← Book details Tsutsar Nama Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 58

Sashe 30

Tsutsar Nama Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*

*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_

_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_

_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒇𝒊𝒗𝒆_

.......A karon farko na sauke ajiyar zuciya. Sai kuma a hankali na ce, “Kayi haƙuri Sir an samu kuskuren fahimta ne kawai saboda ni bakamin bayanin komai ba. Kuma nima banƙi amsar ƙyautar tasa da wata manufa bane, kawai dai albashin da ake bani ya wadatar dani”.
       “Humm kuma gashi ya dawo min da abinda ya bakin akan lallai na maida miki. Na kuma baki haƙuri tare da roƙonki kan ki amsa dan ALLAH.”
    “Gaskiya bazan amsa ba Sir kuyi hakuri. Dan Yayana zai ɓata min rai matuƙa. Nima kuma a karan kaina ma nayima kaina alƙawari a gafarce ni”.
       Shiru kawai yay yana kallona. Nasan mamakin taurin kaina yake yi. Dan har fuskarsa ta fara nuna jin haushi. Sai dai bai sake cewa komai ba akan batun face, “Okay ba damuwa. Sai batun mutuminki, a jiya PA ɗinsa ya turo mana takardar amsar gayyatar da kikai masa. Tare da bamu zaɓin lokaci amma kada mu wuce yau. Adai taƙaice yanzu haka ya tabbatar mana zai shigo kafin 11am, amma awa ɗaya kacal zai yi da mu. Dan haka yanzu zaki je ki kasance cikin shiri, nama su Tsanyawa magana akan su shirya kayan aiki da zauren da zaman zai kasance. A yanzu haka kuma sun fara in sha ALLAH”.
          Har cikin raina sai da naji zantukansa na dukana. Amma sai na dake na amsa masa da to kawai. Shima bai sake cewa komai ba ya miƙamin takardar gabansa. “Ki nazarci wannan, idan kina da wata idea sai ki ƙara, nan da awa ɗaya ki kawo min na gani. Zaki iya tafiya”.
       Zaram na miƙe kuwa na fice abina ko waiwayensa banyi ba. Zuciyata kuwa sai wani irin kai-kawo take. Ina fita kuma na dallama office ɗin harara. Ɗagowar da zanyi muka haɗa ido da Bashira, ashe tana tsaye a wajen bata tafi ba. Ko takanta banbi ba dan ba'itace a gabana ba nai wucewata a raina ina faɗin (Ballagaza kazar sakarai). Koda na koma office duk yanda naso samun damar tunani hakan bai yiwu ba. Dan su Ruƙayya tuni sun baibayeni da surutu akan ɗan ta'addan mutumin can mai kisan kai dako sunansa ban riƙe ba. Bana kuma fata ko ra'ayin riƙewar ma. Dan haka nafi maida hankali akan aikin gabana fiye da hirar tasu dan dama ba tofawa nake ba. A haka har lokacin da MD ya ban ya cika. Miƙewa nai na fita maida masa file ɗin. Yanda naga yana faman washe baki na tabbatar da abinda nai ɗin ya masa. Dan a take ya ɗaga waya yay kiran sauran wanda zamuyi aikin tare. Bayani ya sake mana ta yanda zamuyi komai ya ƙayatar ya kuma sake ɗaga kimar gidan namu. Ni sai ma naji kamar na makesa. Dan na fara saka MD a cikin jerin sunayen mutane mayun kuɗi. Jiba yanda yake rawar ƙafa tamkar zai ci da ka. Yana sallamar mu muka fice zuwa inda aka gyara domin gabatar da shirin. Makeup ɗin da akace na ɗanyi ƙi nai, sai ma shashsha musu ƙamshi nake famar yi. Sai da MD ya dinga lallashina sannan na ɗan sake saka fauda da ɗan lips gloss, daga haka ban sake bi takan komai ba na nema waje na zauna.
Chapter 30 · 0% Book details