← Book details Sanadin Besty Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 17

Sashe 14

Sanadin Besty Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Murmushin jin daɗi Zeenat ta yi domin kuwa yadda ya ke ma ta yawo da hannayen shi a cikin ta ba ƙaramin daɗi ta ke ji ba, tun daga tsakiyar kanta har tafin ƙafarta saƙon yake isa, zamewa ta yi ƙasa ta zauna ganin haka ne ya sa ya sakko shi ma ya fara bata abinci ita ma tana bashi, ko kunya ba ta ji ba, a nata ganin ai anyi mai wuyar tun da an yi auren, sai da suka ƙoshi sannan ya kwashe plates din zuwa kitchen ta shiga toilet ta kuskure baki, yana shigowa shima ya je ya wanke baki, kafin ya fito ya iske har ta kwanta, wutar ɗakin ya kashe ya kunna mara haske sosai sannan ya haura saman gadon ya janye bargon da ta rufa, hijabin jikinta ya cire ai kuwa idanun shi suka ci karo da ƙirjinta, tuni idanunsa suka kaɗa, kuma turaren da ta shafa ya fara fisgar shi, lumshe idanu Zeenat ta yi cike da jin daɗi, Allah-Allah ta ke yi ya jefa ƙwallo a raga ta ji ya yake, shima gaba ɗaya ya gigice a haka ya rabata da komai na jikin ta ya ci-gaba da ma ta wasanni masu tada hankali, ganin ba za ta iya jurewa ba ya sa ta fara mayar mai da martani, bai ma kula da abin da ta ke mai ba saboda gaba ɗaya ya fice a hayyacin shi, ga wani soyayyarta da ke ƙara ƙaruwa, a haka ya samu ya shige ta, sai dai ya tsaya jimm jin ƙofar a buɗe, ko da an yi wasu kwaskwarima hakan ba zai hana shi gane macen da aka taɓa buɗewa ba, wani nauyi ya ji a zuciyar shi, ji ya ke kamar ya fasa ihu amma ina ya kasa ƙarasawa, haka ya zare jikin shi, kamo shi ta ƙara yi suka haɗa ido, nan da nan- ya ji komai ya gudu a ƙwaƙwalwarsa, ci gaba ya yi da sarrafa ta yadda ya ke so ita kuma sai jin daɗi ta ke yi na ganin komai ya tafi yadda ta tsara..

Taimakon gaggawa likitan ya fara ba ma Fadeelah, sai da suka kwashe tsawon awa É—aya sannan aka samu numfashinta ya dawo, ban da kuka ba abin da Anty ta ke yi tana faÉ—in:

"Shikenan Fadeelah kin cuce ni, yanzu sakayyar da za ki min kenan? Duk irin yadda na ke faɗi-tashi a kanki amma sai da kika ɗauko mana abin kunya? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Allah na tuba ", haka Anty ta ke ta maimaitawa cikin baƙin ciki da ƙunar zuciya, ita kaɗai ta san me ta ke ji a cikin zuciyarta, da ƙyar wata nurse ta ja ta gefe ta rarrashe ta sannan ta tsagaita da kukan, jira kawai take yi Fadeelah ta farka ta faɗa ma ta wanda ya aikata ma ta wannan aika-aikar, ko da ya ke ai ba laifin shi ba ne, da ba ta ba da kanta ba ai hakan ba za ta faru ba, ga shi yanzu ta ja musu masifa suna zaman-zaman su cikin rufin asiri. Sai da Fadeelah ta kwashe awanni wajen biyar sannan ta farka, cikin firgici da ihu, bubbuga gadon take yi tana miƙewa jin hakan ya sa Anty da ke bakin ƙofa ƙarasowa da sauri, tana shiga ta tarar da ita a wannan yanayin tsawa ta daka ma ta tare da faɗin:

"Dalla ki mana shiru munafuka, koma mene ne ai ke kika jawo, tun da kin zama ballagaza jaka, wallahi Fadeelah kin cuce mu", ta ƙarasa maganar kuka na kufce ma ta, ita ma Fadeelah kukan take yi ta na cewa:

"Tabbas Anty na cuci rayuwata, Adnan ya cuce ni, Innalillahi wa inna ilaihir rajiun wannan wace irin masifa ce?" Matsowa Anty ta yi gadan-gadan kamar zata dake ta ko me ta tuna kuma sai ta fasa, juya wa ta yi ta tsaya a dai-dai saitin window hawaye na zubowa a idanunta, yadda take ji a zuciyarta ko ta daki Fadeelah ba hucewa za ta yi ba, babban abin takaici ma wai wannan ɗan iskan yaron mai ido a tsakar ka, yaron da ba ya ganin mutuncin mutane, ita kam ina zata saka rayuwarta? Haka dai ta yi ta saƙe-saƙe a cikin zuciyarta, ganin ta rasa mafita ya sa ko kallon inda Fadeelah take kuka ba ta yi ba ta fice gaba ɗaya a ɗakin.

Waya ta É—auka ta kira mijinta kasancewar ba mazauni ba ne ta faÉ—a masa abin da ya faru, cikin kuka take faÉ—in:

"Yaya Fadeelah ta cuce mu, ta kasa riƙe mutuncinta, ciki fa ta yi, ina zamu kai wannan abin kunyan? Ni wallahi na rasa yadda zan yi ma".

