← Book details Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 36

Sashe 32

Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Parking Salim yayi a haraban gidan ya fito rike da ledan abinci daya kawo mata, ahankali yasa mukulli ya bude kofar sannan ya shiga, kasa ya ganta kwance a dakin ta kudundune cikin Hijab, Murmushi yayi aranshi yace wato tayi kokarin yaki da maganin.
Sunan ta ya kira ta bude ido ahankali ta kallesa, bakin magana kawai take dashi amma babu wani karfi Tattare da ita.
"my love kin tashi" ya fada yana shafan fuskar ta, murya sanyaye tace "yaya why, miyasa zaka kawonin nan ?
Murmushi yayi ya dagota zaune suna fuskan tar juna, yace "Salma ina matuka sonki, bazan iya hakura ki auri mujahid ba, cox nafishi sonki"
Dakyar ta iya sakar mai harara, tace "miyasa kace ka fini sonshi
"Salma biliv me, akwai certain time danayi confronting mujahid akan ki nace mai kin zubar da cikina, inda yana sonki dagaske bazai nemi wulakanta ki ba harya yayi kokarin daura miki kisan daba ke kika aikata ba"
Kallon mamaki Salma tamai dajin shairin da yayi mata, amma toh yaushe akayi hakan Mujahid bai taba gayamata ba, wata zuciyar tace ba sonki yake ba tayaya zai gayamaki, Ajiyar zuciya ta sauke, tana son Mujahid bazata bari Salim ya nemi aibata saba.
Bata rai tayi tace "wanda kema son gaskia baya binka da shairi, no matter how bad Ya Mujahid yayi treating dina i still love him, kaga tashi ni kamaida ni gida"
Daura fuska Salim yayi yace "keda gida har abada, you're mine, Ghana zamu tafi gobe"
Mugun kallo tamai sannan ta mike tsaye da kyar tace "you're crazy, no wonder kayi drugging dina dan ka gudu dani, toh wlh baka isa ba" afusace tayi maganar, wucewa zatayi gefensa ya fizgo ta tafada cikinsa, matse ta yayi gam yana shakar kamshi jikinta, batasan sanda wani karfi yazo mata tasa hannu ta turesa hade da kai masa kyakyawan mari.

Kallon mamaki yayi mata sai kuma ya kwashe da dariya uwa tababbe, hannu yasa cikin aljihun sa yadauki wasu kwayoyi gudu biyar ya watsa a bakin sannan ta kalleta
"Ni kika mara ?
Harara takai mai.
"Dont you dare touch me, banza marar hankali"
Murmushi yayi hade da lasar labb'an bakin sa, ya karasa daf da ita ya shako wuyanta tare da hijab dinta, zare idanuwa tayi da already sun canza launi, magana take sonyi takasa tsananin yadda taga ya koma mata uwa zaki, harshen sa yakai kan fuskar ta yana lasa, da sauri tasa k'afarta ta ture sa hade da matsawa, yawu ta hada abakin sannan ta tofa mai a fuska tace,
"wanna ba so bane, rashin hankali ne" akufule yace ni kika tofawa yawu ?" Ba tsoro tace "eh kai din, niba kare bace da zaka na lasar min fuska."

Haushi da takaici ya cika sa, ya tako gabanta tare da bata k'akk'aywan mari guda biyu a fuska, ihu ta sakani dan azaba, bakinta ya fashe yana zubda jini, yace "zan nuna miki kare ya fiki daraja"
Daukar ta yayi tsam ya wurga ta kan gado.

Ihu take tana kiciniyar kwace kanta, shikam ko kallon baiyi ya yage wuyan hijab din ya cire, danne mata hannuwa yayi yahau kai mata kisses ta ko ina ajikinta, kuka tasoma tana rokansa, bai saurareta ba yahau kiciniyar cire mata riga, ringing din wayarsa a aljihu ne ya katse mai hanzari dubawa yayi yaga Mom ce, gabansa ne ya fadi yayi saurin dagawa daga jikinta, itakam Salma kuka take, kallon ta yayi duk ta firgice, yace "zanje na dawo inci gaba daga inda na tsaya"
Sauka yayi kan gadon tayi saurin rikosa "yaya kayi hakuri, na yadda zan auraka, dan Allah karka cuci rayuwata, ka kaini gida plz"
Yace "saboda kin raina ni ko, na maida ki gida dan ki auri wacen banza ko ?
Kai ta girgiza, tsaki yaja ya tureta da karfin gaske har tana bugewa da gadon, yayi gaba ya fice yabarta nan dafe da kanta.

