Sashe 23
Tsutsar Nama Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Sosai yasha barci mai lafiya a safiyar ta yau kasancewar a daren jiya ya jima bai kwanta ba. Dan tunda ya dawo massalaci sallar asuba da Ummiensa kawai yayi waya ya sake komawa ya kwanta. Bai tashi ba sai yanzu babu jimawa. Wanka kawai yayi tare da gyara jikinsa cikin wando 3quater mai laushi kalar baƙi da rigarsa fara da adon baƙi kaɗan itama mai laushi. Dogon hannune da ita tare da hula. Sai dai ya saki hular a bayansa, sannan bai saka zip ɗin rigar ba. Hakan ya bama farar singlate ɗinsa damar fitowa sosai tare da ɗamammen cikinsa da har kana iya ganin kwanciyar gurayen kansa dake nuna shi matsayin mutum mai tsananin motsa jiki. Yau dai bai ɗaure gashin ba, sai dai yasha gyara sosai dan daga shi har siririn kwantaccen sagensa sai uban ƙyalli da ƙamshi sukeyi. Ga gashin ya ɗan sakko masa har kafaɗa kaɗan. Magana ta gaskiya babu wanda zai kalla bawan ALLAHn nan ya yarda wai ya haɗa jini da baƙaƙen fata. Dan sam baya kammani da su sai dai fatarsa da tai ɗan diff ba kamar na fararen dake kasancewa jazur ko fari fat ba. Amma shi yanayin da fatar tasa take ma sai ya ƙara masa wani ƙyawu na musamman. Kai tsaye ga coffee machine ɗin sa da ke a falon ya nufa. Cikin mintina kaɗan ya haɗa coffee. Ƙyaƙyƙyawan mug ɗinsa na zallar farin glass ya ɗauka ya tsiyaya fin rabi a ciki. Sannan ya tako a hankali yana kaiwa bakinsa zuwa cikin falon sosai. Furucin daya fito daga cikin television dake aiki a falon ya sashi karkata hankalinsa ga tvn. Dai-dai nan Hayatu ya shigo kamar wanda aka koro. Kaɗan ya juyo ya kallesa cikin yanayin nan nasa na rashin sakewa, sai kuma ya sake maida kansa ga tvn yana sake kai mug ɗin kan ɗan ƙaramin bakinsa ya zuƙi coffee ɗin duk da zafin da yake da shi.
Hayatu da gaba ɗaya hankalinsa ke a tashe ya ce, “Sir kaga abinda ke faruwa kuw......” sauran maganar ta maƙale sakamakon saukar idonsa akan tvn shima. Da sauri ya ɗan yi baya kamar wanda ke shirin faɗuwa. Ya dai samu nasarar dafe hannun kujerar dake kusa da shi yana bin ogan nasa da ya ƙarasa ya zauna cikin kujera ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya da kallo. Yasan halinsa sarai akan dakiyar masifa dayin biris da abu kamar bai damar ba. Amma magana ta gaskiya wannan bai kamata ai biris ba. Zama yay ya samarwa kansa nutsuwa. Kafin ya furta, “Amma Sir mizai sa Baba prof.. zuwa Kano a yau har yayi hira da yarinyar nan ne? Kodai ya amince da batun buɗe companyn yanzu? Wlhy ni du kaina ya kulle ma”.........✍️
_Ni ma dai mai ɗaukar rahoton neman ruɗar fani ɗin kuke Hayatu PA.🤥🤔_
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚_
.......Kamar yanda Hayatu yasan bazaice komai ba baice ɗin ba kuwa. Sai ma aikin shan coffee ɗinsa da yake hankali kwance idanun nasa dai a tvn dan har an fara program ɗin. Gaba ɗaya hirar anyita ne akan abinda ya shafi harkar ilimi a Nigeria. Da rawar da su malamai ɗin suke takawa domin ganin matarbar ilimin ta dawo hayyacinta da ga mutuwar tsayen da tayi musamman daya kasance tun daga tushene. Dan yanzu secondary schools tafi kowace gaɓa lalacewa a harkar karatu, in ba makarantar kuɗi zaka kai yaranka ba sai a hankali. Gashi kuma Sakandire ɗin nan ne ake ganin tamkar mahaɗar dake riƙe da kowanne reshen ilimin dan anan ne ake karatu tuƙuru cikin halin ƙuruciya da babu wasu damuwoyin fara fuskantar ƙalubalen rayuwa irin na girma. Wannan hira ta matuƙar ɗaukar hankalin mutane, inda ta haifar da cecekuce sosai tare da yaba ma prof... ɗin. Dan tun kafin a kammalata saƙwanni sun cika kowane dandalin sada zumunta na wannan gidan tv da rediyo. Yayinda wasu ke tattaunawa a dandilansu na sada zumunta. A cikin awa ɗaya da akai da Prof.. K/Mashi an amsa harda wayoyin mutane, ya kuma bada cikakkun amsoshi masu jan hankali da suka sake birge mutane da ganin kimarsa da girmansa. Duk da a baya ana zaginsa akan yanda yake aiki tuƙuru ma kudancin Najeriya ɗin kasancewarsa mazaunin can shi da gaba ɗaya zuri'arsa. Dan wasu na ganin a komai nasa bama ya alaƙanta kansa da arewa sam, tamkar ma baida wani alaƙar dasu, musamman idan yana sukar ƴan siyasar arewan da ƙalubalantar shuwagabannin yankin.
