Sashe 4
Tsutsar Nama Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
......A gurguje nake faman shiryawa saboda makarar da naso nayi. Ba kuma komai ya jawo min hakan ba sai sharaɗin girka breakfast ga masu gidan a kullum kafin na fita bisa umarnin Mom bayan gyara ko ina. Ban isa nace bazanyi ba, dan na fahimci hanyar da zata tuzguɗe ɗan aikin nawa take nema. Dan haka na tsarama kaina time table ta yanda bazan cutu ba. Kullum ƙarfe huɗu na asuba na tashi, zan shiga kitchen na ɗaura breakfast. Inayi ina ɗan wasu aikin gyara gidan har na kammala, dana gama na maida hankali ga sauran ayyukan, ALLAH na taimakona kafin ai kiran sallar farko zaka samu na kammala komai, da Yaya Musaddiq ya fahimta ma sai ya zam shima yana tasowa muyi tare dandanan saina kammala nai shiri. To yau an samu akasi ne da alama Yaya ya makara, dan har na kammala bai shigoba, gashi ma har na gama shirina. Nayi ƙyau sosai cikin baƙar abayar dana saka, nai rolling veil ɗin ta da ya sake fiddoni tsamm kamar wata ɗiyar larabawa. A ɓangaren ƙyawun fuska dana jiki babu abinda zance sai Alhmdllh, sai dai ban taɓa jin alfahari ko son yin ɗagawa da wannan baiwar da ALLAH yay min ba. Nakan gode masa ta hanyar suturta kaina da ƙyaƙyƙyawar shiga, dan kullum cikin dogon hijjabi nake da nose mask. Dan ƙaryane kace ka ganni babu nose mask a fuska. A lokacin dazan fara gabatar da shirin nan a sashen tv ansha gumurzu dani a ranar farko dan har hawaye saida nayi saboda ciresa, dole dai na haƙura daga ƙarshe ma toshe idona da eyeglasses sannan na iya gabatar da shirin, a hakanma ina jin kaina kamar ba daidai ba.
Kamar kullum mask ɗina na saka, sai dai yau baƙi ne, yay min ƙyau sosai dan ƙyawawan fararen idanuna masu girma da cikar gashi kawai ake iya gani. Cikin takun nutsuwata na fito, ga wani ƙamshi mai sanyi yana tashi a jikina, sai dai bamai ƙarfi bane, dan sai ka kasance a kusa dani sosai zaka iya jinsa yanda ya kamata. Sauri nake, dan haka bana fatan haɗuwa da kowa na gidan. Sai da na leƙo na tabbatar babu kowa a falon sannan na ƙarasa fitowa. Nan ma da sanɗa na fita, inayi ina waigen bayana. Ban sami nutsuwa ba saida na ganni a waje, na sauke nannauyar ajiyar zuciya ina sakin murmushi, bag ɗita mai zubin school bag na rataya hannunta guda a bayana, ɗakin yaya na fara leƙawa, sai muka kusa cin karo dan shima yana niyyar fitowa ne.
“Kandala ƴar jaridan Yayanta”.
Ya faɗa cikin tsokana yana mun murmushi. Murmushin nima na mayar masa ina ɗan rufe fuskata da tafin hannuna. Sai kuma na janye ina ɗan ɓata fuska da faɗin, “Ai ni fushi ma nake da kai yaya. Na manta nai maka murmushi ma.”
Cikin dariya ya ce, “Oh oh Tom ayi haƙuri Ƴar ficika, nasan laifin Yaya dai rashin shigowa taya aiki, wlhy jiya na matuƙar gajiya ne a gareji, shiyyasa tunda na samu na kwanta ko juyi banyi ba sai kawai naji ana sallame salla. Dan yau ma sai a ɗaki nayi tawa dan abin kunya”.
Dariya na ƙyalƙyale da ita sosai saboda yanda yay da fuska kamar wani ɗan yaro. Sai kuma na kalla agogo da sake kallonsa. A zabure na ce, “Uhm Yaya zan makara. Ni dai taho muje ka saukeni, dan yau a mashin ɗinka zanje office, ina son na baka wani labari a hanya”.
