Sashe 9
Tsutsar Nama Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Cikin gidan na shiga kamar yanda na saba, sai dai acan ƙasan raina ina ɗan jin tsoro-tsoro. Sosai na sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi ganin ban samu kowa a falo ba yau. Zuruf na shige ɗakinmu, in da na tarar da Bibaa kawai tana kallo a wayarta. Yanda bata amsa ko sallamata ba nima ban sake bi takanta ba. Wanka na farayi duk da kuwa cikin ƙyanƙyamin bayin nai haka, dan yanda ban wanke ba haka Bibaa itama bata wanke ba, sai ma datti da suka ƙara masa. Gudun kar lokacin sallah ya wuce min yasa ni saka doguwar riga kawai na saka hijjab na tada sallar. Na kai raka'a ta biyu ina sujidar ƙarshe kawai naji saukar duka kaina. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un wata irin azabace ta ratsa ni, amma na daure sosai na cigaba da sallata. Abinda kuma zai baki mamaki ba'a daina dukan nawa ba har na idar. Karo na farko kenan dana ɗaga hannu sama ina kuka da neman sakayya wajen UBANGIJI na, ina ƙoƙarin shafa addu'ar dai dai nan Abba ya shigo kamar wanda aka jeho.
“Haba Jalilah minene haka? Baki da hankali ne tana salla kina dukanta”. Ya faɗa a matuƙar hasale yana riƙe bulalar. Basu ba hatta ni sai da na shiga shock, dan nidai nasan ba yau ne karan farko da Mum take dukana ba a gidan nan. Hasalima ta dakeni a gabansa a lokuta barkatai amma bai taɓa cewa komai ba. Bama ni ba, hatta da Yaya Musaddiq yasha shan duka a wajen Mum, yanzu ne dai ta daina sai zaginsa da baƙar magana. Hakama Hafizzullah, sai dai duk ni na fisu shan wahala kasancewar akoda yaushe ni ina cikin gida a tare da su....
Mum ce ta katse min tunani na, dan cikin hargagi ta hayayyaƙo ma Abba a gabanmu. Idan ni bazata ji nauyina ba ai ya kamata taji nauyin su Babie kasancewar sa na mahaifinsu. Amma ko'a kwalar kwagirinta. Dan sai da takai ya koma bata haƙuri da lallashinta. Ni al'amarin nasu ma sai ya nema fasan kaina dan al'ajabi. Haka dai ya jata da ƙyar suka fice a ɗakin. Harara Baby ta watsa min da faɗin, “Shegiya mayya. To kurwar iyayenmu kur wlhy. Kuma indai Mum ce kaɗan ma ta miki wlhy, bari dai Abban ya fita duk da ma ko yana nan zata iya cigaba da cin ubanki, yanzu ɗin ma ta ƙyaleki ne kawai kiji da wannan tsamin jikin mtsowww makwaɗaitan banza da wofi anzo an cika mana gida an hanamu rawar gaban hantsi”. Daga haka ta fice kamar iska zata ɗibeta. Dan sam Baby bata da wani jikin kirki, ta girman amma na fita cikar halittar jiki sosai, wanda ma bai sani ba sai ya ɗauka nice babbarta. Sai da suka gama zageni tsaf ita da Bibaa suka fita sannan na fashe da kuka, dan illahirin jikina raɗaɗi yake min sosai. Da ƙyar na iya tashi na zare hijjab ɗina, abinka da farar fata wasu wajen ma har sun fashe. Cikin ƙanƙanin lokaci zazzaɓi mai zafi ya rufeni, haka na kwana ina makyarkyata ga ciwon jiki. Duk kiran da Yaya kemin a waya ban ɗaga ba, har ya gaji ya daina kiran, nasan dai ya zata ko barci nayi ne...
Humm wato Bily inada taurin kai fiye da yanda kike tunani. Zaki sha mamaki idan nace miki washe gari ma duk da dukan da naci haka na sake tsallakewa nai tafiyata wajen aiki batare dana ɗaga ko tsinke a gidan ba. Nasan dai nabar ƙura sosai, amma ko'a jikina nai gaba batare da na jira ko Yaya Musaddiq ba yau. Sai wajen 12 sai gashi yazo lokacin ina kwance zazzaɓi ya addabamin. Ruƙayya ce data lura da haka ta matsa min nasha paracetamol da ƙyar. Da Yaya Musaddiq ma yazo itace tazo ta kirani dan ta ɗan fita taci karo da shi shine tazo ta kamani muka fita.
