Sashe 24
Tsutsar Nama Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Sam nutsuwa bata ɗan dawo jikina ba sai da aka kammala duka program ɗin. Bayan an ɗauke camara daga kanmu na sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi ina mai lumshe ido. Ɗan kallona prof.. yay a kaikaice sai kuma yay ɗan murmushin manya yana miƙewa. Yana fita a ɗakin shi da MD sauran ƴan uwana ma'aikata sukayo kaina. Ruwa aka fara bani nasha, na sake samun nutsuwa sannan nima na miƙe. Muna daga harabar gidan ni da Mansoor dake lallaɓani muje muci abinci aka aiko kiranmu. Dole cikin muka koma. Inda muka samu dukkan ma'aikatan da suka bada gudunmawa a program ɗin har ƴan bayan fage a office ɗin MD. Zama mukayi kamar kowa muma. Daga haka Prof.. ya fara mana bayanin godiya, tare da sanar mana dalilinsa na gabatar da wannan program ɗin cikin gaggawa haka. Sosai muka nuna gamsuwarmu. Musamman ma ni da kaina duk ke a ɗaure da farko. Ƙyauta dukanmu ya danƙa ma kowa a envelope ɗinsa. Daga haka yay mana godiya muma muna masa. Sai dai me ni sam hankalina ya gagara tsayawa waje guda akan hakan. Kallo na fara bin sauran ƴan uwana da shi, kafin na miƙe zaram kamar wadda akaima allura nabi bayansa da sauri. Mansoor na ƙoƙarin tsaidani da son jin ina zanje bamma sauraresa ba na fice da sassarfa. Isowata yayi dai-dai da buɗema prof.. mota zai shiga. Ga mutanensa zagaye da shi kamar zasu iya hana mutuwa ɗaukarsa. Amma ko'a jikina nai sallama kaina tsaye. Su duka juyowa sukai suna kallonna musamman MD da yay rakkiya tare da Prof....
Fuska ɗauke da murmushi Prof.. ya ce, “A'a ɗiyata ko kinyi mantuwa ne?”.
Ƙasa nai da kaina ina ɗan murmushin ƙarfin hali. Kafin cikin ladabi da dakiyata na ce, “A'a ranka ya daɗe. Dama uhm....” sai kuma nai shiru na kasa cigaba da faɗa ganin yanda suka tsatstsareni da idanu su duka. Murmushi mai sauti Prof... yayi yana sakin murfin motar ya juyi gareni da ƙyau. “Daughter yi maganarki ƙofa a buɗe take ai. Ko mu koma gefe ne?”.
Da sauri na ce, “A'a Sir ba sai munje ko'ina ba. Mun gode sosai da karamcinka garemu, amma dan ALLAH kayi haƙuri zan dawo da wannan dan ana biyana albashi akan aikina, kuma yana wadatar dani”.
Bashi ba hatta MD ina ganin yanda yay wani irin sororo yana kallona. Ni dai na ɗauke kaina ina miƙama yaronsa daya raba mana envelope ɗin. Ganin ya tsaya yana kallona bashi da niyyar amsa na ɗaura masa kan kayan hannunsa na juya a nutse na bar wajen. Ina jin yanda idanunsu sukai min riiiii aka. Amma ban waiwayo ba. Cin karo muka kusan yi da Mansoor da alamu suka nuna biyoni yayi. Na ɗan ja da baya ina faɗin, “Ya salam I'm sorry ban san ka taho bane”.
“Babu damuwa” ya faɗa yana kallon hannuna. Fahimtar hakan yasa kai tsaye nace masa “Na mayar musu ne?”.
“Mi ɗin?”.
Ya faɗa cikin waro idanunsa sosai waje. Bakina da ke cikin face mask na tura gaba da faɗin, “Yo abinda suka bamu. Ni gaskiya bana ra'ayi dan zuciyata sam bata ma kwanta waje ɗaya ba. Ta yaya mutum zai taso rana tsaka ya ce muyi hira da shi babu wani goron gayyata babu notes sannan ya kuma kawo wani abu ya bamu wai matsayin ƙyauta. Dan ALLAH kai baka ji abin banbarakwai ba? Shine fa wanda kwanaki akaita kace-nace ɗin nan akansa game da abinda ya faɗa akan shugabannin arewa. Gashi kuma da bakinsa ya faɗa shi haifaffen jihar Kano ne. Amma bai ragi balle ragowa wajen sukar mana mutane kamar wani maƙiyinmu”.
