Sashe 4
Abdurrahim Matukin Jirgin Ruwa Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Tashi ki k'arya dan yanzu zaku Kama hanya, Amma fa zakiyi doguwar tafiya ,dan Allah in tambaye ki mana?"Jamilu ya tambayi Na'ima.
"Ina jinka"cewar Na'ima.
"Dan Allah me yajawo miki wan nan wahalar haka?".
Na'ima kallan Jamilu tayi
da mamaki akan fuskarta ta ce "Wahala kuma tame fa?".
"Ta tafiya a jirgin ruwa mana, waya fad'a maki su kaya dole sai an tsare su, ai daga anba direbobin shike nan, ba sai an had'a da mai tsaron kaya ba",Jamilu ya fad'a.
"Tom nima sha'awar tafiyar ce kawai" Na'ima ta fad'a ma Jamilu haka ne kawai dan ta wuce maganar.
Na'ima da Jamilu tsaye suna sallama dan yanzu jirgin su zai kama hanya. Jamilu kallan Na'ima yayi ya ce,
"Tom shikenan Na'imatu Allah ya isomana dake lafiya, Allah ya karemana ke gaba da baya".
"Ameen "ta amsa.
Jamil bashi yabar gurin ba har sai da yaga jirgin su ya tashi sannan.
Can b'angaran Mahaifiyar Na'ima kuwa bayan ta koma gida, tun tanasaran zuwan Na'ima har ta gaji, har ta fara tunanin k'ila hajiyar ce bata dawo ba sai gobe, tom Allah yasa dai goban ma tazo da wuri, kafin guyababbun Iyayanta su zo.
Washe gari ma haka ya faru ba Na'ima ba dalilinta, Mahaifiyar Na'ima ganin har rana tayi Na'ima bata dawo ba abin sai ya fara bata tsoro, dan tasan tun da tacema Na'ima tadawo tom ba'abinda zai hanata da wowa. "Tom ko dai an sace tane" Haka Mahaifiyar Na'ima tai ta tik'a da warwara akan rashin dawowar Na'imar.
Mahaifiyar Na'ima nanan kwance tana tunanin rashin dawowar Na'ima tajiyo sallamar su Ya'u ,cikin kid'ima Mahaifiyar Na'ima ta fito da tab'arma a hannunta tana k'ok'arin shimfid'amu su , Ya'u ne yad'aga mata hannu ya ce.
"Dakata Mariya,bazama ya kawo mu ba, mun zo ne kibamu 'yarmu kuma matar d'an mu ko kuma wallahi Mariya hukuma zata rabamu da ke".
"Wallahi! Wallhi!! Wallhi!!!" Sonawa narantse Ya'u?" Cewar Jimmai.
"Sau uku, yaya jimmai".
Kai Jimmai ta karkad'a ta ce,
"Wannan shine gargad'i nak'arshe Mariya, ki fitomin da surukata in kuma bahakaba tom zaki san ruwa ba tsaran kwando bane Wallahi"Tana kai wa nan tai gaba.
Ya'u kusa da Mahaifiyar Na'ima yadawo ya ce ahankali yadda Jimmai bazataji ba"Mariya ni zan tai makeki,inma baki son auran Na'imar ne, amma sai da sharad'in in kin aminta zaki auran?".
Wani mugun kallo mahaifiyar Na'ima tayi mai ta ce "Ba aure atsakanina da kai amma ba abin mamaki bane dan ka fad'i haka inda nasan akwai k'arancin rashin sani atattare da kai".
"Kamarya Mariya bangane ba,me kuma ya kawo rashin sani anan? "
"Nufina bakasan haramun ba bakasan halaliiba".
"Haba Mariya mai Ya kawo maganar haramun kuma da halali ana.... ".
Maganar Jimmai da Ya'u yaji ce tasa ya canza abinda yayi niyar fad'a tahan yar cewa "kin ji dai abinda nace maki kinada damar samun mafita, in kinyarda in kuma kink'i tom ya rage naki"Yana kai wa nan yayi gaba abinsa.
washe gari da sassafe mahaifiyar Na'ima ta nufi kaduna, sakamakon wani munmunan mafarki da tayi akan Na'ima.
Gidan gwaggo Mahaifiyar Na'ima ta sauka.
