← Book details Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 36

Sashe 35

Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Acikin kwana kin kullum Salma makale take adakin Mujahid tana jiran farfado warsa, kusa dashi zata zauna tayi ta kallon kyakyawan fuskar sa dake sanye da robar oxygen, wataran tayi kuka wataran kuma tayi ta zuba mai murmurshi kamar wata zautacciya. Zuwan Faiza Uku duba Mujahid, saida ba dawata manufa take zuwa ba face amatsayin daya bata dan tunda ya mata zancen auran Salma yasa ta kame kanta tafara nemawa kanta bazawari, yanxu kuwa Allah yasa tadace wani chairman na karamar hukumar Tafa ke nemanta.
Yau Doctor yayi assuring dinsu Farfadowan Mujahid dan kwana biyu kenan da ciremai oxygen, lafiya kalau yake mayar da sauke numfashi, babu kowa adakin sai Salma dake zauna kan gefe gadon tana dubansa, murmushi ta saki takai hannu bisa gashi kansa ta shafe zuwa fuskarsa aranta tunanin ranar dazai tashi, bata taba expecting xai yi risking life dinsa to save her ba, Murmushi ta kuma saki tace "am sorry, it all my fault" kanta ta daura a fadadan kirjin sa tanai jin heart beat dinsa dake fita, lumshe idanu tayi, cikin dogon bacci da yake yaji dumin ta jikinsa ahankali yayi bude ido ya daura ta kansu, saurin runtse ido yayi saboda yadda yaji wani irin yanayi, left hand dinsa dake ajiye gefe ya daga ya daura bisa kanta, adan tsorace ta zabure zaune ganin tayi idonsa kulle, hannusa ta janyo ta rungume tana kallan sa, cikin sanyi murya ta kira sunan sa, bai amsa ba, kaman zatayi kuka ta cigaba da dubansa, kofar dakin aka turo yasata saurin mikewa tsaye cike da kunya ganin Hajiya ce, "Ya tashi ne ? Hajiya ta tambaya cikin kota kula da yanayin ta...
Sinne kai Salma tayi sai kuma ta dago ta dubi Mujahid taga Idansa bisa kanta, kunya ce ta kuma kamata, batace komai ba tafice a dakin da sauri har tana harde kafa.
Murmushi Hajiya tayi ta karasa gurinsa cike da farin ciki ya farka, magana zatayi taji yace "miyasa ta gudu, plz kice ta dawo bangaji da ganin taba" awahale yayi maganar.
Dan duka Hajiya takai mai cikin wasa tace "marar kunyar banza, saika bari ka murmure ai" dariya yayi ciki ciki yace "ina sonta alot".
Tsaki Hajiya tayi
"Ka manta sanda kace ko akafa aka daura ma baxaka jaba, toh kasani koka warke babu kai ba ita" in serious tone Hajiya tayi magana.
Tsurewa Mujahid yayi, yahau bata hakuri, banza tayi dashi ta zauna kan kujerar dake gurin, saida taka yana neman kuka sannan tace mai wasa take.

Agurguje filis.

Bayan kwana hudu ne Aka sallemi Mujahid gida, duk haduwan su da Salma babu mai cewa juna uffan, ya lura wata sabuwar sarar jin Kunya Salma ta tsiro dashi wanda tun abaya bai santa dashi ba, wataran bacci karya ma yake idan yaji shigo wanta dukda yaji kalaman soyayyan da take rangwada mai amma daya runtse take mazewa tamkar ba ita ba.