Idanu kawai Mansoor ya zuba min kamar mai nazari. Ya buɗe baki zaiyi magana sai ga MD ya iso kamar a fusace. Dan cikin yanayi kamar faɗa-faɗa ya ce, “Samraah sameni a office”.
Sai da na taɓe bakina dake a cikin face mask sannan na amsa masa da to ciki-ciki. Yana juya baya kuma na bisa da harara. Ƙin tafiya nai har sai da Mansoor ya mun magana. Batare da shima na tanka masa ba na wuce fuu nabi bayansa........✍️
*_“Amma Samraah miyyasa kika ƙi amsa bayan kuma kema kin gamsu da bayanin da yay muku na dalilin hirar? Sannan kin siffantashi da mutane kirki a halittar jiki da yanayinsa, kuma bayanansa sunja hankalin mutane da yawa a yau ɗin har hakan ya sake ɗaga darajar gidan tvn ku?”._*
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚-𝑶𝒏𝒆_
.......Humm Bily a zahirance banda wani dalilin yin hakan kamar yanda kowa zai iya gani ko fahimta. Sai dai ni a ƙasan zuciyata ina jin dole-dolene bai kamata na amsa koma miye ɗin ba. Dan babu dalilin hakan bisa hujjoji da dama. Amma ban sani ba ko kema zaki iya fahimtar hujjar tawa a yanzu. Ko kuma sai anan gaba cikin abinda zai zo a labarin nan nawa. Dan a yanzu kam tabbas babu wani dalilin da nima zan tilasta miki gamsuwa dani. Amma dai muje zuwa ofishin MD dake kirana.
(Babu musu na jinjina mata kai, amma magana ta gaskiya al'amarin wannan Sam-G ɗin taku yana ɗan rikitani. A ido zaka iya mata kallon like innocent people. Sai dai a ɗan zaman da nai da ita na fahimci taƙadarar kanta ce. Sannan akwai taurin kai yana jinjirin jaki. Kar dai na cikaku da zance ku muje zuwa dan jin yaya ta kaya a offishin MD)
Tsaye na samesa yana faman kai kawo a tsakkiyar office ɗin nashi. Sai faman furzar da huci yake kamar wani bajimin rago. Ko ɗar banji ba a raina na rafka sallamata. Juyowa yay yana kallona da idanunsa da suka kaɗa sosai. Kamar wanda ke shirin dukana ya wani zaburo kaina har sai da na ɗan ja da baya ina waro manyan idanuna waje.
“Samraah kin san mi kikayi kuwa? Kin san wanene wannan mutumin kuwa? Kin san ƙyautar mi ya baki kuwa? Amma kika watsa masa ƙasa a ido ta hanyar maida masa bayan ya fifitaki sama da kowa. Kuɗi duk ya bama sauran 50-50k, amma ke makullin mota ya baki batare da ko dubawa kinyi ba kika ɗauka kika maida masa...”
“Mata fa dai?”.
Na tambaya da iya gaskiya ta. Shima cike da ƙwarin gwiwa ya amsa min da “Yes Mota Samraah. Shiyyasa a kullum nake faɗa miki ke ɗin mai sa'a ce dear”.
Kaina na ɗan girgiza da murmushin basarwa, na ce, “Humm to amma Sir mi zanyi da shi idan na riƙe? Sannan wace amsa zan bama iyayena idan sun tambayen a ina na samu mota? A shi karan kansa mi ma zaisa ya mana irin wannan ƙyautar haka dan kawai munyi hira da shi?”.
“Tab ɗin, wlhy yarinyar nan baki da hankali...” ya faɗa cikin ƙunar rai, a take na sake tamke fuskata dan kalmar tasa ta mun matuƙar zafi a zuciya. Duk yanda naso na shanye na gagara hakan, kai tsaye nace masa, “Sir minene abin rashin hankali anan? Bayan kuma na faɗa maka hujjata. Wannan fa rayuwata ce”
Wani irin tsayawa yay duka hannayensa riƙe da ƙugunsa kawai yana kallona tamkar ya samu television. Ni kam na sake fuskewa kamar ban san yanayi ba. Na fahimci takaicina ne ya maƙureshi ya hana shi cigaba da magana. Dan a fusace ya sa ƙafa ya tunkuɓar da flower base ɗin da akai ado da ita a office ɗin, sannan ya ce, “Samraah out. Get out of my office now..”