Cikin gwaggo sai da ya kad'a dan ganin mahaifiyar Na'ima da tayi, dan bata san abinda zata ce mata ba game da tafiyar da Na'ima tayi bada izinin taba, haka ma fa na d'aukar mata yarinya na kaita gidan aiki bada sanin taba,kuma koda tazo bata nunamata damuwa ba, ai ko yanzu da kunya in ce mata bata k'asar, tom inama zance mata taje. Haka gwaggo tai ta maganar zuci.
Muryar mahaifiyar Na'ima ce ta dawo da gwaggo daga tunanin da ta lula.
"Gwaggo ki yi hak'uri karkiga nadaimeki da sintiri ,wallahi abubuwane ne sun kacamemin gashi itama Na'imar da nace tayi hak'uri tazo a kaita d'akin mijin ta shine tak'i zuwa, ni hattasani ma afargaba, na fara tunanin ko lafiya"
"Lafiya"cewar gwaggo da batasan ma abinda ta ce ba.
"Alhamdulillah ,dama wani mafarkine nayi akan Na'imar mai ban tsoro, shine nazo ingani ko lafiya, daga nan kuma k'afarta-k'afata".
Wani irin kuka cikin gwaggo ya yi, cikin rashin sanin abinda zatace ma ta ta ce "Tom tashi mu je gidan da take aikin".
B'angaran Na'ima kuwa al'ajabi duk ya isheta wai yau ita ce acikin jirgin ruwa.
Su Na'ima ba su yi tafiya mai nisa ba,suka farajin
Wani irin k'ara daga k'asan jirgin kamar ana balla Abu, cikin kid'ima captain d'in jirgin ya fara sanarwa jirgi yasamu matsala, kafin kace wani abu, jirgin yafara mangar-mangar.
Na'ima kuka tafarayi ganin ruwa yafara tud'ad'owa cikin jirgin.
Ahankali ahankali jirgin yafara k'asa ruwa yana k'ara shigowa cikin jirgin sosai kamar ana k'ara antayo shi.........
🛥️ ABDURRAHIM 🛥️
MATUK'IN JIRGIN RUW NE (RENEW)
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚*
Na
Fadila Sani Bakori.
Page 8 & 9
Banda salati da kuka ba'abinda Na'ima ke iya yi.
Shugaban jirgin ruwan, (captain) ya bada rigar ruwa (life jacket) ya ce
Aba duk matan dake jirgin su sa,sannan ya k'ara da cewa"mu na so dan Allah kowa ya kwantar da hankalin sa, ba abinda zai faru dan mun kai sanarwa (report) ababbar headquarter ta mu, za akawomana agaji yanzun nan" cewar captain d'in jirgin.
Duk maganar da yake cikin speaker yake yinta, in bahaka ba ba kowa zai ji shi ba, dan jirgin nada girma sosai balefi.
Bak'aramin razana mutanan dake cikin jirgin nan su kayiba, ganin jirgin nasu saura k'iris ya nutse, gashi har yanzu basuga alamun masu ceto ba.
Shikan shi captain d'in jirgin yagama sadak'arwa.
B'ak'aramin rud'ani captain d'in ya shigaba, ganin b'angaran matuk'an masu control d'in jirgin gabad'ayan shi ya nutse cikin ruwan .
Gudu mutanan kusa da b'angaran da ya rufta suketayi suna dawowa b'angaran da yake da dama -dama.
Allah sarki kusan baka ganin mutane sai kawu nan su kakegani.
Bindiga carptin d'in ya sa ya harbi kan shi, dan ba zai jure ganin ruftawar jirgin gabad'aya ba.
Rabin jirgin duk ya nutse, duk wata hayaniya da mutane ke yi duk sun baryi, banda mutun uku daga cikin matuk'an jirgin da su kai saura, duk dasu tsabar amanace irin ta su ta turawa, amma su sun iya ruwan da zasu iya taimakon kansu, tom amma su turawa sunada amana duk runtsi duk wuya sai dai amutu tare badai su gudu ba, dan duk sun iya ruwa sannan ga rigar ruwa amma sai sukak'isawa suka ba matan sukasa. Allah sarki su kansu mutum ukun da su kai saura sunriga sun gama galabaita suna ji suna gani haka suka sadaukar da rayuwar su, tsabar alk'awari irin nasu, Mutum d'aya ne da shima yagama galabaita, hannu yake ta d'agawa sakamakon k'arar jirgin da yake ji yana nufo su, dan ko ba afad'a ba yasan su akakawo ma agaji.
