin da alheri ta wankama Na'ima ne ya hanata k'asara abin da tayi niyyar fad'a cikin tsantsar b'acin rai Na'ima ta ta shi rik'e da kunci ta ce"Bai war Allah mai ne miki zaki maran ko shima mairigar da ya ganni da ita ai bai cimin komai ba" Na mare ka dan ubanka" cewar alheri.
Na'ima ko cikin jin zafin zagin mahaifinta da akayi ta ce" ka da ki sake zagar min ubana yana kabari" Uban ka na ce na ce ubanka-ubanka" wani uban kukan kura Na'ima ta yi ta afka ma alheri, da ya ke alheri irin manyamanyan matan nan ce Wanda zaka gansu ga tsawo ga k'iba yasa ta rik'e Na'ima tai ta duka ,da taga abin bai ma ta ba shak'eta ta yi ta ce"Dan ubanka ya ka ke da Abdurrahim?"Ba dai ubana ba" cewar Na'ima.
Janta alheri ta ci gaba dayi ta ce"Inda bazaka fad'amin yadda kake da Abdurrahim ba, tom yanzun nan zakabar gidan nan dan ubanka" janta alheri tai ta yi har zuwa hanyar fita falon, Na'ima kuma sai cijewa take da d'an k'aramin k'arfin ta.Alheri ta ce"Dan ubanka gidan na ubanka ne Da bazaka fita ba? " ke ma gidan ai ba na ubanki ba ne"Ai alheri jin Na'ima ta zageta itama rud'ewa tayi tai ta bugun Na'ima tun k'arfin ta.

Abdurrahim ko yana can gidan alheri yana jiranta ta dawo, da ya ji shirun yayi yawa kiranta yayi awaya amma bata d'auka ba,rufe mata gidan ta ya yi Shikuma ya yo gida. Tun kafin ya gama parking motar sa yake jin hayaniya da saurinsa ya k'araso cikin gidan alheri ya iske tana tura Na'ima waje had'e da kai mata duka, tana sai ta fita inda gidan bana ubanta bane, ita kuma tana cijewa tana cewa bazata fita ba inda gidan banata ba ne.
Wata uwar tsawa Abdurrahim ya bugama alheri ya ce"Wa ya saki? " Alheri ko da ranta ya b'ace jin abin da Abdurrahim yace mata ta ce" Haka zaka cemin ko wayasani ,tom na rantse da d'unbun son da na ke ma yau sai ta b'ar gidan nan ,waya ce ma yasa ma ka riga" da ya ke haka take hausarta namiji ta mai dashi mace mace ta mai da ta namiji, itako Na'ima ta rakub'e gefe bak'inciki yasa sai kuka take yi, alheri kuma nuna Na'ima tayi da ke kuka ta ce"Kab'ar gidan nan nace" Allah sarki Na'ima ko kallanta batayi ba taci gaba da kukan ta, tun kud'ata alheri tayi tun karfinta Na'ima sai da ta bugu da get d'in dake gidan sannan tatafi taga-taga kamar zata fad'i wani k'arfe da ke kusa da Na'ima Na'ima ta d'auka ta yi kan alheri da shi alheri da taga bata da wani abu da zata kare kanta rugawa tayi sai dai duk inda tayi Na'ima binta take yi da gudunta ita ala dole sai ta bugamata alheri shi. ihu alheri ke yi Na'ima ko bata fasa bin ta ba. Abdurrahim da yaga indai ya kyalesu Na'ima zatai ma alheri rauni indai ta bugamata ,dai-dai ko Abdurrahim zai amse k'arfan Allah yaba Na'ima sa'a ta bugama alheri shi, dan ma Allah yasa ahannu ta same ta ba akai ba, wata uwar k'ara alheri ta yi ta zuk'unna agun tana rirrik'e hannun ta re da alkawarin sai taci uban Na'ima.
Da kyar Abdurrahim ya lallabi alheri ta tafi gida, ita kuma Na'ima tana ganin wucewar alheri ta kama hanya zata koma gidan hannu Abdurrahim yad'aga mata ya ce"Kar ki sa ke ki koma min gida" ya na kai wa nan ya shige ya b'arta agun.

Waiwaiye adon tafiya inji Hausawa,can kaduna ko gwaggo jerawa su kai da Mariya mahaifiyar Na'ima har'gidan da Na'ima take aiki kasan cewar me gadin ya gane gwaggo yasa ya barsu suka shiga kai tsaye, alokacin Hajiya Rahina tana waya da k'awarta Hajiya Suwaiba matar da gwaggo ke aiki a gidan ta,Hajiya Rahina ganin su gwaggo najiranta yasa ta katse wayar ta cema Hajiya suwaiba zata kirata anjima tayi bak'i ,sannan ta juya tana kallan su gwaggo ta ce " sannun ku da zuwa gwaggo" nan dai suka gama gaggaisawa, sannan gwaggo ta kalli Hajiya Rahina ta ce"Hajiya wannan da kike gani ita ce mahaifiyar Na'ima, na kawota ne in fad'amata yadda mukayi da Na'ima agabanki dan kar'ta zargan da cin amanar yarinyar ta" gwaggo ta ci gaba da cewa"Mariya bayan kin zo kinsanar da kina son Na'ima ta dawo gida sabo da auran da aka d'aura mata, tabbas agabanki Na'ima bata nuna komai ba, tom ammafa bayan kin tafi ga Hajiya nan itace sheda, Na'ima ta zauna sai rusamana kuka take tana rokan Hajiya akan dan Allah kasar da za'a d'akko ma Hajiya kaya za ai tafiyar dogon zango ta roki hajiya aje da ita wai kafin lokacin k'ila asamu mafita dan ita bazata auri mutumin da mahaifinta yabar wasiyar kar ta aura ba, hajiya tace ma Na'ima ita bazata d'auketa ba ta kai ta doguwar tafiya batare da amincewar ko wa na ta ba, sai dai ta fad'a ma mahaifiyar ta in ta amince, Mariya in tak'aicemiki magana Na'ima tazo tasamin kuka akan sai dai in amince aitafiyar da ita. Tom Allah yasani tausayin Na'ima yasani amincewa ,kin ji yadda akayi wallahi"

