← Book details Ubayd Maleek Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 66

Sashe 48

Ubayd Maleek Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

_TSAYA KUJI, A RANO NET ZAKA IYA ZAMA RESELLER KO WHOLESALER KAI MA, EH ZAKA/KI IYA ZAMA MA SAYAR DA DATA A FARASHIN SARI MUKE BAYARWA, KAI/KI KAFA KASUWANCIN KU KUMA. DA KUDI KALILAN._

_MUNA KUMA SAYARWA AKAN ‘DAI DAYA, KOWANE NETWORK MUNA SAYARDA DATA PLAN DINSA AKAN KUDI KALILAN, MASU FARASHIN SARA KUWA MA KU KUDIN BAI KAI HAKA BAMA_

_AIRTEL_
_9MOBILE/ETISALAT_
_MTN_
_GLO_

_DUK MUNA SAYARDA TSARIN DATA DINSU. KAMAR MISALI MTN MUNA SAYARDA 1GB.24MB AKAN FARASHIN NERA 300 KUMA YANA KAIWA WATA DAYA, GWARGWADON YADDA KAKE AMFANI DA DATA, 2GB 600, 3GB 900!!_

_DUKA WADANNAN TSARIN DATA DAMA NA SAURAN LAYIKA MUNA SAYRWA AKAN FARASHI MAI RAHUSA, WANDA KOWA ZAI IYA YIN TSARIN DAI DAI ALJIHUN SA_

_Ranonet.com.ng_
_GA SITE DINMU NAN DAKE YANAR GIZO, KAI TSAYE ZAKI/KA IYA SIYAN NAKA TA NAN. _

_KO A TUNTUBE MU TA NAMBAR TARHON MU: +234 803 081 1300/+234 808 540 5215_

_KYAU, INGANCI, RAHUSA, ADADE ANA YAWO A YANAR GIZO SAI RANO NET._

_RANO NET..!!!!_

****************
Direct dakin afia din NURU ta nufa data fito farhat ma ta tashi tana biyeda ita suna shiga dakin ta waiwayo tana kallonsu farhat ta qarasa gurinta da gudu cikin tsananin farin ciki me yawa tana cewa"

Yeeee afia.

Rungumeta afia tayi cikin farin cikin ganinta da kewarta datayi kwanakin tace"

My baby I love you I love you.

I love you too afia Kuma nayi kewanki sosai musamman kafin Aunt NURU da daddy sudawo nikadai dasu mum Sarah munata Jin dadinmu.

Rungumeta tasakeyi tana kallon NURU dake kallonsu cikin murmushi ta qaraso tana kallon afia din tace"

Sannu da zuwa.

Murmushin afia tayi tareda sakin farhat taqaraso gaban NURUn suka Dan rungume juna NURU ta bude Baki ahankali tace"

Am sorry afia ban....

It's ok yawuce Dan nice yakamata na Baki hakuri akan abinda mum Dina ta...

No afia yawuce kaman yanda kikece abar maganar.
Zamewa sukayi NURU na gyara tsayuwa tace"

Bari natayaki jejjera kayanki a dakin kafin agama breakfast muci.

Tayata bubbude kayan tayi suka jere suna fira anan NURU ke sanarwa afia din gobe zata fara zuwa Court Inshallah ita dayake tafara zuwa asibitin kafin wannan rigimar ta dakata sai itama tace gobe zataci gaba da zuwa kada tun wuri rashin bada himma yashiga cikin aikin.

Suna gamawa NURU ta fito ta nufi dakinta tayo brush ta sauyo Kaya ta cire na baccin dake jikinta wainda takejin nauyinsu tun dazun agaban afia.
Afia dasuka zauna cin abinci Bata wani samu damar sakewa taci sosaiba sbd tunanukan dasukai yawa akanta musamman na mum dinta da batasan meyake faruwaba a gizah din ga dad dinta har lokacin wayarsa Bata Shiga gashi takasa tambayar NURUn dad saidai ta tambayi farhat tafada Mata yayi tafiya baya Nan.