Jin jirgin nata shawagi yasa ya lalibo usir d'insa yahura yasan k'arar zata ankarar da su dan yasan sakamakom ruwan da yasha kansu ne yahana masu kawo masu agajin sugan su.Tun k'arfin shi yahura usir din.
D'aya daga cikin masu kawo agajin ne yajiyo k'arar husird'in,
nuna ma sauran abokan tafiyar ya yi inda yajiyo k'arar .
Da saurin su su ka k'araso in da su ke ji yo k'arar hura usir d'in.
Shiko Azera da yajiyo alamun tahowar su cigaba da hura usir d'in yayi yana bubbuga hannun shi aruwan da d'an sauran k'arfin da yarage mai.
ta ke suka gane inda al'amarin yafaru, suka k'arasa wajan.
Cikin ikon Allah su kai ta fito da mutane daga cikin jirgin da had'arin yafaru, basuyi wani wahalar fito da mutanan ba, k'asan cewar yawancin matan duk asaman ruwa suke, saboda rigar ruwa da akabasu sukasa .
Sun d'au dogon lokaci suna fito da mutane acikin ruwan, inda duk Wanda aka ciro asibiti ake wucewa da su.
Ikon Allah duk iya sa idona danayi banga Na'ima ba cikin muta nan da aka ciro, har suka gama cirowa, ban ga alamu da sauran mutum ba, dan har na'urorin su saida suka haska basuga komai ba, sannan suka nufi da wa inda aka ciro asibiti.
Tafe yake cikin d'an ma dai-dai cin jirjin sa. Matashi wanda kallo d'aya zakai mai ka tabbatar da kwanciyar hankalin ya wadatai, dan dagani ba sai an fad'aba kallo d'aya za kai mai kagane hakan, Sauri yake yak'osa yaje gida saboda uzirin da yake da shi agidan, wani tudu-tudu yake gani na tun karo shi da alama koma meye igiyar ruwa ce ta jawo shi.
Tun kafin abun ya iso kusa da shi ya tabbatar da mutun ne, parking ya yi da jirgin nasa acikin ruwan, sannan yasa wata sanda dake cikin jirgin yarika jawo abun nan ahankali, sai dai tun kafin ya iso wajan shi ya tabbatar da mutum ne, dan yaga rigar ruwa ajikin mutum d'in ,shi ne dalilin da yasa bai nutseba acikin ruwan.
Cikin jirgin sa ya sata sannan ya tub'e mata rigar ruwan da ke jikin ta.
Al'ajabi ne ya isheshi ya ce " ikon Allah tom wannan kuma daga ina mutum cikin ruwa kuma mace"
Tafiya yake yana sake- saken yadda zai yi da ita, kai ko dai in yadda ta ne, tom in kuma fa nayadda ta kuma bata mutu ba fa?"
Nan dai ya yanke ma kan shi shawara akan ya kai ta gidansa alabashi yakira alheri ta dubata ta tagani ko tanada rai.
Bashi ya isa gida ba sai shida na yamma (6: 00pm) lokacin garin yafara duhu.
Yana shiga gidan ya d'akko ta daga mota kasan cewar yana fita gab'ar ruwan yayi parking a inda suke aje jiragan su. Ya d'auki drop d'in mota har gidan sa."
Bayan ya kwantar da ita ne nalura she Na'ima ce.
Waya ya d'auka ya turama alheri sako tazo yanzu yana son ganin ta.
Cikin mintina kad'an alheri ta iso gidan.
Alheri kallan shi tayi damamki ta ce,
"Abdurrahim wannan fa, ina kasamota?. "
Banza Abdurrahim yayi da ita kamar bazai amsa mata ba, sannan ya ce ahankali kamar an mai dole "Tsintarta nayi, ki dubata mana"
Alheri da mamaki take kallan Abdurrahim , so take tak'ara tambayar shi amma bataga fuskar hakan ba, dan haka taja bakin ta tayi shiru, ta fara aikin da yakawota.
