← Book details A Tsakankanin Soyayya Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 58 OF 71

Sashe 58

A Tsakankanin Soyayya Complete Hausa Novel · about 7 min read

Jin fitan su Ammi yasa ahankali ta sauko kasa jikinta yay sanyi dan taji gabaki dayan maganganun Dady da Ammi, ahankali ta zauna agaban littafan ta tana kallon assignment din datafarayi dan gobe zasu bayar, rasa natsuwan ta tayi jin Aliyu ya kulle kanshi adaki yakima kowa magana, ahankali tadauki byronta zata cigaba da assignment din takasa, pink hijabin ta dake kan saman kujera taja tareda mikewa tsaye ta zura hijabin tai hanyar kofa, ahankali tabude kofan tafita daga dakin tareda maido kofan tarufe ta tsaya agaban flat din nasu tana kallon flat din Aliyun dake nesada su kadan sotake tahana ranta zuwa but takasa takasa hakura sabida jitayi yana cikin damuwa jitayi itama ta shiga cikin damuwa sosai, ahankali ta shiga taka matattakalan sauka daga gaban flat dinsu tasauka
Tai hanyar shashin Aliyun, agaban kofar sitting room dinshi ta tsaya heart dinta na racing kafin ahankali tasa hannu tabude dakin, wanan mayen kamshin nashine dahar tagane taji a falon, falon babu datti kodaya saiyan littafai datagani kan kujera kaman karantawa yake, ganin baya falon yasa ahankali tai hanyar bedroom dinshi heart dinta na racing but takasa hakura, tsayawa tayi agaban kofan kirjinta na bugawa fiyeda dazuma takasa knocking, wani irin sauke ajiyan zuciya tayi trying to calm her self down kafin ahankali tadaga hannunta zatai knocking aka bude kofan hada ido tayi da Aliyu dataga idanunshi sunyi jajir har kumbura sunyi kaman wanda yasha kuka, yana rike dawani babban trolley yana sanye da faran riganshi ta dazu, tsayawa yayi chak yana kallonta kaman yanda itama ta tsaya chak tana kallonshi tundaga kai har kafa kirjinta na bugawa, her heart breaking ganin yanda idanunshi sukayi tanajin wani irin sadness da bakinciki kaman suna sharing dsame feelings, lumshe ido yayi ahankali kirjinshi namai zafi kafin ahankali yabude su yadaura akanta dauke kai yay da sauri yaja akwatinshi tareda bi tagefenta zai wuce falo, kama hannunshi tayi da sauri tarike gam batare data juyoba wani irin kuka nataso mata, ahankali shima ya tsaya chak jin soft hand dinta rike da hannunshi.
[4/5, 8:09 AM] Hijabi_muslimah🙌: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_

_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤

_✍🏿M Shakur_

3️⃣7️⃣

Fita tayi daga kitchen din da sauri, hada ido sukayi da Abdul dake kan kujera yana rikeda remote din TV yana murmushi, dauke kai tayi da sauri tai hanyar stairs daidai Ihsan tafito sabida gajiya d jiranta datake tayi a daki tace "ainazaci afalo kikecin abincin shine nace barina biyoki" girgiza mata kai Aneesa tayi, cikin yar siriruwan muryanta tace "a'a, mukoma daki" juyawa Ihsan tayi sukai sama.

Ahankali ta zauna kan gadonta rikeda plate din abincin tana murmushi tana juyawa tana tunanan kalaman Aliyu dake ratsa mata zuciya, tana wani irin karajin maimaicin kalaman shi a kunnuwanta, tabatan da akayi yasa tadago kanta da sauri Ihsan ne kaman zatai kuka tace "kinki kulani, ba Momma tacemin mun zama friends ba, kodai bakisona ne a matsayin kawarki" da sauri Aneesa ta girgiza kai tareda ajiye abincin agefe ta zare hijabin jikinta ta ijiye tace "laaaa, no bahaka bane ina sonki a matsayin kawata sosai ma" murmushi Ihsan tayi cikedajin dadi tana kallon jikinta, wani milk color shimi tasaka ya kwanta a jikinta bulbul ya bayyanar da kirjinta sosai kaman zasu yaga sufito, murmushi tayi tace "to yaushe zakizo gidanmu ki kwana?" ahankali Aneesa tace "nima bansaniba amma zan tambayi Ammi da Abba insun barni zanzo I promise" murmushi Ihsan tayi tace "to shikenan dau abincin ki to kici hudu takusa zaku koma islamiya kumako" gyadamata kai Aneesa tayi ta faracin abincin haka Ihsan keta mata hira babu labarin makarantan su dabata bataba harta cinye abincin hira takemata, kwalama Aneesa kira da Ammi tayi yasa ta amsa da sauri. "na'am Ammi" daga tachan Ammi tace "kin manta zaki islamiya ne ko" da sauri ta kalli agogo hudu saura minti biyar, da sauri Ihsan tace "la mun manta tashi da sauri ki shirya" tashi tayi ta shiga bayi tadauro alwala tazo tai sallan la'asar sanan tai wajen wardrobe dinta, wani dogon rigan yar kanti tadauka baki ne color tasaka, tazaro wani clean ironed mustard color hijabinta har kasa tasaka tasaka safa sanan tadauko wani dan babban jakanta ta kwashe littatafan da aka bata aciki ta rataya ta kalli Ihsan dake ta binta da kallo itadai tanason wanan Aneesan tarasa mesa, waya Aneesa ta mikamata tace "gashi samin number ki zamu dinga WhatsApp" sakamata number Ihsan tayi sanan tarakota suka fito afalo sukaga Ammi da Momma sai hira suke Momma tace "har anfito yan islamiya to adawo lafiya" Ameen tace tana kallon Ammi dake binta da kallo batare datace mata komiba, turobaki tayi a shagwabe tace "Ammi bazakimin addu'a ba" dariya Ihsan tayi tace "laaaa ashe kina shagwaba katuwa dake" murmushi kawai Ammi tayi tace "wanan Ihsan, aina kosa Allah yakaimu ranan aurenta nayi na tarkatata nakaita gidan mijinta nagaji" kaman zatai kuka tace "niba inda zani ina tare da Ammi na" dariya dukansu sukayi Ammi tace "bazaki wuce kitafi ba kin tsaya surutu sai kinyi latti, kyasha dukan latti, adawo lafiya to Allah kiyaye, banda wasa kuma adage da karatu" bye tama Ihsan sanan tawuce tabude kofa tafita daga dakin already taga har yara sun cika wurin motar ana jiran driver yazo yabude su shiga, ahankali take tafiya tana nufan parking space din kaman ance ta daga kai da Aliyu suka hada ido dake gaban shashin shi yana mata wani irin kallo yay folding hannunshi a kirji, dauke kai tayi kirjinta na bugawa tarasa mesa kirjinta ke bugawa duk inta ganshi kasa daurewa tayi tadan dagokai ta kallai sake hada ido sukayi har lokacin itayake kallo kaman zai cinyeta da idanu, samin kanta tayi da dagamai hannu kaman wata yar koyo taimai waving hand din alamun bye da sauri ta kalli hannun nata kaman ma batasan lokacin data dagashi ba, dan murmushi yayi tareda lumshe ido yabude su ahankali yana kallonta ahankali yay waving nata back irin waving dinan na yaron dabayason maman shi tafita, dauke kai tayi da sauri tadena kallonshi dan hakanan taji yawani irin bata tausayi kaman zuciyanta da nashi na communicating, kaman zuciyanshi nace mata karki tafi kidawo ki zauna dani.