Koda aka kammala ma babu alamar Maash zaice wani abu. Zuwa yanzu dai kansa na jingine da kujerar idanunsa a lumshe. Ta ƙasan ido Hayatu ke kallonsa da nazartarsa. Sai kuma a hankali ya furta, “Sir miza'a kawo maka breakfast?”.
Shiru babu alamar zaima motsa balle ya tanka masa. Sai kuma dai cikin motsa lips da ƙyar ya furta, “Waka ɗora akan aikin bincike akan yarinyar nan?”.
Ƙasa Hayatu yay da kansa, cikin girmamawa sosai ya amsa da, “Da kaina nayi Sir. Dama abinda nazo kawo maka kenan. Sai kuma wanda zai ringa bibiyar tata ne kuma ina kan nazari. In sha ALLAHU daga nan zuwa yamma zan kawoshi shima.”
Yana daga kwancen ya ɗan buɗe idanunsa yana kallonsa. Hayatu ya ƙara rissinar da kansa yana ɗan murmushi, dan yasan abinda yay ɗin ya faranta ran ogan nasa koda bai fito ta faɗa ba. Ci gaba yay da faɗin, “Sunanta Samraah Abdul-wahab Gwarzo. Wasu kan kirata Sam-G. Tana da yaya Musaddiq da ƙani Hafizzullah. Musaddiq ɗin makanike ne, shike riƙe da rayuwarsu, ƙanin nata kuma na jami'ar Umaru Musa Yar'adua dake Katsina yana karatu. Iyayensu sun jima da rasuwa, a hannun Uncle ɗinsu suke tun suna ƙanana. Akwai wani yaro Mansoor da ko yaushe suna tare shine zata aura dan har maganar iyaye ta shiga. A zahiri Samraah bata da hayaniya ba kuma sabgar kowa take shigaba sai in itace taso hakan. Sai dai kuma tana da tsiwa a wasu lokutan musamman ga wanda ya shigar mata hanci. A shekarun baya kaɗan ta fara rubuce-rubuce kan abubuwa masu muhimmanci musamman da suka shafi ƙananun yara mata dake tallace-tallace a tituna. Sai dai tunda ta fara wannan aikin ta ɗan rage hakan. Bincikena kuma ya tabbatar min tanada fans sosai, dan a duka shafukanta akwai fallowers dake fallowing ɗinta sosai. Na tabbatar da yanda suke jin daɗin karatun rubuce-rubucen nata ne ta hanyar comments da suke mata. A office kuwa tana fannin ƙananun ma'aikata ne. A ɓangaren rediyo ta fara aiki kuma. Sai dai ƙwazonta da yanda program ɗin data bada shawarar samarwa akan matasa ya amsu, ya saka suka maidata itace mai gabatar da program ɗin. Da kuma a iya rediyo kawai akeyinsa, amma yanayin karɓuwarsa yasa suka koma gabatar da shi har da television, sannan shi MD ɗin su ne ya bata power sosai a al'amarin. Shiyyasa ma ake zargin yana sonta ne duk da yasan akwai alaƙa mai ƙarfi tsakaninta da shi wancan yaron Mansoor, amma har yanzu bai san iyayensa sunje gidansu ba ma har anyi maganar aure.” ɗan matsawa yay gabansa yana yunƙurin ajiye tab.. ɗin dake a hannunsa yana cigaba da faɗin, “Nayi fallowing duka shafukanta, gashi ko zaka duba”.