Alheri tad'an kwashi mintina tana dubata, sannan takalli Abdurrahim ta ce,
"Abdurrahim k'alau take inajin furgicin da tayi ne yasata cikin wannan yanayin amma bari ina zuwa akwai allurar da zan mata yanzu.
"Ina jinka"cewar Na'ima.
"Dan Allah me yajawo miki wan nan wahalar haka?".
Na'ima kallan Jamilu tayi
da mamaki akan fuskarta ta ce "Wahala kuma tame fa?".
"Ta tafiya a jirgin ruwa mana, waya fad'a maki su kaya dole sai an tsare su, ai daga anba direbobin shike nan, ba sai an had'a da mai tsaron kaya ba",Jamilu ya fad'a.
"Tom nima sha'awar tafiyar ce kawai" Na'ima ta fad'a ma Jamilu haka ne kawai dan ta wuce maganar.
Na'ima da Jamilu tsaye suna sallama dan yanzu jirgin su zai kama hanya. Jamilu kallan Na'ima yayi ya ce,
"Tom shikenan Na'imatu Allah ya isomana dake lafiya, Allah ya karemana ke gaba da baya".
"Ameen "ta amsa.
Jamil bashi yabar gurin ba har sai da yaga jirgin su ya tashi sannan.
Can b'angaran Mahaifiyar Na'ima kuwa bayan ta koma gida, tun tanasaran zuwan Na'ima har ta gaji, har ta fara tunanin k'ila hajiyar ce bata dawo ba sai gobe, tom Allah yasa dai goban ma tazo da wuri, kafin guyababbun Iyayanta su zo.
Washe gari ma haka ya faru ba Na'ima ba dalilinta, Mahaifiyar Na'ima ganin har rana tayi Na'ima bata dawo ba abin sai ya fara bata tsoro, dan tasan tun da tacema Na'ima tadawo tom ba'abinda zai hanata da wowa. "Tom ko dai an sace tane" Haka Mahaifiyar Na'ima tai ta tik'a da warwara akan rashin dawowar Na'imar.
Mahaifiyar Na'ima nanan kwance tana tunanin rashin dawowar Na'ima tajiyo sallamar su Ya'u ,cikin kid'ima Mahaifiyar Na'ima ta fito da tab'arma a hannunta tana k'ok'arin shimfid'amu su , Ya'u ne yad'aga mata hannu ya ce.
"Dakata Mariya,bazama ya kawo mu ba, mun zo ne kibamu 'yarmu kuma matar d'an mu ko kuma wallahi Mariya hukuma zata rabamu da ke".
"Wallahi! Wallhi!! Wallhi!!!" Sonawa narantse Ya'u?" Cewar Jimmai.
"Sau uku, yaya jimmai".
Kai Jimmai ta karkad'a ta ce,
"Wannan shine gargad'i nak'arshe Mariya, ki fitomin da surukata in kuma bahakaba tom zaki san ruwa ba tsaran kwando bane Wallahi"Tana kai wa nan tai gaba.
Ya'u kusa da Mahaifiyar Na'ima yadawo ya ce ahankali yadda Jimmai bazataji ba"Mariya ni zan tai makeki,inma baki son auran Na'imar ne, amma sai da sharad'in in kin aminta zaki auran?".
Wani mugun kallo mahaifiyar Na'ima tayi mai ta ce "Ba aure atsakanina da kai amma ba abin mamaki bane dan ka fad'i haka inda nasan akwai k'arancin rashin sani atattare da kai".
"Kamarya Mariya bangane ba,me kuma ya kawo rashin sani anan? "
"Nufina bakasan haramun ba bakasan halaliiba".
"Haba Mariya mai Ya kawo maganar haramun kuma da halali ana.... ".
Maganar Jimmai da Ya'u yaji ce tasa ya canza abinda yayi niyar fad'a tahan yar cewa "kin ji dai abinda nace maki kinada damar samun mafita, in kinyarda in kuma kink'i tom ya rage naki"Yana kai wa nan yayi gaba abinsa.
washe gari da sassafe mahaifiyar Na'ima ta nufi kaduna, sakamakon wani munmunan mafarki da tayi akan Na'ima.
Gidan gwaggo Mahaifiyar Na'ima ta sauka.