Sosai NURU ke kokarin janta da fira sbd su samu duk su dukan su sake dan sukoma kaman yanda suke wannan sabon yanayin nasu bayayiwa kowaccensu Dadi
Da Haka dai gurin firar suka fara sakewa suna danne komai tareda qoqarin mantawa kawai ahaka dai har dare yayi suka kwanta washe gari kowannensu ya tashi kan lokaci sbd Shirin fara fita zuwa gurin ayyukansu
Sukai breakfast suka fito NURUn na sanye da white long sleeves da White pencil trauser sai black kimono har qasa sai brawn and white scarf dake kanta da takalmi wedges na _Le labo_ sai handbag da Jakarta rigarta
Afia kuwa cikin jeans da shirt take sai white coat dake jikinta ta likitocin asibiti suka fada mota Edward ya fita dasu aka fara aje afia kafin aka wuce aka Kai NURU.

*************
Ranarda jekadi suka iso gizah tundaga shigowarsu padima ta 'dan kalli jekadi tana gyara zama cikin motar da aka daukosu daga airport tace

Saqona na NURU datace za'a bani ko za'a banishi tun ayau inason hada kayana guri dayane idan ba damuwa.

Waiwayowa jekadi tayi ta kalleta tareda sakin murmushin manya tace"

Babu matsala saqonki a Daren yau Zaki fara karban abinki basai kin damu kanki da tambayawarbama za'a Baki komai dukkanin abinda Kika cancanta.

Murmushi padima tayi tana dauke Kai tareda cewa"

Yawwa dai Ngd Sosai.

Suna Isa har kofar dazata sadasu da sassan Matar maleek ma'ana sassan NURU anan akai parking suka fito Kai tsaye suka shige hanyar suka wuce sassan NURU sukabi wata hanya sukai tafiya me tsayi datasaka padima fara waiwaye tana son yin mgna Amma tana dannewa sbd tasamu tafara riqe abinda za'a Bata din tukuna.

Sassan maleek suka nufa suka kusa can baya sosai inda wani boyayyan gurin sirrinsa yake jekadi ta waiwayo tareda kallon padima tana bude kofar tace"

Bismillah shigo daga ciki.

Ba wani tsoro padima ta qaraso tana leqawa ta shige sbd ganin kamar dakin ajiyar dukiyane ta qarasa ciki tana dube dube tanajin matsuwar abata abinda za'a Bata ta bar gurin sbd kaman tsoro da fargaban gurin na neman shigarta.

Mintuna biyar ba'ayi ba da shigarta saiga jekadi dauke da ruwa da drinks masu sanyi a tray ta qaraso tana ajiyewa kan table dake dakin tana cewa"

Bismillah.

Dagowa padima tayi ta kalli tray din kafin ta kalli jekadi tace"

Anan ne saqon yake?

Wannan karon jekadi Bata kalletaba tace"

Eh saqon ne za'a Baki idan kinyi hkr Yana isowane.

Shiru padima tayi cikin qaguwa da gagfawarta ta saqon yashigo hannunta tasaki guntun tsaki cikin ranta tareda Kai hannu ta dauki lemun takai bakinta tafara kurba ahankali tana kallon kofa tana Jin matsuwarta na qaruwa harta shanye lemun ta dauki ruwama Tasha kadan ta ajiye tareda Miqewa dagakan kujera daya tal dake dakin sai table da kayan adon daki masu kamar zaiba ta juyo tana kokarin komawa ta zauna taji wani irin gumi da zafi zafi me tsanani Yana tasowa daga cikin jikinta ta hadiye wani wahalallen yawu sbd bakinta dake gauraya da wani irin mummunan daci ta juyo da sauri tana share gumin fuskarta tana kallon jekadi da alamar tashin hankali da azaba tace"

Me Kika bani???
Me kikeson yimin???
Innalillahi wayyo Allah
Mutuwa zanyi azaba nakeji me tsanani....
Wurgi tayi da dankwalin kanta tana fige rigar jikinta cikin wata mummunar azabar dabata taba Jin makamanciyartaba arayuwarta ta zube qasa tana yagar jikinta tako Ina tana cewa"

Dan Allah ki taimakeni
Jikina cikinsa wuta ake hurawa
Dan Allah kibani ruwa
Zan mutu......

Shure Shure tafara jikinta na rikidewa jajir duk inda ta Sosa Kota fizga saiyayi wani irin kumburi kaman wuta ta koneta a gurin take ta haukace tana Shure shuren azaba tana ihun mummunan yanayi Jin takeyi kamar ruwan dalma na sirkuwa cikin jininta da bargonta..

Ihunta yasa jekadi juyawa ta fice daga dakin tareda rufewa ta waje ta cire qaton mukullin ta bar gurin Takoma can kofa daganan ta dauki hanyar zuwa gurin Anneti da akaiwa isarwada sakon zuwan jekadi.

