← Book details Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 36

Sashe 16

Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

8.20 Jaafar ya iso gate din Gidan Daddy, bai tab'a zuwa gidan ba yasa yakira Daddy awaya dan tabbar da gidan ne, nan take Daddy ya kira mai gadi aka budewa mai gate ya shigo gidan, cikin palo gidan Daddy yamai iso, ya shiga yagaida Mom aladabce, sosai mom ta yaba da hankalin sa, sun gaisa sosai, mai aiki ta kawo mai na shasha baki, shikam Jaafar gaban sane keta faduwa, har yayi dana sanin kowa kanshi gidan.

Mom kam murmushi kawai take tana saurara isowan Salma....
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta

~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
®NWA

43 - 50

Murmusawa Mujahid yayi ganin yadda take cikin walwala. Table dinsa ya k'arasa yadau wayarsa tare da mukulin mota. Ficewa sukayi daga office suka nufi ma'ajiya motar, Salma na tafe tana waya da Mom, cikin sauri tayi gaba ta tsaya bakin motar. Wayar sace tayi ruri, ya duba yaga Junaina da kuma miss call datai mai wanda bai lura ba sai yanzu, tsaye yayi nan inda yake batare daya karasa inda Salman take ba ya dauka.
"Little sis ya ake ciki ?
Kaman munafuka Junaina tahau duben ko ina a palo gudun kar wani yajita, murya kasa kasa tace "yayA naga ya jafs ya fita, kuma naji yana waya da wani zaije ganin wata yarinya, i dont know wace yarinya ce"
"Yaushe ya fita ?..
"Yadan jima kuma bai cewa Hajiya Komai ba"
"Okay Sis, ki cigaba da samai ido, i'll call you later" katse call din yayi ya karasa motan suka shiga, sai sannan ya tambayi salma dalilin tafiyar ta, bata boye maiba ta fadi mai Mom ke kiranta kuma it urgent.
Shuru Mujahid yayi yana tunani anya ba gidansu Salma yaje ba, wata zuciyar tace it cnt be possible, miye zai kaishi gidan, saidai surprise da Mom zata bawa salma ne ya tsaya mai arai, zuciyar sam bata aminta da hakan ba, kuma baiji yana son tafiyar Salma ayanzuba. Kallonta yayi da gefe ido yaga tana latsar wayarta fuska ta dauke da murmushi..
Murmushi yayi sannan yaja wani wawan burki da saida ta tsorota, afirgice ta kalle shi, gani tayi ya daura kansa bisa steering hannusa dafe kan gefen cikinsa, murkutsutsu yahau yi tamkar wanda zai mutu.
Tsabar gigita bata san sanda takai hanunta bisa bayan saba tanai tambayarsa maike damunsa, kasa magana yayi banda cije labb'a da yake, fita tayi motan ta zagayo gurin sa. Tambayarsa ta kuma tayi, murya ciki ciki yace "am sick, can you drive ?
Kai ta gigiza alamun eh, taimaka mai tayi ya koma dayan sit din sannan ta shiga taja motar.
Kaman mai shirin kuka ta kalle shi, "wana asibiti zamu ?
"Kaini gida kawai" ya fada yana lumshe ido, shingidewa yayi akan sit kaman wani marar lapian gaskia.
Hankali tashe tahau driving ba tare data tuna kiran da Mom ke mata ba, suna isowa gidanshi ta taimaka mai suka shiga ciki ayayinda sai faman cemai sannu take, shikam dariya ke cinsa yana gimtsewa. Zaunar dashi tayi kan two sitter sannan ta dube shi, murya cike da tausayi tace "sannu yaya.."
Yi yayi tamkar baiji taba saima rufe ido dayayi, itakam tanason tafiya ga dare yafara lulawa, gyara zama tayi ta fuskan ceshi tanai karemai kallon aranta tanai kara jin sonshi. Sunkai 20mins ahaka kafin nan ya bude ido, suna kallan juna, lumshe ido yayi yace hado min tea nasha magani"
Ba musu ta mike ta shiga kitchen ta hado ta kawo mai, k'insha yayi ya ajiye akan yayimai zafi da yawa, zama tayi tanai jiran tea yayi sanyi tanason tafiya saidai bata iya barin sa cikin larura.