Cikin gwaggo sai da ya kad'a dan ganin mahaifiyar Na'ima da tayi, dan bata san abinda zata ce mata ba game da tafiyar da Na'ima tayi bada izinin taba, haka ma fa na d'aukar mata yarinya na kaita gidan aiki bada sanin taba,kuma koda tazo bata nunamata damuwa ba, ai ko yanzu da kunya in ce mata bata k'asar, tom inama zance mata taje. Haka gwaggo tai ta maganar zuci.
Muryar mahaifiyar Na'ima ce ta dawo da gwaggo daga tunanin da ta lula.
"Gwaggo ki yi hak'uri karkiga nadaimeki da sintiri ,wallahi abubuwane ne sun kacamemin gashi itama Na'imar da nace tayi hak'uri tazo a kaita d'akin mijin ta shine tak'i zuwa, ni hattasani ma afargaba, na fara tunanin ko lafiya"
"Lafiya"cewar gwaggo da batasan ma abinda ta ce ba.
"Alhamdulillah ,dama wani mafarkine nayi akan Na'imar mai ban tsoro, shine nazo ingani ko lafiya, daga nan kuma k'afarta-k'afata".
Wani irin kuka cikin gwaggo ya yi, cikin rashin sanin abinda zatace ma ta ta ce "Tom tashi mu je gidan da take aikin".
B'angaran Na'ima kuwa al'ajabi duk ya isheta wai yau ita ce acikin jirgin ruwa.
Su Na'ima ba su yi tafiya mai nisa ba,suka farajin
Wani irin k'ara daga k'asan jirgin kamar ana balla Abu, cikin kid'ima captain d'in jirgin ya fara sanarwa jirgi yasamu matsala, kafin kace wani abu, jirgin yafara mangar-mangar.
Na'ima kuka tafarayi ganin ruwa yafara tud'ad'owa cikin jirgin.
Ahankali ahankali jirgin yafara k'asa ruwa yana k'ara shigowa cikin jirgin sosai kamar ana k'ara antayo shi.........
🛥️ ABDURRAHIM 🛥️
MATUK'IN JIRGIN RUW NE (RENEW)
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚*
Na
Fadila Sani Bakori.
Page 8 & 9
Banda salati da kuka ba'abinda Na'ima ke iya yi.
Shugaban jirgin ruwan, (captain) ya bada rigar ruwa (life jacket) ya ce
Aba duk matan dake jirgin su sa,sannan ya k'ara da cewa"mu na so dan Allah kowa ya kwantar da hankalin sa, ba abinda zai faru dan mun kai sanarwa (report) ababbar headquarter ta mu, za akawomana agaji yanzun nan" cewar captain d'in jirgin.
Duk maganar da yake cikin speaker yake yinta, in bahaka ba ba kowa zai ji shi ba, dan jirgin nada girma sosai balefi.
Bak'aramin razana mutanan dake cikin jirgin nan su kayiba, ganin jirgin nasu saura k'iris ya nutse, gashi har yanzu basuga alamun masu ceto ba.
Shikan shi captain d'in jirgin yagama sadak'arwa.
B'ak'aramin rud'ani captain d'in ya shigaba, ganin b'angaran matuk'an masu control d'in jirgin gabad'ayan shi ya nutse cikin ruwan .
Gudu mutanan kusa da b'angaran da ya rufta suketayi suna dawowa b'angaran da yake da dama -dama.
Allah sarki kusan baka ganin mutane sai kawu nan su kakegani.
Bindiga carptin d'in ya sa ya harbi kan shi, dan ba zai jure ganin ruftawar jirgin gabad'aya ba.
Rabin jirgin duk ya nutse, duk wata hayaniya da mutane ke yi duk sun baryi, banda mutun uku daga cikin matuk'an jirgin da su kai saura, duk dasu tsabar amanace irin ta su ta turawa, amma su sun iya ruwan da zasu iya taimakon kansu, tom amma su turawa sunada amana duk runtsi duk wuya sai dai amutu tare badai su gudu ba, dan duk sun iya ruwa sannan ga rigar ruwa amma sai sukak'isawa suka ba matan sukasa. Allah sarki su kansu mutum ukun da su kai saura sunriga sun gama galabaita suna ji suna gani haka suka sadaukar da rayuwar su, tsabar alk'awari irin nasu, Mutum d'aya ne da shima yagama galabaita, hannu yake ta d'agawa sakamakon k'arar jirgin da yake ji yana nufo su, dan ko ba afad'a ba yasan su akakawo ma agaji.