Gidan su Salma Mujahid ya nufa, dakyar ya iya samun ganin Mom a haraban gidan saboda yawan mutanen dake cikin gidan, fuska daure tamai iso saboda haushin su Hajiya da Annah da takeji.
Hankali tashe yahau tambayar ta ko Salma na gidan, ranta ne yakuma bacci da sabon rainin wayon da takeji, banza tayi dashi saida yace mata Annah tacemai batasan Inda Salma take ba sannan Mom ta saurare shi, mamaki ne yakamasu, Mom ta kwalla kiran maigadi ta tambayase ko yaga fitar Salma, yace tunda ta dawo baiga fitar taba. Hakalin sune ya kara tashi Mom ta kira Salim awaya, koda ya iso tsaye yaga Mujahid da Mom akidemi, cike da tashin sense Mom ta tambayashi koya ga Salma, ware ido yayi kamar gaske yace bai ganta. Salati Mom tahauyi. Mujahid kam kallon banxa ya aikawa Salim dan kuwa bai yadda dashi ba, karasawa kusa dashi yayi da niyyan mai magana yaji kamshi Salma ya ajikinsa, kaman jira yake ya damko wuyan sa, cikin huci da haushi yace "ina ka kaimin Salma ?
Bata rai salim yayi ya turesa, Mujahid yakai mai naushi, nan dambe ya chakwade, Hankalin Mom ne yatashi gudu kar yan ciki su fito, mai gadi ta kuma kwallawa kira, yazo ya shiga tsakanin su dakyar.
Saurin jan Salim tayi gefe ta kalli Mujahid, tace "yanzu ba lokacin fada bane, nemo inda ta shiga yakama ta kayi, tun kafin Daddy yasan cewa b'ata tayi, kuma kai kasan Hajiyar ku bazata so jin wannan mugun labari ba, duk inda aka shiga kaine main suspect saboda dakai tayi waya last kafin na nemeta na rasa" tana gama maganar taja Salim sukabar gurin tanai bashi hakuri.
Fuzgar da Iska Mujahid yayi ya juya ya fice daga gidan ya tsaya nan waje bakin motar sa, yasan cewa indai Salma is missing bashi da haufin cewa babu hannu Salim ciki, amma yazai yi bashi da evidence da zaa yadda dashi, duk Annah ta kara wuta cikin lamarin, inda tun asali batai karya ba da tuni ya binciko inda Salma take.
Haushi ne yakamasa baima san ta ina zai fara ba, wayarsa ya ciro a aljihu ya kira Mubarak, sun jima suna waya sannan ya katse ya shiga motar sa yaja yabar gurin.

Masoyana kuyi hakuri da typing din yau sai ahankali...bana jin dadin jikina kwana biu, yanxu haka am on medication.
[9/7, 12:38 AM] Xarah Bukar: ​Zuma Sai Da Wuta

~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ

62

Gabad'aya Mujahid ya gama birkicewa, cike da kid'ima yahau laluban mukullin motar sa dake aljihun wandon sa.
Saurin rik'osa Abdul yayi yace,
"kabar tayar da hankalin ka, koka nufeta ba sauraran ka zatayi ba ayadda ka mugun b'ata mata rai"
Dafe kai Mujahid yayi cike da tsantsan tashin hankali, duban Abdul yayi da rinannun idanuwan sa da suka sauya launi zuwa ja.
"Ya kakeso nayi, dole naje na fahimtar da ita".
Hannu Abdul ya daura bisa kafadar sa.
"ka bari ba yanzu ba, she need some time"
Shuru Mujahid yayi batare daya iya cewa uffan ba, sun d'an jima nan tsaye kaman sanduna daga bisani suka koma ciki. Wayarsa dake ajiye kan kujerar palon yadauka ya kira Salma, saidai ba bugun duniyar dabai yiba fir taki dauka.

Akan titi kuwa wuta sosai Salma take bawa motar ayayinda take zubar da hawayan bak'in ciki, dakyar ta iya karaso da kanta gida, Afusace ta bude motar ta fito batare da ta tsaya bi takan wayarta ba, wani mugun juwa da azababban ciwon kai ke barazanar barar da gabobin jikinta.
Adaddafe tafara takawa zuwa bangaran Salim wanda ayanzu ta tabbatar shi daya ke mata son gaskia, sab'anin da datake mai kallon wawa, soko marar hankali, yaudai gashi wanda take ma kallon zinare yazame mata bak'in gwarwashi.
Kuka take sosai ta k'usa kai cikin palon, kwance ta iske shi bisa doguwar kujera duk jikinsa mace, da alamun ma cikin zufin tunanin yake, sunansa ta kira cikin sheshek'a tare da fad'awa jikinsa, Atsorace ya dagota ya yunkuro zaune yana kallon ta, duk ta gama birkice sa da kamshin jikinta, tunda suke gidan bai taba ganin ta cikin mugun yanayi aka ba.
Cike da firgita yahau tambayan ba'isin kukan ta, kasa magana tayi saima sautin kukan ta daya tsanan ta, hankalin Salim ne yatashi, dakyar ta iya cewa
"Yaya kaina ke ciwo"
Janyota yayi ta kwanta bisa kirjinsa yanai mata sannu hade da bubbuga mata baya cike da lallami, sosai yaji dadin yadda suke makale da juya, aransa sai aiyanawa yake dama tazo mai yanzu yakamata ya mayar da Salma tashi ta har abada.

Salma kam kukan ta take, ko tuna abunda ya faru bata sanyi, yadda zata gayawa Daddy ta fasa auran Mujahid kadai ne matsalan ta, tunda tun farko ita tace tagani tanaso bawai tursasa ta akayi ba.
Dagota yayi ahankali ya jingine ta jikin kujerar, cikin sanyi murya yace
"bari nadauko miki maganin ciwon kan"
Kai kawai ta daga mai, ya wuce dakin sa, side drawer ya bude ya dauko wani magani dani kaina bansan na miye ba sannan ya fito yadauki bottle water dake ajiye center table ya karasa gareta..
Salma kam bata kaunar magani, dakyar da lallami ta yadda tasha pills guda biyu daya dauko, ubansa tayi ido jajir tace, "nagode"
Aranta kuwa danasani take dama tun farko shi ta baiwa soyayyan ta, koda yake bai baci ba zata fadi ma Daddy shi takeson aura ba Mujahid ba. Shingid'e kanta tayi kan kujerar, Murmushi Salim yayi yahau goge mata hawayan fuskar ta, bayan kaman minti biyar tafara ji nauyin jiki da kasala, mikewa tayi tace
"yaya sai da safe"
Yace "Allah ya kaimu" aranshi kuwa yace keda ganin safiya badai a gidan nan ba.
Taku tafarayi ahankali taji mugun hajijiya, abubuwan dake palon biyu uku tafara ganin su, bata aune ba taji ta ta fadi kasa wanwas.
Chapter 32 · 0% Book details