Hayatun ya ɗan kalla sai kuma ya ɗauke idanun nasa. A daƙile ya ce, “Ba buƙata. Ka kammala komai dan zuwa jibi maybe zamu wuce. Ka tura ma MD nasu takardar amsa gayyatar da tai min, sai dai kar ya wuce gobe” daga haka ya miƙe. Har ya shige bedroom ɗin sa Hayatu da kansa ke ƙasa na binsa da kallo. Sai kuma yaja numfashi tare da sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi yana kaiwa zaune cikin lallausar kujerar dake a falon. Tagumi ya zuba da hannaye biyu, gefe ɗaya mamakin komai yake yi, wani gefe kuma na ayyana masa akwai abinda ogan nasa ke shiryawa. Kuma tabbas da wahala ace zai kasance mai daɗi, yana tausayin yarinyar nan, dan ta taroma kanta match. Bashi da zaɓin daya wuce cika umarni, dan haka ya ɗauka tab.. ɗinsa. A take yay kiran wani tare da buƙatar number ɗin MD na gidan tvn na AlHERI. Ko mintuna biyar ba'a cikaba kuwa sai ga saƙon Number ɗin ya shigo masa. A take ta shirya text message ya tura musu kamar yanda Maash ya umarcesan.....
Yayanmu nima fa ka fara ban olo gaskiya😌🥺🥺.
🌟(☉。☉)!(☉。☉)!(☉。☉)🌟
Hayatu da gaba ɗaya hankalinsa ke a tashe ya ce, “Sir kaga abinda ke faruwa kuw......” sauran maganar ta maƙale sakamakon saukar idonsa akan tvn shima. Da sauri ya ɗan yi baya kamar wanda ke shirin faɗuwa. Ya dai samu nasarar dafe hannun kujerar dake kusa da shi yana bin ogan nasa da ya ƙarasa ya zauna cikin kujera ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya da kallo. Yasan halinsa sarai akan dakiyar masifa dayin biris da abu kamar bai damar ba. Amma magana ta gaskiya wannan bai kamata ai biris ba. Zama yay ya samarwa kansa nutsuwa. Kafin ya furta, “Amma Sir mizai sa Baba prof.. zuwa Kano a yau har yayi hira da yarinyar nan ne? Kodai ya amince da batun buɗe companyn yanzu? Wlhy ni du kaina ya kulle ma”.........✍️
_Ni ma dai mai ɗaukar rahoton neman ruɗar fani ɗin kuke Hayatu PA.🤥🤔_
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚_
.......Kamar yanda Hayatu yasan bazaice komai ba baice ɗin ba kuwa. Sai ma aikin shan coffee ɗinsa da yake hankali kwance idanun nasa dai a tvn dan har an fara program ɗin. Gaba ɗaya hirar anyita ne akan abinda ya shafi harkar ilimi a Nigeria. Da rawar da su malamai ɗin suke takawa domin ganin matarbar ilimin ta dawo hayyacinta da ga mutuwar tsayen da tayi musamman daya kasance tun daga tushene. Dan yanzu secondary schools tafi kowace gaɓa lalacewa a harkar karatu, in ba makarantar kuɗi zaka kai yaranka ba sai a hankali. Gashi kuma Sakandire ɗin nan ne ake ganin tamkar mahaɗar dake riƙe da kowanne reshen ilimin dan anan ne ake karatu tuƙuru cikin halin ƙuruciya da babu wasu damuwoyin fara fuskantar ƙalubalen rayuwa irin na girma. Wannan hira ta matuƙar ɗaukar hankalin mutane, inda ta haifar da cecekuce sosai tare da yaba ma prof... ɗin. Dan tun kafin a kammalata saƙwanni sun cika kowane dandalin sada zumunta na wannan gidan tv da rediyo. Yayinda wasu ke tattaunawa a dandilansu na sada zumunta. A cikin awa ɗaya da akai da Prof.. K/Mashi an amsa harda wayoyin mutane, ya kuma bada cikakkun amsoshi masu jan hankali da suka sake birge mutane da ganin kimarsa da girmansa. Duk da a baya ana zaginsa akan yanda yake aiki tuƙuru ma kudancin Najeriya ɗin kasancewarsa mazaunin can shi da gaba ɗaya zuri'arsa. Dan wasu na ganin a komai nasa bama ya alaƙanta kansa da arewa sam, tamkar ma baida wani alaƙar dasu, musamman idan yana sukar ƴan siyasar arewan da ƙalubalantar shuwagabannin yankin.
Koda aka kammala ma babu alamar Maash zaice wani abu. Zuwa yanzu dai kansa na jingine da kujerar idanunsa a lumshe. Ta ƙasan ido Hayatu ke kallonsa da nazartarsa. Sai kuma a hankali ya furta, “Sir miza'a kawo maka breakfast?”.