Karasawa wajen motan tayi har direba yabude yaran duk sun shiga Hajar ne kadai agaban motan, wani matsiyacin kallo tama Aneesan tace "gasu agola nan anzo" daidai Aneesa takaraso wajen Rauda dake cikin motan dan ciwon cikin yasaketa sosai yanzu tace "kai Anty Hajar wlh babu kyau fa" ta kalli Aneesa datai kaman batajisu ba tasakin mata murmushi tace "shigo ki zauna Aneesa" murmushi itama tamata dan sai yanzu ne tagane Rauda itace yarinyan data taimaka ranan data fara ganin Aliyu sarkin kallo sai kallonta yake kaman baitaba ganintaba, shiga cikin motan tayi ta zauna kusada Rauda, Hajar ta shigo itama sanan direba yarufe kofan yakoma gaba ya shiga yaja.

Ahankali Rauda tasa hannunta takarbi hannun Aneesa data danyi wani zanen lalle ta around kumbunan ta tace "wow Aneesa wanan wani irin zanen lalle ne? Bbu kodaya a hannunki saita wurin yatsun ki it really looks nice, waya miki ya bala'in burgeni, waya miki?" murmushi Aneesa tayi tana kallon yatsun nata zanen datayi ne da bikin Ammi saitama Ammi kuma lalli mai kyau, ahankali tace "ninayi" "iyye kin iya lalle ne daman?" gyadamata kai tayi tace "na iya, kinaso namiki?" da sauri Rauda ta gyada mata kai tace "inaso mana, sosai ma" ahankali Aneesa tace "shikenan duk randa kika shirya zan miki wanda ma yafi wanan kyau" washe baki Rauda tayi tace "nagode, Awani aji aka saki dazu a hadda?" ahankali tace "aji hudu, islamiya ma aji hudu" bangaje mata kafada Rauda tayi cikeda jin dadi hira irin na kawayen nan tace "iyye ajinmu daya ashe, nima dazu dasafe cikina keta ciwo saisa banjeba wlh" ahankali Aneesa tace "sorry Allah ya sawake" cikeda damuwa Rauda tace "kema kinayin ciwon ciki idan zakiyi?" gyadamata kai Aneesa tayi batare datai magana ba she's not just comfortable sabida Hajar dake wurin, dan tana ganin yanda Hajar ke hararanta itada Raudan kaman ta bubbuge su, cikeda damuwa itama Rauda tace "sannu kinji Aneesa, ance inkai aure yana denawa" "dalla malama kimana shiru ko kina maganan iskanci agaban yara" Hajar tafada cikeda masifa, cikin tsiwa Rauda tace "to wai me ruwanki dani Anty Hajar, yaran sunsam menake cewa ne, kinamin wani ihu saikace nayi dake" ta harari gefen side din Hajar din, murmushi Aneesa tayi hakan yakara harzuka Hajar tace "dan ubanki nikekema rashin kunya?" cikeda rashin kunya Rauda tace "karki kara zaginmin uba nidai, Dady na nagida yana hutawa abinshi kina duramai zagi, kuma ai badake nakeba daga ina firana da kawata saikiyi ta zagina, dakenayi? Neman tsokana kawai" kwashe wa da dariya yaran motan sukayi, wani mugun kallo Hajar tamusu hakan yasa at ukai shiru, Hajar tai kwafa tace "zamu koma gida kaman Mama taji komi" dauke kai Rauda tayi tacigaba da hira ta da Aneesa batakara cemata komiba harsuka kai makaranta suka tafi ajinsu a binsu.

***
Chapter 58 · 0% Book details