Da murmushi Anneti ta kalli jekadi tace"

Barkan jekadi da dawowa lafiya,
Muna fatan anbaro Mana su maleek da mushransa tareda 'yayansa lafiya?

Da murmushi akan fuskan jekadi cikeda biyayya tace"

Alhmdlh muka barosu Inshallah.

Masha Allah to Yaya bakuwar mushrah?
Da ita kuka dawo dai Ina fata?

Sauke Kai jekadi tayi tace"

Da ita muka dawo saidai tariga ta wuce delah inshallah Bata biyo ta Nanba.

Masha Allah shikenan kije kihuta kin debo gajiyar Kai baquwa da dawowa da ita Dan Haka kije ki huta na tsawon kwanaki shida bakya buqatan fitowa kawo gaisuwa nabaki daman hutawa tukuicin Kai baquwar NURU da dawo da ita.

Cikin tsananin farin ciki jekadi tace"

Allah yaqarawa Anneti tsawon Rai da lafiya tareda girma, jekadi godia take sosai da matuka.

Murmushi kawai Anneti tayi tareda gyada kai tana cewa"

Amin.

Tashi jekadi tayi ta fice tana sake miqa godiya.

Tana fita hamdala ta sauke sbd hutunta zaibata ikon rike aikin gabanta da kyau su samu su gano asalin maqiyin maleek da nahaifinsa daya rasu Wanda suka shafe shekaru suna bibiya.

Sassanta NURU ta nufa inda takeda babban Palo da daki tareda makeken toilet dinta ware musamman acikin sassan na NURU tareda makeken dakin bayin sassan dake gefen nata.

Wanka tayi ta huta taci abinci sai alokacin tasamu ta rintsa dataga tafara aikata aikin kaleeb da maleek wainda zata iya bada ranta akansu.

Washe gari da sassafe ta saci jiki Babu me gani ta nufa gurin padima daukeda abinci cikin kwando tana Isa ta saka mukulli ta bude kofar ahankali tareda shigowa ta maida ta rufe ta ajiye kwandon hannunta tana kallon padima da kamanninta suka Gama sauyawa zuwa wani irin yanayi na tsoro da firgici tana fidda wani irin azababben Nishi dake fitar Mata daqyar.

Gyaran murya jekadi tayi tana kallonta batareda taji tausayinta ko dayaba aranta.

Daqyar cikin tsananin azaba padima ta dago idanuwanta dasuka kumbura suntum dama fuskarta Baki daya
Dukkaninta tayi jajir koina jininta.

Da hannu jekadi ta nuna Mata abincin data shigo dashi tana cewa"

Ga abinci Nan kici zai taimaka Miki kadan gurin samun karfin iya daukan dose din anjima.

Wasu siraran hawayen azabane suka silalo Mata ta gefen ido ta bude bakinta daya kunbura batako iya motsashi daqyar can qasa ta iya furta"

Meyasa? Meyasa akemin Haka????

Numfashi jekadi ta sauke ahankali tareda kallon padiman tace"

Da zakiyiwa kanki adalci tun Baki lalace da yawaba da kin Fadi inda Kika samo wannan garin da kanki Amma nasan burinki da gurbataccen tunaninki bazai Bari ki zabi hanyaba.,
Wannan shine aikin da kikaje gidan 'yar uwarki aikatawa akan mijinta kokuma nace akan MALEEK sbd qyashi da hassada sungama cinye zuciyarki gashi kin samu kanki acikin abinda tun kafin kizo duniya yake Dan haka batareda wahalarda sauran rayuwarkiba kifadamun inda wannan garin meriz din yafito yashigo hannunki.

Rintse ido tasake Yi cikin wahala wasu siraran hawayen suka sake gangaro Mata tanason fashewa da kuka batada hali sbd batada qarfin iyawa tanaji tana gani jekadi ta fice tasake rufeta cikin dakin dakeda tsananin duhu da zafi ta daga hannunta dake rawa ahankali ta wawuro abincin taga flatbread na alkama da dafaffuyar madara
Jikinta na tsananin rawa takai madarar Baki ta shanye tana Gama shanyewa tasaki cup din tana zare idanuwanta dake firfitowa kaman zasu tsinko jikinta ya tsananta rawa ta kife agurin tana ihun da baya fita ko kadan sbd dushewar murya cikin azaba Dan Ashe anxuba meriz din ciki.
Chapter 48 · 0% Book details