Shiru babu alamar zaima motsa balle ya tanka masa. Sai kuma dai cikin motsa lips da ƙyar ya furta, “Waka ɗora akan aikin bincike akan yarinyar nan?”.
Ƙasa Hayatu yay da kansa, cikin girmamawa sosai ya amsa da, “Da kaina nayi Sir. Dama abinda nazo kawo maka kenan. Sai kuma wanda zai ringa bibiyar tata ne kuma ina kan nazari. In sha ALLAHU daga nan zuwa yamma zan kawoshi shima.”
Yana daga kwancen ya ɗan buɗe idanunsa yana kallonsa. Hayatu ya ƙara rissinar da kansa yana ɗan murmushi, dan yasan abinda yay ɗin ya faranta ran ogan nasa koda bai fito ta faɗa ba. Ci gaba yay da faɗin, “Sunanta Samraah Abdul-wahab Gwarzo. Wasu kan kirata Sam-G. Tana da yaya Musaddiq da ƙani Hafizzullah. Musaddiq ɗin makanike ne, shike riƙe da rayuwarsu, ƙanin nata kuma na jami'ar Umaru Musa Yar'adua dake Katsina yana karatu. Iyayensu sun jima da rasuwa, a hannun Uncle ɗinsu suke tun suna ƙanana. Akwai wani yaro Mansoor da ko yaushe suna tare shine zata aura dan har maganar iyaye ta shiga. A zahiri Samraah bata da hayaniya ba kuma sabgar kowa take shigaba sai in itace taso hakan. Sai dai kuma tana da tsiwa a wasu lokutan musamman ga wanda ya shigar mata hanci. A shekarun baya kaɗan ta fara rubuce-rubuce kan abubuwa masu muhimmanci musamman da suka shafi ƙananun yara mata dake tallace-tallace a tituna. Sai dai tunda ta fara wannan aikin ta ɗan rage hakan. Bincikena kuma ya tabbatar min tanada fans sosai, dan a duka shafukanta akwai fallowers dake fallowing ɗinta sosai. Na tabbatar da yanda suke jin daɗin karatun rubuce-rubucen nata ne ta hanyar comments da suke mata. A office kuwa tana fannin ƙananun ma'aikata ne. A ɓangaren rediyo ta fara aiki kuma. Sai dai ƙwazonta da yanda program ɗin data bada shawarar samarwa akan matasa ya amsu, ya saka suka maidata itace mai gabatar da program ɗin. Da kuma a iya rediyo kawai akeyinsa, amma yanayin karɓuwarsa yasa suka koma gabatar da shi har da television, sannan shi MD ɗin su ne ya bata power sosai a al'amarin. Shiyyasa ma ake zargin yana sonta ne duk da yasan akwai alaƙa mai ƙarfi tsakaninta da shi wancan yaron Mansoor, amma har yanzu bai san iyayensa sunje gidansu ba ma har anyi maganar aure.” ɗan matsawa yay gabansa yana yunƙurin ajiye tab.. ɗin dake a hannunsa yana cigaba da faɗin, “Nayi fallowing duka shafukanta, gashi ko zaka duba”.
Hayatun ya ɗan kalla sai kuma ya ɗauke idanun nasa. A daƙile ya ce, “Ba buƙata. Ka kammala komai dan zuwa jibi maybe zamu wuce. Ka tura ma MD nasu takardar amsa gayyatar da tai min, sai dai kar ya wuce gobe” daga haka ya miƙe. Har ya shige bedroom ɗin sa Hayatu da kansa ke ƙasa na binsa da kallo. Sai kuma yaja numfashi tare da sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi yana kaiwa zaune cikin lallausar kujerar dake a falon. Tagumi ya zuba da hannaye biyu, gefe ɗaya mamakin komai yake yi, wani gefe kuma na ayyana masa akwai abinda ogan nasa ke shiryawa. Kuma tabbas da wahala ace zai kasance mai daɗi, yana tausayin yarinyar nan, dan ta taroma kanta match. Bashi da zaɓin daya wuce cika umarni, dan haka ya ɗauka tab.. ɗinsa. A take yay kiran wani tare da buƙatar number ɗin MD na gidan tvn na AlHERI. Ko mintuna biyar ba'a cikaba kuwa sai ga saƙon Number ɗin ya shigo masa. A take ta shirya text message ya tura musu kamar yanda Maash ya umarcesan.....
Yayanmu nima fa ka fara ban olo gaskiya😌🥺🥺.
🌟(☉。☉)!(☉。☉)!(☉。☉)🌟