Gidan su Mom Salma ta koma da zama, hakan bai damu Abbanta ba, dan kuwa yaji dadi yadda Daddy ya riketa tamkar yar cikinsa, Su Junaina tuni su Aunty Bilki suka kaita gidan Jafar kaduna, hankalin su kwance basu da wata matsala.
Satin Salma uku agida Daddy yace zaman ya isa haka, dama abunda take jira kenan dukda ma ba waya suke da Mujahid ba amma ta matsu ta ganshi, ta bangaran Mujahid shima hakan ne akullum sai yama Hajiya Magiyan yaushe zaa kawomai Salma saidai kawai ta share shi taki tanka shi, sauki daya samu ma ya koma bakin aikin sa.
Daddy da kanshi ya kaita Gidan Mujahid bayan tasha fada da nasihohi iri iri da uban kwarai kema diyarsa.. Komai na gidan saida aka canxa sabo, Daddy da abbanta sunyi kokarin zuba mata tsadaddun kayan alatu. Bayan daddy ya tafi zaman shuru tayi da kadai ci koda Mujahid ya zo ya isketa babu wata magana dana shiga tsakanin su face gaisuwa, kowanne su dar dar yake da juna gudun kar ran wani ya bacci azo ana yar ramuwar gayya, dakuna daman uku ne agidan ko wanne da nasa dakin, haka sukayi ta zaman babu ruwan wani da agidan, idan Mujahid ya tafi aiki haka zata zauna tayi ta kewansa, da dare kuwa yana dawowa zata gudu daki ta zauna, daya shigo yaji kamshin ta a palon yasa barin palon tayi, murmushi kawai zaiyi ya wuce dakin sa.

Bayan wasu kwanaki, yau dawuri Salma ta tashi ta fita palo jiransa fitowar sa, so take tacemai sun koma skull zata fara fita, kamar munafuka ta takure da zumbulelan hijab.
Hankali kwance ya fito daga daki yana adjusting hulan sa na uniform din police, sai ganinta yayi jugum zaune, baice komai ba zai wuce tayi saurin mikewa tsaye hade da risinawa gaidasa, fuska ba yabo ya amsa, wucewa zaiyi yaji tace "uhmm zan fara zuwa skull gobe, munyi resuming"
Dariya ma tabata shi, wai uhmm yau kodan yaya babu, kallonta yayi, sosai ta bashi dariya da Hijab din, tuna sanda take sa kayan dake bayyana gaba daya jikinta yayi, kwafa yayi baice komai ba ya fice yana tunanin wai Salma da yakeso ta taba zubar da ciki, kodayake koma miye i still love her like dat.

Ajiyar zuciya Ta sauke ta koma ta zauna, tana son Mujahid saidai tafiso yafara sauraran ta kafin ta iya sakin jiki dashi, dan har yau takasa manta abunda Khaleel ya fada nacewa koda mujahid bai sont zai ji dadin hutuwa da jikinta, she need to know ko yana sonta dagaske.

Washe gari around 9 Salma ta shirya, yauma hijab din tasanya, Mujahid dakanshi ya kaita skull sannan ya wuce office, by 6 ne zai dawo daukan ta, mis taje tayi registration sannan ta tafi faculty dinsu taga time table harya fito kuma alokacin ma lecture garesu, hankalin tane ya tashi dan anyi 1 hour da farawa, da sauri ta nufi Hall din, ganin Faiza ke masu Lecture din yasa bata shiga ba ta tsaya bakin kofar, daga ciki taji Faiza tace mata ta shigo, jiki ba kwari tafara takawa ciki atunanin ta dizga ta zatayi sai kuma taga sabanin haka, direct gurin da mata ke zaune taje ta zauna, yan aji sai mamaki suke dan sunsan bata da gurin zama saida maza, su shehu kam so suke kadai suji ko dagaske tayi aure dan sunji labari a gari, Around 6 suka gama lecture da sauri ta fito ta tsaya inda Mujahid zaizo ya dauke ta, saiga su Shehu da habib su karaso gurin da fara'arsu, Shehu ne yahau tambayarta ko dagaske tayi aure, Daure fuska tayi, aranta tana rokon Allah kar Mujahid yaganta saidai mi bata gama adduar ba saiga motar sa ya iso gurin.
Habib yace "Salma kinyi shuru.."
Gabanta ne ya fadi gani ganin Mujahid ya fito daga motan, su Shehu kam saurin barin gurin sukayi ganin wani mugun kallo dayake watsa masu.
Fuska ba annuri yace da ita "kinyi auran ma bazaki fita harkar suba"..
Kuka ne ya kufce mata, cikin rawar murya tahau bashi hakuri, bude motar tayi ta shiga tana sharar kwalla, shima shiga yayi yaja motar, bamai yiwa wani magana har suka isa gida, da sauri Salma ta fito ta fada ciki.
Chapter 35 · 0% Book details