Har kafar Tara su Daddy da jaafar na zauna suna jiran salma, shuru babu labarinta, sau kusan hudu Daddy na kiran wayarta babu respond, ransa ne ya bacci, nan yahau tambayan Mom, cemai tayi skull ta shiga karatu saboda exams da zasu fara, jin shaanin karatu yasanya Daddy yayi calming down, dan yasan lokacin exam Salma bata wasa. shikam Jaafar dadi yaji, amma aransa mamaki yake ace yarinya har yanzu bata dawo ba, jinjina kai yayi "anya ta arziki ce kuwa" azuci yayi maganar.
Hira kadan suka tab"a Daddy yace mai yayi hakuri idan ya dawo daga tafiyar sai yadawo kafin nan diyarshi ta gama exams sai ayi magana, Jaafar kam bai damuba, gaba ta kaishi gobarar titi a Jos, san samu ma kar Daddy ya kuma mai zancen. Sallama yayi masu yabar gida.

Mujahid kuwa shiriritar da Salma yahau yi, bayan tea yayi sanyi k'insha yayi wai zaiyi amai, saida ta kuma had'amai Black tea sannan yadan sha kadan da maganin bayan tasha walaha da lallaba shi sannan ya iya shan pill na magani guda daya, acewarsa daci yayi yawa. Bayan nan kuma ta tashi da niyya tafiya ya langwabe da ciwon kai, saida ta tayi zaman kusan 30 minti tanai mai sannu.. Karshe dai saida yaga 11 tayi sannan ya koma normal, tace mai zata tafi dare yayi, ba kunya yace suje ya kaita gida, itakam mamaki ne ya kamata mutum sai kace mai aljanu, tunani tayi anya ba raina mata wayo yake ba. Haka dai tabishi suka shiga mota, sai janta yake da hira, kasa magana tayi tsananin yadda taganshi garau, wayarta ta duba taga miss calls na Daddy, tsaki tayi aranta tace "Allah yasa banyi ranshi surprise dinnan ba"
Nan baki gate ya sauke ta tamai sallama ta shiga gida, Mom ta tarar zaune palo, dan tuni Daddy ya shiga ya kwanta, ganin Salma yasa hankalinta ya kwanta, fada tayi mata sosai akan dawowan dare amatsayin mace bai kamaceta ba, hakuri Salma ta bata, itadai surprise din takeson sani, tambayar Mom tayi taki fada mata komai sai ce mata tayi bayan exams zataji komai daga bakin Daddy.

***

Washegari langwabewa Mujahid yayi bayan yayi shirin sa tsaf na fita office, Salma ya kira yace ta taimaka ta kaishi office dan baya jin dadi, bata kowa mai aranta ba dukda dai zuciyar ta na kisyasta mata wani abu, kuma jiya taji dadin karatu a office dinsa. Gidan taje ta dauke sa suka tafi.

Tun ranar abu kaman wasa, kullum Salma na tare da Mujahid iyakacin taje skull tayi exam tadawo ta koma office dinsa ta zauna karatu, ko shopping zataje saidai ta zauna shi yaje yayi mata, sam bayaso ta fita ba tare dashi ba gudun kar yan'uwansa su ganta, balle jaafar da har yanxu neman ta yake.
Har azuciya Mujahid yasan ya kamu da son Salma saidai yayi alwashin rama abunda tamai dan kuwa bazai barta taci bulus ba, ganin yadda ta dukufa da karatu yasa ya bata lokaci dan gama exams dinta, ita kuwa Salma zuciya daya take zaune dashi, abu daya ke daure mata kai yadda bai furta yana sonta ba alhalin soyayya kuru kuru yake nuna mata, tanason sani mike zuciyarsa game da ita.

