← Book details Two Different Wold Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 51 OF 79

Sashe 51

Two Different Wold Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read

M SHAKUR

4
Ko minti biyar baiyi da fita ba saiga yan aikin da Ammi ta aiko mata dashi, murmushi tayi taji hawaye nazuwan mata mema take tunani tanada mother in law maisonta haka taje tawani biyema Arham dat use her to make money yagina gidan marayun shi, fita tayi tabama mai rainon Arham tace "achanza mai kaya agoyashi, inya tashi saiki kawomin shi yasha nono, muje kiga dakinshi" tai maganan tanayin stairs mai rainon biyeda ita itakuma yar aiki ta zauna akasa afalon tana jiran fitowarta abata nata aikin.
Fitowa yayi da motarshi gateman yarufe kofar gidan, wayarshi yaciro daga aljihun shi dayaji tai karan notification, duba notification din yayi yaga notification ne na Mama food stuff drugs and what have you, wanan notification din tuntuni yake wayanshi duk karshen watan duniya yake mata cefane, ko tunanin Arham bai kawoba dan koda Arham koba Arham Mama yadauketa amatsayin mahaifiyarshi ce kuma har abada he will always see her that way nomatter what Arham did to him, tada motar yayi yana fasa zuwa office din wani pharmacy yaje yasayo mata yan magungunan ta sanan yawuce wani supermarket, ya lodo mata kayan abinci aka jeramai a boot sanan yawuce har anguwan su, yana zuwa yasami yaran anguwan as usual suka 000 shiganmai da kayan ciki suna murna suna fitowa yamusu kyaututtuka sanan yawuce ya shiga cikin gidan yana tafiya ahankali, sallama yayi ya shiga falon daidai Sadiya tafito daga corridor idanunta sunyi jajir sun kumbura suntum tana zuwa takarasa gabanshi harda dan gudunshi ta tsugunna agabanshi sai kuka abunku dayar kauye, anatse yace "Sadiya menene lafiya kike kuka haka? Maiya faru" kafin ya amsata yaji muryan wata mata dabai wayetaba tace "au zuwa kikayi kinamai kuka ko Sadiya keda akace ki shigo dashi" dagokai Waleed yayi ya kalli matar yanda yaga kamannin matar da Mama yasa yagane kanwar Umma ce itace mahaifiyar Sadiya, cikeda girmamawa yace "ina yini Umma" murmushi Maman Sadiya tayi tace "Waleed shigo kaji kekuma ki tashi ki kawomai abinsha" bin gefe Waleed yayi yashiga ciki har zuwa gaban dakin Mama, Maman Sadiya tabude kofa ta shiga Waleed yabiyota ciki, Mama yagani kwance kan gado kafar damanta ya kumbura yay suntum tundaga kan dan yatsa har zuwa cinya wando daya da rabine ajikinta kafar hagu ne dogon wandon shikuma na dama aka yake kafar, daidai gwuiwar kafar daman ta baya yafashe ruwa na fita, gabaki dayan Mama tafice hayyacinta ta rame tana kallon Waleed din dayama kasa motsi tsabagen shock tana murmushi, hannu tamikamai alamun yazo sanan tace "zo Waleed dina, zo karkaji komi kaji karkaji tsoro, bayamin wani ciwo kumburi ne kawai" cikin wani irin kuka Sadiya data kawo lemu a tray tana bayan Waleed tace "wlh karyane, Ya Waleed kafar Mama ciwo take na fitan hankali, kafan yafara mata zugi har suma takeyi tafice hayyacinta, taki bari akaita asibiti waisai Arham yazo inbaizo ba haka zata mutu adakin nan, takishan magani, abinci ma wani zubin sai Umma tamata dure takeci, mun kira Arham amman baya dauka koyama dauka baya sauraran mu yake kashe wayan, tun ranan dayamaka wulakanci Mama tamai fada yabar gidan bai kara dawowa ba amman Mama nason kashe kanta kanshi bayan tasan baidamu da itaba bazai dawoba" Sadiya takara rushewa da kuka itama Maman Sadiya kasa daurewa tayi saikawai tabi ta gefen Waleed tafita tana kuka dan batason tai kuka agaban yayar tata.