Kallo ɗaya na masa na duƙar da kaina. Dan sosai naga ɓacin rai tattare da shi. Sai dai shima yanayin da ya ganni naga ya ɗan raunana fushin nasa, dan muna isowa inda yake sosai naji ya sauke ajiyar zuciya yana mai furzar da huci mai zafi.........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑵𝒊𝒏𝒆_
........Sai da Yaya yayma Ruƙayya dake shirin barin wajen godiya sannan ya juyo gareni. Kallo ya ƙare min daga sama har ƙasa sannan cikin yanayin fusata ya ce, “Miyasa kike da taurin kai ne wai Samraah?. Yanzu ga abinda kikayi jiyan wace riba kikaci tunda kinfi kowa sanin halin matar nan?. Amma ke da yake ba'a taɓa faɗa miki kiji shine yau ma kika kuma. To ai gashi nan ta sake ƙulla miki sharri kala-kala ita da yaranta. Tun ɗazu ina gidan basu barni na fito ba sunata min masifa akan wai ni nake sakaki. Har Abban na saka sharaɗin ko dai ki ajiye aiki ki dawo ki cigaba da aikin gidan ko kuma ya aurar da ke ga wa wanda ita Mum ɗin ta kawo. Idan yaga shi zai barki yin aiki ki cigaba, amma albashinki dolene kema ki dinga rabawa biyu daga yanzu kina basu rabi ana haɗawa ayi cefane. Nama kawo masa batun Mansoor yaƙi ya saurareni sam. Wai shi bai san da wani Mansoor ba kuma bazai aura masa ke ba, wanda Mum ta kawo kawai ya sani kuma shi zai bawa dan yaron nada tarbiyya sosai, kuma shi ya gamsu da hakayensa....”
Kuka na sakar masa mai taɓa zuciya. Hakan ya sakashi yin shiru ya gagara cigaba da magana ya zubamin ido kawai. Kusan mintuna uku ina kukan sosai kafin ya kai zaune kusa dani. A jikinsa ta gefe ya sakani kawai shima hawayen na cika masa ido. “Amma kin san bana son kuka ko Samraah”. Ya faɗa muryarsa na rawa. Ɗagowa nai a karo na farko ina kallonsa. Sai kuma na sake fashewa da wani sabon kukan ganin yanda idanunsa suka kaɗa sukai jazur gasu cike da hawaye. “Yaya ya kake so nayi, shike nan haka zamu lalace a yima waɗanda basu taɓa jin tausayinmu ba biyayya. Kullum burin matar nan wulaƙanta mu, Yaya tun fa ban isa iya aiki ba nake bautar gidan nan, amma ko sau ɗaya ba'a taɓa min adalci ba idan nai kuskure a yafe min. Kullum kuma a banayi nake. Su Baby na kwance. Yaya na gaji wlhy, ji nake kamar na gudu na bar gidan nan kawai....”
“Shiii!!! Karna sake jin irin wannan maganar a bakin ki. Samraah ai wuya bata kisa. Da ace tana yi wlhy da bamu kai haka a rayuwa ba. Duk can baya baki ƙosa ba sai yanzu da aski yazo gaban goshi. Kwana nawa ma ya rage miki a gidan. Bama ke ba da kike mace zaki tafi gidan aure hatta ni da Hafizzullah in sha ALLAHU mun kusa bar musu gidansu. Gara kawai na tada gini na kamar yanda kike bada shawara mu koma can kawai. Amma dan ALLAH ina roƙonki kada ki sake maimaita abinda kika faɗa yanzu. idan kin gudu ina zaki? Ki daure ki cigaba da musu abinda suke so. Watarana sai labari ai. Maganarki kuma da Mansoor na yanke shawarar zuwa wajen dangin mahaifinmu, duk da sun watsar damu basu taɓa waiwayen mu ba tunda ɗan uwansu yabar duniya zanje na roƙesu su shiga wannan maganar a baki wanda kike so tunda dama sune ai da wannan alhakin ba Abba ɗin ba. Ki tashi kuma muje asibiti dan jikinki akwai zazzaɓi sosai.”