Ko kallonsa banyi ba na juya nai ficewata. In ma ca yay na bar Company ɗin gaba ɗaya daga yau banda matsala da hakan. Ko takan Mansoor banbi ba nai ficewata gaba ɗaya daga gidan. Napep na tare zuwa garejin su Yaya Musaddiq. Na samu suna shirin shiga sallar azhar, sai dai shi Yaya bai kai ga tafiya ba yana ƙoƙarin ɗaura alwala ne. Tun kafin na ƙarasa inda yake na fahimci ya zuba min ido.
“Lafiya kike?”.
Ya faɗa dai-dai ina isowa gabansa shi kuma yana wanke ƙafarsa. Mai makon amsa sai na tura masa baki. Kansa ya girgiza kawai yana sake faɗin, “Je can ki zauna muyi salla to, idan na dawo sai kiyi taɓarar”. Daga haka ya wuce ya barni a wajen dan ya kammala alwalar...
💫´⊙ω⊙💫⊙ω⊙💫⊙ω⊙`💫
Fuska ɗauke da murmushi Prof.. ya ce, “A'a ɗiyata ko kinyi mantuwa ne?”.
Ƙasa nai da kaina ina ɗan murmushin ƙarfin hali. Kafin cikin ladabi da dakiyata na ce, “A'a ranka ya daɗe. Dama uhm....” sai kuma nai shiru na kasa cigaba da faɗa ganin yanda suka tsatstsareni da idanu su duka. Murmushi mai sauti Prof... yayi yana sakin murfin motar ya juyi gareni da ƙyau. “Daughter yi maganarki ƙofa a buɗe take ai. Ko mu koma gefe ne?”.
Da sauri na ce, “A'a Sir ba sai munje ko'ina ba. Mun gode sosai da karamcinka garemu, amma dan ALLAH kayi haƙuri zan dawo da wannan dan ana biyana albashi akan aikina, kuma yana wadatar dani”.
Bashi ba hatta MD ina ganin yanda yay wani irin sororo yana kallona. Ni dai na ɗauke kaina ina miƙama yaronsa daya raba mana envelope ɗin. Ganin ya tsaya yana kallona bashi da niyyar amsa na ɗaura masa kan kayan hannunsa na juya a nutse na bar wajen. Ina jin yanda idanunsu sukai min riiiii aka. Amma ban waiwayo ba. Cin karo muka kusan yi da Mansoor da alamu suka nuna biyoni yayi. Na ɗan ja da baya ina faɗin, “Ya salam I'm sorry ban san ka taho bane”.
“Babu damuwa” ya faɗa yana kallon hannuna. Fahimtar hakan yasa kai tsaye nace masa “Na mayar musu ne?”.
“Mi ɗin?”.
Ya faɗa cikin waro idanunsa sosai waje. Bakina da ke cikin face mask na tura gaba da faɗin, “Yo abinda suka bamu. Ni gaskiya bana ra'ayi dan zuciyata sam bata ma kwanta waje ɗaya ba. Ta yaya mutum zai taso rana tsaka ya ce muyi hira da shi babu wani goron gayyata babu notes sannan ya kuma kawo wani abu ya bamu wai matsayin ƙyauta. Dan ALLAH kai baka ji abin banbarakwai ba? Shine fa wanda kwanaki akaita kace-nace ɗin nan akansa game da abinda ya faɗa akan shugabannin arewa. Gashi kuma da bakinsa ya faɗa shi haifaffen jihar Kano ne. Amma bai ragi balle ragowa wajen sukar mana mutane kamar wani maƙiyinmu”.
Idanu kawai Mansoor ya zuba min kamar mai nazari. Ya buɗe baki zaiyi magana sai ga MD ya iso kamar a fusace. Dan cikin yanayi kamar faɗa-faɗa ya ce, “Samraah sameni a office”.
Sai da na taɓe bakina dake a cikin face mask sannan na amsa masa da to ciki-ciki. Yana juya baya kuma na bisa da harara. Ƙin tafiya nai har sai da Mansoor ya mun magana. Batare da shima na tanka masa ba na wuce fuu nabi bayansa........✍️
*_“Amma Samraah miyyasa kika ƙi amsa bayan kuma kema kin gamsu da bayanin da yay muku na dalilin hirar? Sannan kin siffantashi da mutane kirki a halittar jiki da yanayinsa, kuma bayanansa sunja hankalin mutane da yawa a yau ɗin har hakan ya sake ɗaga darajar gidan tvn ku?”._*
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚-𝑶𝒏𝒆_
.......Humm Bily a zahirance banda wani dalilin yin hakan kamar yanda kowa zai iya gani ko fahimta. Sai dai ni a ƙasan zuciyata ina jin dole-dolene bai kamata na amsa koma miye ɗin ba. Dan babu dalilin hakan bisa hujjoji da dama. Amma ban sani ba ko kema zaki iya fahimtar hujjar tawa a yanzu. Ko kuma sai anan gaba cikin abinda zai zo a labarin nan nawa. Dan a yanzu kam tabbas babu wani dalilin da nima zan tilasta miki gamsuwa dani. Amma dai muje zuwa ofishin MD dake kirana.