Ahankali Mama tace "zo Waleed, taho" ahankali Waleed ke daga kafarshi da bayajin shike iya motsata ba haryakai gaban gadon wani irin zubar da guwiwan shi yayi agaban gadon cikin wani irin muryan fada dake rawa sosai yace "Mama bakida......d....da....lafiya maisa baki kirani nazo ba, kinada number na namiki saving ta yanda kika gane kina kirana dashi, maisa bakisa ankirani ba Mama kika zauna da ciwo look at your leg, maisa baki kirani ba, eh......eh Mama"? Hannunshi Mama takama tarike gam takara kakalo murmushi tace "Waleed bayan duk abubuwan da d'ana yamaka na yaudara da cin amana kunya bazai taba iya barina nakiraka ba Waleed kayakuri" girgiza matakai Waleed yayi hawaye yazubo daga idanunshi haka Allah yayishi yanada mugun tausayi ko mace bazata nunamai tausayi ba, yamayi kuka amutuwan yaran gidan marayunshi balle wani nashi, fuskarshi yadaura kan hannunta yafashe da kuka sosai yace "Mama koda Arham koba Arham ke Mahaifiyata ce, amatasayin Mahaifiyata na daukeki and I will always yimiki abinda kowani d'a kema mahaifiyar shi Mama" yanda yake kuka akan hannunta yasa takai dayan hannunta tadaura kan saman kanshi tana shafawa alamun lallashi tace "Waleed kayakuri, inamai dada baka hakuri akan abinda Arham yamaka, wlh daidai da rana daya bantaba rainon Arham yazama abinda yazama ba, Arham kaga koni mahaifiyarshi baidamu daniba, yaron dako uwarshi bai kulawa da ita kagako zai iya komi aduniya amman bakomi, duniya nada mugun fadi da babu
wanda yasan a ina karshen ta yake, yaje zaiga......." da sauri Waleed yadago rinanun idanunshi yakai hannunshi kan bakinta yarufe yana girgiza matakai yace "karkimai baki Mama, karkimai baki" ture hannunshi tayi zatai magana saikuma tafashe da kuka tamaida idanuwanta kan silin tana wani irin kuka tana nuna kirjinta tace "ni Arham zai wulakanta, Arham dan Adam ne, butulu kacireshi daga rana kakaishi Inuwa yamaka dare, nakira Arham banda lafiya amman yaron nan yanuna mini banda amfani, Waleed na tsugunna ni dinan na tsugunna na haiho Arham, da ina nakudan shi har barkono aka zubamin a garwashi aka lullubeni da bargo na shaka ina tari inajin azaban yaji dukan yaron nan nafito, nasha azaban duniya kafin na haiho Arham amman shine zai wulakantani aduniya, Waleed wlh bazan yahewa Arham ba, bazan yafemai ba" tafashe dawani irin kuka dayasa Waleed yaji shima kukan yazomai, juyowa tayi ta kalleshi, murmushi tamai ta share hawayenta sanan tace "bani fuskarka" matso da fuskarshi yayi yakai mata, hannunta tasa ta sharemai hawayen tastas tana murmushi, sanan takama keyanshi tamai kiss agoshi abinda bata tabamai ba kenan tace "naji dadi daka ganni kafin Allah yakirani gidan gaskiya Waleed" kasa daurewa Waleed yayi sai kuka, sake gogemai hawayen tayi tace "Waleed kai bawan Allah ne sanan yaro nagari wanda kudin iyayenshi baisa kana isgilanci ba ko raina nakasa dakaiba, inaso karage kukan nan kaji, saurin kukanka da tausassan zuciyan da Arham yagama karanta yaga kanadashi yasa yacutar dakai dashi, karage kuka kaji sabida kaga nabar duniya babu mai kula dakai, kaga wanan kafar tawa Waleed" taidan shiru sanan tasakemai murmushi tace "bata tashi bace, saisa nasa Sadiya takira mahaifiyarta tazo duk narasu a hannun yar uwata da yarta tunda ni yanzu banda d'a" Waleed jiyayi heart dinshi yay breaking tasake fashewa da kuka, murmushi tamai tace "kadena kuka Waleed sabida inaso inna rasu ka tsaya ka tabbatar an suturtani da kyau ammin duk abinda yakamata dan nasa d'anda nahaifa bazaizoba yamin wayan nan abubuwan ba" fashewa da mugun kuka yayi yasake taushe mata baki yace "Mama babu abinda zai sameki ciwo ba mutuwa bane, kuma Arham zaizo namiki alkawari zan kirashi zakiga zaizo, amman yanzu bari nafara kaikai Zenith abaki kulawa tukunna kinji Mamana" wani irin ijiyan zuciya tasauke sanan tace "Waleed harnakoma ga ubangiji bazan taba manta abinda kama d'ana daniba, yau kuma zan roka maka Allah agabanka, ubangiji Allah ya sakamaka da sakkayya ta aljanna Firdaus, Waleed Allah ya kareka ya nisanta ka daga dukkannin shairuka sanan ya Sadaka da alkhairi, Allah yabaka mata tagari dakuma zuri'a dayyaba, Waleed irinku bakuda yawa aduniyan nan kai kyauta ne Allah yama iyayenka, ina rokon Allah daya biyaka duniya walahira, Waleed bissalam kaji d'ana danakeso" takarashe maganan ahankali tana murmushi wani irin kuka da Waleed yakeyi jikinshi har bari yake da kyar yay controlling