Ɗagowa nai zanyi magana ya girgiza min kai alamar kar nace komai. Dole na haɗiye kuwa. Ruƙayya ya kira da wayata, yace ta tattare masa kayana dan ALLAH. Cikin mintuna kaɗan ko sai gata. Da taimakonta muka fita inda mashin ɗinsa yake. Ta taimaka min na hau muka wuce dan Mansoor yau baizo office ba sunje wani aiki Jigawa. Sai da muka fara tsayawa a camix aka dubani kafin mu ƙarasa gida dan nata roƙonsa kan bazanje asibiti ba, sanin da yay min na ƙin jinin asibitin shima yasa ya barnin mukaje camix ɗin kawai aka bani magani.
“Haba Jalilah minene haka? Baki da hankali ne tana salla kina dukanta”. Ya faɗa a matuƙar hasale yana riƙe bulalar. Basu ba hatta ni sai da na shiga shock, dan nidai nasan ba yau ne karan farko da Mum take dukana ba a gidan nan. Hasalima ta dakeni a gabansa a lokuta barkatai amma bai taɓa cewa komai ba. Bama ni ba, hatta da Yaya Musaddiq yasha shan duka a wajen Mum, yanzu ne dai ta daina sai zaginsa da baƙar magana. Hakama Hafizzullah, sai dai duk ni na fisu shan wahala kasancewar akoda yaushe ni ina cikin gida a tare da su....
Mum ce ta katse min tunani na, dan cikin hargagi ta hayayyaƙo ma Abba a gabanmu. Idan ni bazata ji nauyina ba ai ya kamata taji nauyin su Babie kasancewar sa na mahaifinsu. Amma ko'a kwalar kwagirinta. Dan sai da takai ya koma bata haƙuri da lallashinta. Ni al'amarin nasu ma sai ya nema fasan kaina dan al'ajabi. Haka dai ya jata da ƙyar suka fice a ɗakin. Harara Baby ta watsa min da faɗin, “Shegiya mayya. To kurwar iyayenmu kur wlhy. Kuma indai Mum ce kaɗan ma ta miki wlhy, bari dai Abban ya fita duk da ma ko yana nan zata iya cigaba da cin ubanki, yanzu ɗin ma ta ƙyaleki ne kawai kiji da wannan tsamin jikin mtsowww makwaɗaitan banza da wofi anzo an cika mana gida an hanamu rawar gaban hantsi”. Daga haka ta fice kamar iska zata ɗibeta. Dan sam Baby bata da wani jikin kirki, ta girman amma na fita cikar halittar jiki sosai, wanda ma bai sani ba sai ya ɗauka nice babbarta. Sai da suka gama zageni tsaf ita da Bibaa suka fita sannan na fashe da kuka, dan illahirin jikina raɗaɗi yake min sosai. Da ƙyar na iya tashi na zare hijjab ɗina, abinka da farar fata wasu wajen ma har sun fashe. Cikin ƙanƙanin lokaci zazzaɓi mai zafi ya rufeni, haka na kwana ina makyarkyata ga ciwon jiki. Duk kiran da Yaya kemin a waya ban ɗaga ba, har ya gaji ya daina kiran, nasan dai ya zata ko barci nayi ne...
Humm wato Bily inada taurin kai fiye da yanda kike tunani. Zaki sha mamaki idan nace miki washe gari ma duk da dukan da naci haka na sake tsallakewa nai tafiyata wajen aiki batare dana ɗaga ko tsinke a gidan ba. Nasan dai nabar ƙura sosai, amma ko'a jikina nai gaba batare da na jira ko Yaya Musaddiq ba yau. Sai wajen 12 sai gashi yazo lokacin ina kwance zazzaɓi ya addabamin. Ruƙayya ce data lura da haka ta matsa min nasha paracetamol da ƙyar. Da Yaya Musaddiq ma yazo itace tazo ta kirani dan ta ɗan fita taci karo da shi shine tazo ta kamani muka fita.