(Babu musu na jinjina mata kai, amma magana ta gaskiya al'amarin wannan Sam-G ɗin taku yana ɗan rikitani. A ido zaka iya mata kallon like innocent people. Sai dai a ɗan zaman da nai da ita na fahimci taƙadarar kanta ce. Sannan akwai taurin kai yana jinjirin jaki. Kar dai na cikaku da zance ku muje zuwa dan jin yaya ta kaya a offishin MD)
Tsaye na samesa yana faman kai kawo a tsakkiyar office ɗin nashi. Sai faman furzar da huci yake kamar wani bajimin rago. Ko ɗar banji ba a raina na rafka sallamata. Juyowa yay yana kallona da idanunsa da suka kaɗa sosai. Kamar wanda ke shirin dukana ya wani zaburo kaina har sai da na ɗan ja da baya ina waro manyan idanuna waje.
“Samraah kin san mi kikayi kuwa? Kin san wanene wannan mutumin kuwa? Kin san ƙyautar mi ya baki kuwa? Amma kika watsa masa ƙasa a ido ta hanyar maida masa bayan ya fifitaki sama da kowa. Kuɗi duk ya bama sauran 50-50k, amma ke makullin mota ya baki batare da ko dubawa kinyi ba kika ɗauka kika maida masa...”
“Mata fa dai?”.
Na tambaya da iya gaskiya ta. Shima cike da ƙwarin gwiwa ya amsa min da “Yes Mota Samraah. Shiyyasa a kullum nake faɗa miki ke ɗin mai sa'a ce dear”.
Kaina na ɗan girgiza da murmushin basarwa, na ce, “Humm to amma Sir mi zanyi da shi idan na riƙe? Sannan wace amsa zan bama iyayena idan sun tambayen a ina na samu mota? A shi karan kansa mi ma zaisa ya mana irin wannan ƙyautar haka dan kawai munyi hira da shi?”.
“Tab ɗin, wlhy yarinyar nan baki da hankali...” ya faɗa cikin ƙunar rai, a take na sake tamke fuskata dan kalmar tasa ta mun matuƙar zafi a zuciya. Duk yanda naso na shanye na gagara hakan, kai tsaye nace masa, “Sir minene abin rashin hankali anan? Bayan kuma na faɗa maka hujjata. Wannan fa rayuwata ce”
Wani irin tsayawa yay duka hannayensa riƙe da ƙugunsa kawai yana kallona tamkar ya samu television. Ni kam na sake fuskewa kamar ban san yanayi ba. Na fahimci takaicina ne ya maƙureshi ya hana shi cigaba da magana. Dan a fusace ya sa ƙafa ya tunkuɓar da flower base ɗin da akai ado da ita a office ɗin, sannan ya ce, “Samraah out. Get out of my office now..”
Ko kallonsa banyi ba na juya nai ficewata. In ma ca yay na bar Company ɗin gaba ɗaya daga yau banda matsala da hakan. Ko takan Mansoor banbi ba nai ficewata gaba ɗaya daga gidan. Napep na tare zuwa garejin su Yaya Musaddiq. Na samu suna shirin shiga sallar azhar, sai dai shi Yaya bai kai ga tafiya ba yana ƙoƙarin ɗaura alwala ne. Tun kafin na ƙarasa inda yake na fahimci ya zuba min ido.
“Lafiya kike?”.
Ya faɗa dai-dai ina isowa gabansa shi kuma yana wanke ƙafarsa. Mai makon amsa sai na tura masa baki. Kansa ya girgiza kawai yana sake faɗin, “Je can ki zauna muyi salla to, idan na dawo sai kiyi taɓarar”. Daga haka ya wuce ya barni a wajen dan ya kammala alwalar...
💫´⊙ω⊙💫⊙ω⊙💫⊙ω⊙`💫