← Book details Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 36

Sashe 25

Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ahankali Junaina ta turo kofar dakin ta shigo, babu kowa ciki tayi tunanin koya fita, wayarsa data gani kan gado yasa ta karasa ciki hade da daukar wayar, camera ta shiga zata dauki kanta Selfi ya fito daga toilet. A tsorace ta dire wayar, cikin inda inda tace "Good morning".
Mamaki ne yakama shi, yaushe Junaina ta renashi haka harda shigomai daki batare da izinin saba.
Fuska ya murtuke "ke!!! Miya shigo dake nan..
Kaman marar gaskiya ta ware idanu, "dama wai kiran ka zan..."
Katse ta yayi da cewa "wato bincike kika zo yimin ad'aki harda daukan wayata, gayamin waya aikoki ?
Yadda yake magana yasa ta tsorota, bata ga alamun wasa tattare dashi ba, kaman zatayi kuka tace "wallahi yaya ba bincike nazo yi ba ?..
Cikin tsawa yace "karya kike, ni nasan halin ki am sure kuma rahoto kikazo samu dan kaiwa gaba".
Kasa magana Junaina tayi, gabanta na dukan uku uku, ga kuma haushi kalamansa daya turnuk'e ta, koda take nemo rahoto aishi take kawo wa shine kuma yau zaiyi turning tables around.
"Get down on your kneels" ya fada cikin harsh voice.
Kuka ta fashe dashi "yaya dan Allah kayi hakuri"
Rab'awa yayi ta gefenta ya wuce yana cewa "bari na dauko belt, yau sai kin gayamin ubanwa ya aiko ki"
Da sauri tayi kneel down tana rokansa, belt ya dauko ya tsula mata daya abaya, ihu tayi tace "na shiga uku, yaya wlh da akwai zafi"
Jinjina kai yayi yana tunanin anya ba ita tasamai abu mai yaji a shower gel dinsa ba, dan kuwa kafin yafita playing b-b yayi wanka da gel din baiji yaji ba.
Fuska ba annuri yace "wato daxun kin shigomin daki ko ?.
Ware ido tayi cikin rashin fahimta, yace "badake nake ba" daka belt yayi zai tsula mata.
Tace "yaya wlh yanxu nashigo, daxu dai naga Adda Ummi ta sauko daga stairs bansani ba konan ta shigo" kuka sosai ta fashe dashi
Cize Lab'a Mujahid yayi aranshi yace "lailai yarinyar nan ta cika yar daba" kallon Junaina yayi yace "b4 d count of three tashi ki bace anan"
Mikewa tayi ta fita da gudu tana sosa baya.

Nisawa Mujahid yayi yakarasa bakin mirror, cire glass dun fuskar sa yayi yanai kallon idonsa dayai jajir ya duru da ruwa, wani irin raradi da azaba yake ji.
Sunan Salma kadai yake ambata aranshi, shi kadai yasan rashin mutumcin dazai mata.

A can Garden kuma.....

To be continued......
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta

~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
(Aunty Cute)

NAGARTA WRITERS ASSOCIATION...

Allahu akbar kulu'nafsi za'ikatu mauti, Allah yaji kanki da rahma Maman besty Yar ficika. May jannatul Firdausi be ur final destination.