Kiran da akaima Hajiya Rahina ne awaya yahana mahaifiyar Na'ima magana, cikin furgici Hajiya Rahina ta tashi tsaye ta ce"Accident , kana nufin jirgin ruwan da ya d'akko kayan mu yayi accident?" Banji me akacemata ba daga can b'angaran naji tana cewa"Innalillahi'wa ina ilaihirraj'un, kana nufin ba aga Na'ima ba?" kashe wayar Hajiya Rahina tayi ta dafe kai tana karanto duk addu'ar da tazo bakinta.

Tun kafin Hajiya Rahina tayi masu gwaggo k'arin bayani suka fahimci duk abinda yafaru.

Kuka mahaifiyar Na'ima takeyi sosai tana fad'in "Allah sarki Na'ima ashe haduwar da mukayi itace ganawar mu tak'arshe"

Dukkansu Sunyi kukan su san rai dan bamai ba wani hak'uri, sai da mijin Hajiya Rahina ya dawo yayi masu nasiha akan shi komai da kuka gani muk'addarine daga Allah tunrar gini tunrar zane, nan dai alhaji yayi ta masu nasiha har Allah yasa jikinsu duka yayi sanyi bakamar maman Na'ima ba, saidai ita kad'ai tasan irin rad'adin da takeji acan k'asan zuciyar ta, Alhaji da kan shi yad'auki mama amotar sa shida Hajiya Rahina da gwaggo suka rakata har gida, bayan sun isa ne Alhaji yak'arayima ma mahaifiyar Na'ima nasiha sosai, sannan yaciro kud'i masu yawa yabata.

Kafin kace me mutuwar Na'ima takauraye duka sabon yalwa, koda labarin mutuwar ya isa kunnan dan gin baban ta, har gida su ka je sukacima mama mutumci sannan suka ce mata sunanan suna jiran dawowar Na'ima duk inda ta kaita," k'aryar banza in mutuwa ta yi dagaske kamar yadda ki ka ce ina gawar ta? " Cewar jimmai mahaifiyar gali Wanda aka d'aura auran sa da Na'ima.

Can b'angaran Na'ima ko tana ganin Abdurrahim yayi shigewar sa cikin gidansa ta na kuka ta fita daga gidan..........

🛥️ ABDURRAHIM🛥️
MATUK'IN JIRGIN RUWA NE.

🔔📚
*JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚*

Na
Fadila Sani Bakori.

Wannan shafin gaba d'ayanshi na sadaukar da shi ga 'yar'uwata barrister Hassana Sani,Allah ya taimakeki yabada sa'ar jarabawa🙏🏻🙏🏻

Page 16 & 17.

Na'ima ko da ta fita daga gidan ja tai ta tsaya tana kuka dan bata san inda zata ba gashi duk inda zata waiga masu ja-ja yan kunne kawai take gani suma jefi-jefi turawa kenan.

Na'ima na nanan tsaye sai ga wani bak'in kare yana kewaye unguwar yana zaro harshe, duk dare Wannan karan shike gadin unguwar, Na'ima ganin karan nan na tunkarota yasa tafara ja da baya ganin karan da gaske gunta ya yo yasa ta juya ta shige gidan Abdurrahim da gudunta, tana shiga taja k'ofar ta rufe, amma duk da haka jikinta be dai na rawa ba dan ta matuk'ar tsorata da karan, cikin tsoro Na'ima ta samu can gefe agidan ta rakub'e tana mai addu'ar da duk tazo bakinta. Na'ima na nan zaune agun har wani wahalallan bacci ya kwasheta.

Can b'angaran Abdurrahim ko sai bayan ya shiga gida ya ke jin abin da yayi ma Na'ima bai kyauta ba dan dagagani yarinyar batasan inda zata ba, "Tom ai garama da yayi mata haka dan yarinyar tana bashi haushi gashi tak'i fad'a mai dalilin zuwanta garin "Tofa in ban da abin ka Abdurrahim ba sai ka tambaye ta zata fad'ama ba"inji wani tunanin nashi kenan.

Abdurrahim tunawa da yayi be rufe gida ba ne yasa ya tashi ya nufi wajan get d'in dan rufe gidan, torch light d'in wayarshi ya haska ya rufe gidan dan shi daga dare yayi Yake kashe hasken gidan.Bayan ya rufe gidan ne ya juyo sai ya ga abu kamar mutum ya k'udindine awaje d'aya kusan mutuk'an jirgin ruwa basu da tsoro k'arasawa wajan yayi amma abin mamaki Na'ima ya gani kwance agun ta k'udindine jikinta tana barci abun ta.
Bak'aramin tausai Na'ima ta ba Abdurrahim ba ji ya yi tausayinta gaba d'aya ya cika zuciyarshi.
Abdurrahim ya dad'e atsaye akan Na'ima sannan ya lallab'a yadda ba zata tashi ba ya d'akko ta kamar k'aramar baby ya yi cikin gidan da ita, d'akinta ya kwantar da ita ya ja blanket ya rufe ta sannan ya je d'akin shi shi ma ya kwanta.
Chapter 8 · 0% Book details