Babu musu yace min muje, saboda karna makara bai shiga gidan ya gaidasu kamar yanda ya saba ba. Ya kuma san sai yasha masifa akan haka ɗin, amma yafi buƙatar farin cikina. Cike da farin ciki muka bar ƙofar gidan tamkar bamu da wata damuwar rayuwa. Maganar da nace masa zamuyi na fara masa. Ba komai bane face batun fara gininsa, dan ina son a fara ya samu yay aure. Bai dai ce dani komai ba face murmushi kawai har muka isa, a ƙofar gate ya ajiyeni. Har lokacin fuskarsa da murmushi ya kalleni. Sai kuma ya ɗan ja fasali da harɗe hannayensa a ƙirjinsa yana kallona.
“Samraah!”.
Ya kirayi sunana da tsantsar kulawa. Amsa masa nai nima da girmamawa. Numfashi ya sake furzarwa da ɗan duƙar da kansa ƙasa kamar mai nazari, sai kuma ya ɗago yana sake kallona. “Samraah inaga ba batun gini ya kamata muyi ba yanzu. Kamata yay ace mu tattali abinda muke samu domin kayan aurenki. Kin girma Samraah, kin kammala karatunki cikin aminci, ga aiki kin samu cikin sauƙi, kina da Mansoor a hannu, a ganina batun aure ya kamata ace kunyi da shi yanzu kafin ma lokacin da Abba ya baki ya cika. Kin san dai halin Mom basai na faɗa miki ba, wannan shirun da kikaga tayi wlhy bazai zama na alkairi ba. Gara mu fiskanci zahiri. Wannan ƙaramin jikin naki yabar kwasarki ba baya kike komawa ba shekaru ne ke ƙaruwa. mutanen wajene kawai suke miki kallon ƴar ƙarama ganinki ƴar ficit. Ni nawa batun mai sauƙi ne, namiji ne ni, konan da shakara goma bazan tsufa da aure ba ai. Ga Hafizzullah yanzu ya fara karatunsa, kamata yay har sai shima ya kammala koda zan yi batun wani aure, sai nake ganin kamar hakan zai fi, ni dama ba wata budurwa ba a ƙasa”. Ya ƙare maganar da zolaya.
Baki na kumbura cikin ƴar shagwaɓa nace, “Yaya ni duk ban amshi wannan ƙorafin naka ba sam. Kadai bari mu samu lokaci mu zauna mu tattauna. Amma batun bazakai aure ba sai nayi ko Hafiz ya kammala makaranta duk baima taso ba. In dai Dan budurwar ce zan maka, amma bazan bari ka cigaba dama waɗan can mutanen bauta ba. Kura da shan bugu gardi da ƙwace kuɗi. Wannan lokacin ya wuce muma yanzu munsan kammu”.
Kansa kawai ya girgiza, nasan kuma ba komai ya sakashi yin hakan ba sai ganin yanda na ƙarasa maganar a hasale. A bayyane fushina da zafin mariƙanmu ya gama bayyana. Maimakon yace wani wani sai kawai yaymin nuni da gate alamar naje ciki. Banyi musu ba nai masa sallama na nufi shiga ciki ina kumbura baki da fiki-fiki da idanu najin haushi........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑭𝒊𝒗𝒆_
Kamar kullum mask ɗina na saka, sai dai yau baƙi ne, yay min ƙyau sosai dan ƙyawawan fararen idanuna masu girma da cikar gashi kawai ake iya gani. Cikin takun nutsuwata na fito, ga wani ƙamshi mai sanyi yana tashi a jikina, sai dai bamai ƙarfi bane, dan sai ka kasance a kusa dani sosai zaka iya jinsa yanda ya kamata. Sauri nake, dan haka bana fatan haɗuwa da kowa na gidan. Sai da na leƙo na tabbatar babu kowa a falon sannan na ƙarasa fitowa. Nan ma da sanɗa na fita, inayi ina waigen bayana. Ban sami nutsuwa ba saida na ganni a waje, na sauke nannauyar ajiyar zuciya ina sakin murmushi, bag ɗita mai zubin school bag na rataya hannunta guda a bayana, ɗakin yaya na fara leƙawa, sai muka kusa cin karo dan shima yana niyyar fitowa ne.
“Kandala ƴar jaridan Yayanta”.