58

Acan Garden kuwa zaune suke kan d'aya daga cikin kujerun, Jafar kam duk'ufa yayi da danna laptop dinsa kasancewar wani babban aiki dayasa agaba, Salma kuwa wayarta kadai take latsawa, so take ta kira Mujahid amma tafasa gudun karya dago abun data mai, ajiye wayar tayi a cinye hade da sauke ajiyar zuciya.
"Kin gaji ne ? Jafar ya fad'a yana cigaba da aikin sa ba tare daya dube taba.
Dubansa tayi.
"Bakai ka shareni ba" ashagwabe tayi maganar.
Dariya yayi
"Kinga wani case nake bincike akai, mayb zuwa next week zanje Kaduna"
Dadi Salma taji aranta, idan ya tafi zata samu sararin yiwa Mujahid rashin mutunci.
"Murna kike zan tafi ko ? Ya jeho mata tambaya.
Kunya ce takamata, ta dake tace "yazaka ce hakan bayan kai yayana abun alfahari nane, ni wlh banso ka tafi kaine kaidai good abu arayuwa ta"
Murumshi yayi, ciki ciki yace "naga alama kam".
Bataji abun da yace ba, zatayi magana suka ji ana rangad'a uban horn daga can bakin gate, maida dubansu sukayi b'angaran, wata mota jeep ce ta shigo ta karasa maajiyar motoci ta tsaya.
Salma tace "suwaye ne..
Mikewa tsaye yayi itama ta mike suka fara tawaka gurin....
Wata kyakyawar tsohuwar matar ce ta zuro kafa daga motan ta fito, da ganinta kasan ta hada alak'a da masu gidan, da azama driver ya zagawo gurin ta hade da risinawa ya mika mata wani sliver walking stick, amsa tayi tanai karewa gidan kallon hade da sauke sanyayyiyar ajiyar zuciya.
Gaban Salma ne yafadi, tagane matar data gani a hoto ce, murya jafar taj yace "Granny dinmu ce, mahaifiyar Daddyn mu"
Yaken dole Salma tayi, kwakwata bataga alamun annuri a fuskar taba, shuru tayi suka cigaba da takawa gurin da take tsaye tana shakar sanyayyar iskar gurin.
Daga inda suke tagowa Jafar yace "wa nake gani kaman Annah." Karashe maganar yayi cikin zolaya.
Dariya Annah tayi har hakoranta suka bayyana.
Ga mamakin Salma taga Annah ta juya wani bangaran tana lalube, cewa take "Jafar kaine ko kuwa kunne na ne ?
Karasawa yayi ya rikon ta, yana dariya gani tanan".
Tace mikomin gilashi na yana mota, dauko mata yayi ta amsa tasa sannan ta kallesa "wato kun gurma ko ganin ku baa yi, tunda baku iya zuwa gurina gani zo gurinku"..
Dariya yayi.
"Kai Annah daga zuwa sai neman sababi ?
"Kaga ni bani guri" ta fada, wucewa zatayi Salma tace "Annah ina wuni ?
Kallon Salma tayi, bata amsa ba sai tab'e baki datayi ta wuce.
Jiki sanyaye Salma ta dubi shi.
"Bata gani ne ?
Alamun tayi shuru yayi mata, saida Annah ta masu tazara yace "zaki sha duka idan taji kinci mata bata gani, tana gani amma sai da glasses,
Ware ido salma tayi.
"Miya sameta halan
"Bakomai, ciwon idon gada sukayi gurin babansu, sai dai nata yayi worst, sau biyu ana mata operation"
"Allah sarki, amma naga ku yaran Hajiya baku gada ba"
Dariya jafar yayi, yace "inji wa, koda yake niban da matsalan ido, Aunty Bilki da Mujahid suka gado ta"
Mamaki ne yakama Salma bata ga alamun ciwon ido ga mujahid ba, dama ma Aunty Bilki tanasa glass.
Shuru tayi suka cigaba da tafiya ciki.

Side drawer Mujahid ya bude yadauko wani magana a tube ya diga a idon, wani mugun azaba yaji, maida black shade yayi ya fice daga d'akin.

Ta bangaran Junai kuwa kitchen ta shiga ta zauna matsar kwalla, koda Hajiya ta fito ta isketa a hakan ba tambayar da batai mata ba taki fad'a mata komai sai cewa tayi cikinta ke ciwo, Palo hajiya ta riko ta suka dawo tanai mata sannu.