Jin jirgin nata shawagi yasa ya lalibo usir d'insa yahura yasan k'arar zata ankarar da su dan yasan sakamakom ruwan da yasha kansu ne yahana masu kawo masu agajin sugan su.Tun k'arfin shi yahura usir din.
D'aya daga cikin masu kawo agajin ne yajiyo k'arar husird'in,
nuna ma sauran abokan tafiyar ya yi inda yajiyo k'arar .
Da saurin su su ka k'araso in da su ke ji yo k'arar hura usir d'in.
Shiko Azera da yajiyo alamun tahowar su cigaba da hura usir d'in yayi yana bubbuga hannun shi aruwan da d'an sauran k'arfin da yarage mai.
ta ke suka gane inda al'amarin yafaru, suka k'arasa wajan.
Cikin ikon Allah su kai ta fito da mutane daga cikin jirgin da had'arin yafaru, basuyi wani wahalar fito da mutanan ba, k'asan cewar yawancin matan duk asaman ruwa suke, saboda rigar ruwa da akabasu sukasa .
Sun d'au dogon lokaci suna fito da mutane acikin ruwan, inda duk Wanda aka ciro asibiti ake wucewa da su.
Ikon Allah duk iya sa idona danayi banga Na'ima ba cikin muta nan da aka ciro, har suka gama cirowa, ban ga alamu da sauran mutum ba, dan har na'urorin su saida suka haska basuga komai ba, sannan suka nufi da wa inda aka ciro asibiti.
Tafe yake cikin d'an ma dai-dai cin jirjin sa. Matashi wanda kallo d'aya zakai mai ka tabbatar da kwanciyar hankalin ya wadatai, dan dagani ba sai an fad'aba kallo d'aya za kai mai kagane hakan, Sauri yake yak'osa yaje gida saboda uzirin da yake da shi agidan, wani tudu-tudu yake gani na tun karo shi da alama koma meye igiyar ruwa ce ta jawo shi.
Tun kafin abun ya iso kusa da shi ya tabbatar da mutun ne, parking ya yi da jirgin nasa acikin ruwan, sannan yasa wata sanda dake cikin jirgin yarika jawo abun nan ahankali, sai dai tun kafin ya iso wajan shi ya tabbatar da mutum ne, dan yaga rigar ruwa ajikin mutum d'in ,shi ne dalilin da yasa bai nutseba acikin ruwan.
Cikin jirgin sa ya sata sannan ya tub'e mata rigar ruwan da ke jikin ta.
Al'ajabi ne ya isheshi ya ce " ikon Allah tom wannan kuma daga ina mutum cikin ruwa kuma mace"
Tafiya yake yana sake- saken yadda zai yi da ita, kai ko dai in yadda ta ne, tom in kuma fa nayadda ta kuma bata mutu ba fa?"
Nan dai ya yanke ma kan shi shawara akan ya kai ta gidansa alabashi yakira alheri ta dubata ta tagani ko tanada rai.
Bashi ya isa gida ba sai shida na yamma (6: 00pm) lokacin garin yafara duhu.
Yana shiga gidan ya d'akko ta daga mota kasan cewar yana fita gab'ar ruwan yayi parking a inda suke aje jiragan su. Ya d'auki drop d'in mota har gidan sa."
Bayan ya kwantar da ita ne nalura she Na'ima ce.
Waya ya d'auka ya turama alheri sako tazo yanzu yana son ganin ta.
Cikin mintina kad'an alheri ta iso gidan.
Alheri kallan shi tayi damamki ta ce,
"Abdurrahim wannan fa, ina kasamota?. "
Banza Abdurrahim yayi da ita kamar bazai amsa mata ba, sannan ya ce ahankali kamar an mai dole "Tsintarta nayi, ki dubata mana"
Alheri da mamaki take kallan Abdurrahim , so take tak'ara tambayar shi amma bataga fuskar hakan ba, dan haka taja bakin ta tayi shiru, ta fara aikin da yakawota.
Alheri tad'an kwashi mintina tana dubata, sannan takalli Abdurrahim ta ce,
"Abdurrahim k'alau take inajin furgicin da tayi ne yasata cikin wannan yanayin amma bari ina zuwa akwai allurar da zan mata yanzu.