Kallo ɗaya na masa na duƙar da kaina. Dan sosai naga ɓacin rai tattare da shi. Sai dai shima yanayin da ya ganni naga ya ɗan raunana fushin nasa, dan muna isowa inda yake sosai naji ya sauke ajiyar zuciya yana mai furzar da huci mai zafi.........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑵𝒊𝒏𝒆_
........Sai da Yaya yayma Ruƙayya dake shirin barin wajen godiya sannan ya juyo gareni. Kallo ya ƙare min daga sama har ƙasa sannan cikin yanayin fusata ya ce, “Miyasa kike da taurin kai ne wai Samraah?. Yanzu ga abinda kikayi jiyan wace riba kikaci tunda kinfi kowa sanin halin matar nan?. Amma ke da yake ba'a taɓa faɗa miki kiji shine yau ma kika kuma. To ai gashi nan ta sake ƙulla miki sharri kala-kala ita da yaranta. Tun ɗazu ina gidan basu barni na fito ba sunata min masifa akan wai ni nake sakaki. Har Abban na saka sharaɗin ko dai ki ajiye aiki ki dawo ki cigaba da aikin gidan ko kuma ya aurar da ke ga wa wanda ita Mum ɗin ta kawo. Idan yaga shi zai barki yin aiki ki cigaba, amma albashinki dolene kema ki dinga rabawa biyu daga yanzu kina basu rabi ana haɗawa ayi cefane. Nama kawo masa batun Mansoor yaƙi ya saurareni sam. Wai shi bai san da wani Mansoor ba kuma bazai aura masa ke ba, wanda Mum ta kawo kawai ya sani kuma shi zai bawa dan yaron nada tarbiyya sosai, kuma shi ya gamsu da hakayensa....”
Kuka na sakar masa mai taɓa zuciya. Hakan ya sakashi yin shiru ya gagara cigaba da magana ya zubamin ido kawai. Kusan mintuna uku ina kukan sosai kafin ya kai zaune kusa dani. A jikinsa ta gefe ya sakani kawai shima hawayen na cika masa ido. “Amma kin san bana son kuka ko Samraah”. Ya faɗa muryarsa na rawa. Ɗagowa nai a karo na farko ina kallonsa. Sai kuma na sake fashewa da wani sabon kukan ganin yanda idanunsa suka kaɗa sukai jazur gasu cike da hawaye. “Yaya ya kake so nayi, shike nan haka zamu lalace a yima waɗanda basu taɓa jin tausayinmu ba biyayya. Kullum burin matar nan wulaƙanta mu, Yaya tun fa ban isa iya aiki ba nake bautar gidan nan, amma ko sau ɗaya ba'a taɓa min adalci ba idan nai kuskure a yafe min. Kullum kuma a banayi nake. Su Baby na kwance. Yaya na gaji wlhy, ji nake kamar na gudu na bar gidan nan kawai....”
“Shiii!!! Karna sake jin irin wannan maganar a bakin ki. Samraah ai wuya bata kisa. Da ace tana yi wlhy da bamu kai haka a rayuwa ba. Duk can baya baki ƙosa ba sai yanzu da aski yazo gaban goshi. Kwana nawa ma ya rage miki a gidan. Bama ke ba da kike mace zaki tafi gidan aure hatta ni da Hafizzullah in sha ALLAHU mun kusa bar musu gidansu. Gara kawai na tada gini na kamar yanda kike bada shawara mu koma can kawai. Amma dan ALLAH ina roƙonki kada ki sake maimaita abinda kika faɗa yanzu. idan kin gudu ina zaki? Ki daure ki cigaba da musu abinda suke so. Watarana sai labari ai. Maganarki kuma da Mansoor na yanke shawarar zuwa wajen dangin mahaifinmu, duk da sun watsar damu basu taɓa waiwayen mu ba tunda ɗan uwansu yabar duniya zanje na roƙesu su shiga wannan maganar a baki wanda kike so tunda dama sune ai da wannan alhakin ba Abba ɗin ba. Ki tashi kuma muje asibiti dan jikinki akwai zazzaɓi sosai.”
Ɗagowa nai zanyi magana ya girgiza min kai alamar kar nace komai. Dole na haɗiye kuwa. Ruƙayya ya kira da wayata, yace ta tattare masa kayana dan ALLAH. Cikin mintuna kaɗan ko sai gata. Da taimakonta muka fita inda mashin ɗinsa yake. Ta taimaka min na hau muka wuce dan Mansoor yau baizo office ba sunje wani aiki Jigawa. Sai da muka fara tsayawa a camix aka dubani kafin mu ƙarasa gida dan nata roƙonsa kan bazanje asibiti ba, sanin da yay min na ƙin jinin asibitin shima yasa ya barnin mukaje camix ɗin kawai aka bani magani.