Banko kofar Palo Annah tayi batare da Sallama ba ta kutsa kai ciki ta fadin "ba kowa agidan ne ?
Adan tsorace su Hajiya suka juya kallanta jin yadda aka banko kofar, bata yi samma nin ganin taba ba dan kuwa sunyi waya jiya bata ce mata tana tafe ba.
Dakyar Hajiya ta iya hadiyan yawu tace "Annah sannu da zuwa, aibansan kina tafe ba"
Tabe baki tayi ta kalli yadda palon ke haskawa da kayan alatu, tace "yanzu kin ganni ai
Shuru Hajiya tayi, Junaina ta gaidata, nunata tayi da walking stick din tace "kece haka kika girma ?
Magana Junai zatayi Salma da Jaafar suka shigo palon adaidai lokacin da Mujahid ya sauko daga stairs.
Zubamai ido sukayi, ko kallonsu bayi ba, fuska daure ya kama hanyar ficewa, dakatar dashi Hajiya tayi da cewa "bakaga Annah ba zaka wuce ?
Tsaye yayi chak yanai ma wani Annah mugun kallo ta Black shade din fuskar sa, aranshi yace "uhnm sai yadda ta yuyu kenan, nakuda ad'aki mayya"
Afili yace "mai makauniyar nan tazoyi agidan nan ?
B'ata rai Annah tayi ta k'arasa kusa dashi, bai ankara ba yaji ta fara kaimai Duka da Sandar hannu ta tana fadin "uwar ka nazo, dan tselan uwa kawai" ta ko ina tahau kaimai bugu, ihu kadai yarage baiyi ba tsabar yadda sandar keda zafi, Salma kam dariya tahau babbaka wa, ayayinda saura kuma suke kallon Annah cike da takaicin abunda take, Mujahid kam ganin ba bari zatayi ba yasa yayi hanyar waje da sauri, baima lura ba yaji ya buge kai da bango, da azama ya fice waje.

"Ni zai nunawa duniyan ci kamar wace ya samu sa'ar sa" Annah ta fada Masifa sosai tahau yi, Salma kam kasa daina dariya tayi, da sauri tabi bayan sa waje, Mugun kallo Annah takai masu, tace da Hajiya ke kuma muje ciki ina da magana dake, haushi biu ne yakama hajiya ba yadda ta iya ta marawa Annah baya suka shiga daki.

Ajiyar Zuciya Junaina ta sauke ta kalli Jafar dake tsaye yana jin haushin fitar Salma, tace "yaya Alhakina ya kaima ya Mujahid, dazu bakaga dukan da yayi min ba
Da mamaki ya kalle ta, "duka kuma, mi kikayi ?
"Daga daukar wayarsa, wai bincike zan mar, yahau ni da zagi da duka"
Dariya zancenta yabashi, yace "yayi maganin ki kenan ?
Turo baki tayi "aini yanxu ba ruwana dashi, he is so mean".
Murmushi yayi, Baice komai ba ya wuce ya haura sama, turo baki tayi ta tahau gungunin baice mata sannu ba.

Haraban Gidan Salma ta fito waigen inda Mujahid yake, daga can nesa ta ganshi gurin parking motaci zaune kan boot din motarsa, kansa daure bisa cinyar sa.
Karasawa tayi gurin tana mamakin miyake yi gurin. Yana jin tsayuwar ta gurin yaki d'ago wa, hannu tasa ta d'ago da fuskar sa tana fadin "yaya badai dukan nan yasaka kuka ba" cike da zolaya tayi maganar, saidai ganin shatin dukan da yadda fuskarsa ta kumbura yasata ta shan jinin jikinta.
Hawaye taga ya fara gangarowa bisa kunci sa, yace "hankalin ki ya kwanta koh tunda kinga karshe na?
Cike da kidima da tsoro take kallan sa, gabanta sai faduwa yake..
Murmushin takaici yayi yace
"Am sorry nasan nayi hurting dinki, plz forgive me".
Tausayin sane ya kamata saidai bazata bari ya raina mata wayo ba, tace "miyasa sai yanzu zaka nemi afuwata ?
Ahankali ya zamo daga kan motar, suna fuskan tar juna, cikin sanyi murya yace "Salma i love you alot, dou nasan ba lailai ne ki yadda ba but tun ranar dana fara ganinki nakasa samin nutsuwa, kawai karfin hali da ego irin nawa yasa ban taba fahimtar hakan ba sai yau"
Kur Salma tayi mai da idanu, danson tantance gaskiar maganar sa ko kadan bata yadda dashi ba, saidai taji dadi i love you daya ce mata, kalamar data jima take son ji garesa, koda ace karya yake itadai taji dadi.
Chapter 25 · 0% Book details