Ta b'angaran Junaina bata daina cusa kai gurin mujahid ba, ko tusa akai a gida saita buga ta fadimai, wataran rohoton sumai amfani wataran kuma data fara fadin abunda bai dameshi ba katse wayan yake. Kullum a rokonshin take ya dawo gida.

Yauce ranar da Salma ta gama Exams, tana fitowa Hall tayi kicibis da Faiza zata shiga next hall supervision, Hararan juna sukayi kowa ya wuce, kowane da abunda yake zak'awa game da junan su aranshi, K'wafa Faiza tayi aranta tace "yar banzan yarinya very soon zai jefar dake".
Tuni Salma tabaiwa banza ajiya, kobi takan Faiza bata kuma ba tq fada mota taja zuwa gida, karfe sha biyu ne lokacin, so take tayi wanka ta huta kafin taje gurin Mujahid tamai albishir din gama exams danba sani yayi ba.

Tana isa gida parking tayi ta fito, kokarin kulle motar tayi taji muryan Salim abayanta.
"Yau kuma baki je wajan sa karuwan ci ba ? Fuska babu annuri yayi magana.
Mamakine ya kamata, ta juyo tace "yaya karuwan ci, a ina, yaushe, ?
Mugun kallo yakai mata wanda daga gani asama yake, cikin zafin nama ya riko hannuta da karfin gaske wanda saida tadan tsaki kara, "ni zaki rainawa wayo Salma, gayamin uban mi kikeyi a office dinsa"
Kokarin kwance hannuta tahau yi takasa, bata rai tayi tace "zan kira Daddy idan baka sake niba.."
Mugun dariya yayi yace "tunda shine ke dauramiki gindin kina iskancin da kikaga dama ko, waya sani ma kokin bashi kanki"
Wani mugun girgiza Salma tayi da kalaman sa, cike da tsantsan bacin rai takai mai azababan mari da dayan hannuta, ba shiri ya saki hannuta yanai mata kallon mamaki lokaci guda kuma zuciyar sa ke tafasa, afuce ta nuna shi da yatsa "idan kana iskancin ka yakare akaina karka kuskura kasako min iyaye, banza, dan akuya kawai, kuma kasani i hate you Mujahid nakeso bakai ba wanda baisan ciwon kansa ba"
Dafe Kunci Salim yayi yana huci, tunanin abunda zai mata kawai yake, Harara ta ballamai, wucewa zatayi yasa mata kafa tayi wani mugun faduwa kasa wanwas, adan tsorace ta daga kai ta budeshi, sosai ta tsorata da yanayin, "anya Salim baya da hankali" ta fada aranta.
Nunata yayi da yatsa yace "ni kika mara saboda da wani banza, aikuwa sai kinyi danasani zan nuna maki ni ba wawan da kike tunani bane" juyawa yayi ya tafi, zuciyarsa na tafasa, shi kadai yasan makircin da zai shuka mata gurin Mujahid din da take takaman tanaso da kauna.

Salma kam tsoro ne sosai ya kamata, mikewa tayi kokarin yi ta kasa zabar azabar dataji kafar ta guda nayi, dakyar da azaba ta mike tsaye, kaman tayi ihu dan azaba, awahale ta iya jan dayar kafar ta karasa cikin gida, bata iya shiga gurin mom ba ta wuce dakinta.

Duk akan Idon Salim, yaji dadin yadda yaga ta kasa takawa, koba komai dole ta hakura da zuwa gurin Mujahid, murmurshin Mugunta ya saki afili yace "zaki gane kuran ki .............

Ni xarah nace Toh Fah, Salma duk ke daya, enemies ta ko ina.
Allah ya karemu daga sharin masu shairi.
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta

~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
(Aunty cute)
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION...

Wattpad Cutexarah
Blog xarahbukar.wordpress.com

51
Chapter 16 · 0% Book details