kanshi yay shiru yatashi wardrobe dinta yabude hijabin dayagani yazaro yazo bakin gadon yadaga kanta yasa mata sanan ya ciccibeta bai damu da ruwan dake fitaba yana bata kayanshi yay wajen dakin da ita yanacema Maman Sadiya da Sadiya yace "kurufo gidan mu tafi asibiti" yay waje da ita, yana tafiya tana kan jikinshi tana kallon fuskarshi tana murmushi, bayan mota yabude ya kwantar da ita ya gyara mata riga da zaman wandon sanan ya maida kofan yarufe daidai su Mama sun fito, gaban motan shi ya nunamusu suka shiga su biyun shikuma yazauna mazaunin direba yaja motar dawani mahaukacin gudu, suna zuwa zenith dayake an sanshi sosai a asibitin yay housemanship dinshi yana zuwa suka karbeta akai wani daki dasu yabisu shima da gudu, yarike mata hannu gam yace "Mama na" murmushi tamai saikuma yaga hawaye ya ziraro ta gefen idanunta but still murmushi takemai kasa daurewa yayi yashiga kuka cikin rawan murya sosai yace "lemme call Arham Mama kinji, yanzun nan zaizo, yanzun nan I promise" yay maganan yana sakinta likitoci suka dukufa akanta yawuce yafita daga dakin, staff room dinsu yawuce ya shiga yawuce bayida sauri tap yabude ya wanke fuskarshi dataija sosai sanan ya jingina da bango, kafin ahankali yazura hannunshi cikin aljihu yaciro wayarshi, mantawa daduk wani fadanshi da Arham yayi yay dailing number Arham har wayan takatse bai dauka ba, saida yamai good 7miss calls ana 8th one dinne ya dauka, cikin wata irin dashshiyar murya dan yanacikin sex da Murja ne yakira yakai wayan kunnenshi awulakance yace "wai ya akayi ne? Idanma ka kirane danka sanar dani ka karbi offer dana baka na matsayin nani kazo office in person kafadi min" Waleed bai damu da maganganun shi ba yace "Arham something serious is going on yanzu is not time for our fight, Mama batada lpy sosai she's even admitted, please kazo kaganta kaji" wani mugun tsaki yaja yace "inzo in mata ubanme? Ai tuntuni Mama tai taking side dinta, she choose you and your money over ni danda ta haifa, so kuyi abuku gaka likita tana nemana namata me nidai tagama dukana kanka, kace nace bazan zoba gaka likita kamata abinda yakamata, please don't call me again am eating virgin pussy kasan ba pussy dayakai virgin one dadi" ya katse wayan, da sauri Waleed yasake dailing number dan ayanzu he doesn't mind har guwiwa zai iya samishi akasa dandai kawai yazo yaga mahaifiyar shi dan is obvious Mama na kewan danta, kira yayi harsau uku but yaji wayan akashe hakan yasa yasake wanke fuskarshi yafito daga bayin sanan yabude dakin yafito cikin asibitin, ganin wasu nurses da Dr na gudu suna shiga dakin da aka kwantar da Mama yasa da gudu yay dakin ya shiga shima, gani yayi likitoci almost 7 sun zagayeta ga nurses kafanta dake ruwa yanzu yafara jini irin jinin nan kaman na maruru yafashe jikinta nawani irin rawa tana kokarin magana but hakoranta sun datse, dawani irin gudu yay kanta yace "Mama!" hannu Mama tadaga tana mikamai jikinta na bari da sauri Waleed yay kanta yakama hannunta yarike, ahankali consultant din dake kanta yadago kanshi ya kalli sauran likitocin tareda girgiza musukai, damke hannunta gam Waleed yayi yana kuka mai sosarai yace "Mama tsaya kiji karki tafi ga Arham nan zuwa, gashinan zuwa go slow ne yarike shi yace kijirashi kinji Mama" hannunta tasake mikawa tadaura akan na Waleed, Waleed dayagama fita hayyacinshi yace "Mama me haka ki kallen dan Allah kinji, Mama" wani Dr ne yakama mai kafada kallon Dr yayi hakan yasa yagane sakon Dr, kallon Mama yayi saiya fashe kuma da kuka ahankali cikin wani low tone yace "La'ilaha illallah Muhammadur rasulullah" haka yadinga maimaita mata kafin bakinta yabude kadan ta iya furtawa sanan Allah ya karbi ranta hannayen Waleed nacikin nata, wani irin kuka Waleed yadingayi he can't believe Mama tarasu right infront of his eyes, yakai kusan 10min kuka yake sanan ya iya yay shiru ya share fuskarshi tass dan yatuna kalamanta nadazu _kadena kuka Waleed sabida inaso inna rasu ka tsaya ka tabbatar an suturtani da kyau ammin duk abinda yakamata dan nasa d'anda nahaifa bazaizoba yamin wayan nan abubuwan ba_
Ahankali yakai bakinshi kan goshinta ya sumbaceta yace "Allah ya gafarta miki Mama, Allah ya jikanki" sanan yaja zani ya lullubeta yay shiru yana kallonta, gabaki dayan jikinshi yamutu, gani yake suma tayi saisa ya tsaya yana jiran tabude idanu yamata magana.
_TWO DIFFERENT WORLD_
Chapter 51 · 0% Book details