Ya faɗa cikin tsokana yana mun murmushi. Murmushin nima na mayar masa ina ɗan rufe fuskata da tafin hannuna. Sai kuma na janye ina ɗan ɓata fuska da faɗin, “Ai ni fushi ma nake da kai yaya. Na manta nai maka murmushi ma.”
Cikin dariya ya ce, “Oh oh Tom ayi haƙuri Ƴar ficika, nasan laifin Yaya dai rashin shigowa taya aiki, wlhy jiya na matuƙar gajiya ne a gareji, shiyyasa tunda na samu na kwanta ko juyi banyi ba sai kawai naji ana sallame salla. Dan yau ma sai a ɗaki nayi tawa dan abin kunya”.
Dariya na ƙyalƙyale da ita sosai saboda yanda yay da fuska kamar wani ɗan yaro. Sai kuma na kalla agogo da sake kallonsa. A zabure na ce, “Uhm Yaya zan makara. Ni dai taho muje ka saukeni, dan yau a mashin ɗinka zanje office, ina son na baka wani labari a hanya”.
Babu musu yace min muje, saboda karna makara bai shiga gidan ya gaidasu kamar yanda ya saba ba. Ya kuma san sai yasha masifa akan haka ɗin, amma yafi buƙatar farin cikina. Cike da farin ciki muka bar ƙofar gidan tamkar bamu da wata damuwar rayuwa. Maganar da nace masa zamuyi na fara masa. Ba komai bane face batun fara gininsa, dan ina son a fara ya samu yay aure. Bai dai ce dani komai ba face murmushi kawai har muka isa, a ƙofar gate ya ajiyeni. Har lokacin fuskarsa da murmushi ya kalleni. Sai kuma ya ɗan ja fasali da harɗe hannayensa a ƙirjinsa yana kallona.
“Samraah!”.
Ya kirayi sunana da tsantsar kulawa. Amsa masa nai nima da girmamawa. Numfashi ya sake furzarwa da ɗan duƙar da kansa ƙasa kamar mai nazari, sai kuma ya ɗago yana sake kallona. “Samraah inaga ba batun gini ya kamata muyi ba yanzu. Kamata yay ace mu tattali abinda muke samu domin kayan aurenki. Kin girma Samraah, kin kammala karatunki cikin aminci, ga aiki kin samu cikin sauƙi, kina da Mansoor a hannu, a ganina batun aure ya kamata ace kunyi da shi yanzu kafin ma lokacin da Abba ya baki ya cika. Kin san dai halin Mom basai na faɗa miki ba, wannan shirun da kikaga tayi wlhy bazai zama na alkairi ba. Gara mu fiskanci zahiri. Wannan ƙaramin jikin naki yabar kwasarki ba baya kike komawa ba shekaru ne ke ƙaruwa. mutanen wajene kawai suke miki kallon ƴar ƙarama ganinki ƴar ficit. Ni nawa batun mai sauƙi ne, namiji ne ni, konan da shakara goma bazan tsufa da aure ba ai. Ga Hafizzullah yanzu ya fara karatunsa, kamata yay har sai shima ya kammala koda zan yi batun wani aure, sai nake ganin kamar hakan zai fi, ni dama ba wata budurwa ba a ƙasa”. Ya ƙare maganar da zolaya.
Baki na kumbura cikin ƴar shagwaɓa nace, “Yaya ni duk ban amshi wannan ƙorafin naka ba sam. Kadai bari mu samu lokaci mu zauna mu tattauna. Amma batun bazakai aure ba sai nayi ko Hafiz ya kammala makaranta duk baima taso ba. In dai Dan budurwar ce zan maka, amma bazan bari ka cigaba dama waɗan can mutanen bauta ba. Kura da shan bugu gardi da ƙwace kuɗi. Wannan lokacin ya wuce muma yanzu munsan kammu”.
Kansa kawai ya girgiza, nasan kuma ba komai ya sakashi yin hakan ba sai ganin yanda na ƙarasa maganar a hasale. A bayyane fushina da zafin mariƙanmu ya gama bayyana. Maimakon yace wani wani sai kawai yaymin nuni da gate alamar naje ciki. Banyi musu ba nai masa sallama na nufi shiga ciki ina kumbura baki da fiki-fiki da idanu najin haushi........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑭𝒊𝒗𝒆_