Daga ɓangaren shi shiru ya yi sai da ta gama bayani sannan ya ce:

"Ki yi haƙuri ki daina kuka, ƙaddara ce amma kuma duk da ganganci, ki kwantar da hankalin ki insha'Allah gobe ko jibi zan taso sai mu san yadda za a yi, amma kafin nan dan Allah kar ki ce ma ta komai", sai da ya tabbatar da hankalin ta ya kwanta sannan ya ma ta sallama ya ajiye wayar cike da mamakin abin da ƙanwar matar ta shi ta aikata, yana ma ta kallon mai wayo ashe shashasha ce...

Kwanan Fadeelah uku a asibiti a ka sallame ta a É—an wannan lokacin jikin na ta ya yi kyau sai dai damuwa da ya ramar da ita, tsakanin ta da Anty kuwa sai dai kallo don ko ta ma ta magana ba amsawa ta ke ba, a haka dai suka tattara suka koma gida, kuma har a lokacin mijin Anty bai dawo ba, rayuwa ta ma Fadeelah tsauri, ko kaÉ—an Anty ba ta raga ma ta...

Ango Adnan kam sai zuba soyayya a ke yi da Amarya Zeenat, ba ta bari ya fita ko nan da can, gaba ɗaya gajiyar da shi take amma ya kasa ce ma ta komai, tsabar tsanar ta ce a kwance a ƙasan ranshi amma bakinsa na mai nauyin furta ma ta, ga shi bai isa ya sa ta abu ta yi ba sai dai ta balbale shi da masifa ta na faɗin ita fa ba 'yar aiki ba ce, ko girki ba ta yi sai dai kullum ya siyo musu, ga ƙazanta kamar me, cikin wata ɗaya da aure Adnan ya rame, sai idanu, kana ganin shi ka ga mai damuwa amma ba zai iya furta wa ba, wani sabon abu ma da Zeenat ta tsira shine fita da ta ke yi kullum ba tare da izinin shi ba, ga shi bai isa ya ma ta magana ba sai ta hau shi da masifa wai yana takura ma ta, tsakanin shi da ita yanzu sai idanu...

Noor na isa asibiti ya kira Abba ya sheda mai abin da ya faru sannan ya ƙarasa ya kira nurses, ba ɓata lokaci aka karɓe su kasancewar asibitin mahaifinsa ne, cikin ƙanƙanin lokaci aka ba su taimakon gaggawa, Besty kam ya jigata sosai kasancewar ya bugu da gefen kujera ga kuma karaya a hannun shi na dama, naɗe wajen aka yi da bandeji bayan an gyara karayar hannun da ƙyar, sannan aka mai allura ya koma baccin wahala, ita kuwa Raudah allura kaɗai aka ma ta kasancewar suma kaɗai ta yi, Noor ya na ƙofar ɗakin da Raudah ta ke a tsaye, haushin ta yake ji sosai, gani yake kamar wani abu ya shiga tsakanin ta da Dee, sam ya ji ba ya ƙaunar ganin ta, ana cikin haka Abba da Mommy suka ƙaraso asibitin a tare, don Noor na gama faɗa wa Abba a lokacin ya na kasuwa shi ma ya kira Mommy hankali tashe, a bakin titi Mommy ta jira shi ya zo ya ɗauke ta suka wuce cike da fargaba, ran Abba ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, wato Raudah ba ta jin maganar shi kenan, duk faɗan da ya ma ta a banza ta yi auren ma ba ta rabu da wannan tantirin yaron ba, haka su ka tsaya cirko cirko a asibitin ba wanda yake iya magana, sai bayan isha'i sannan Raudah ta farka, ƙin shiga ɗakin Noor ya yi sai mommy ce ta shiga a lokacin Abba bai dawo daga masallaci ba.

Ko da Mommy ta shiga ta tarar da Raudah a kwance idanunta biyu amma hawaye na tsiyaya a fuskarta, ko a mafarki ba ta taɓa zaton Noor zai iya dukan ta ba, lallai ta san ta kai shi maƙura, tsinkar muryar Mommy ta yi ta na cewa:

"Ai ba ki ma yi kuka ba, bari Abbanku ya shigo za ki faÉ—a mana uban me wannan yaron ya je yi gidanki na aure",
Ƙara sautin kukan Raudah ta yi don ta tabbatar yau kashinta ya bushe, babu abin da zai hana Abba dukan ta, ita babbar damuwar ta ma Noor ganin ba ta gan shi a ɗakin ba, tunowa ta yi da abin da ya faru sai ta ji duk duniya ba wanda ta tsana kamar Dee don ko sunan shi sai ta ji ya ma ta ɗaci, yau a kan shi mijinta da take matuƙar so kuma yake son ta, mai haƙuri da kawaici ya sa hannu ya dake ta? Ko da ya ke ba ta laifinsa ba ne, don ko ita ce abin da za ta yi kenan ko zuciyarta za ta ji sanyi, babbar damuwarta ma shi ne kallon da Noor zai ma ta, ba ta da wata mafita, kuma duk abin da za ta faɗa ba lallai su yarda da ita ba, ita yanzu babbar matsalar ta ma bai wuce Noor ba ta ga har yanzu bai shigo ba, numfashi mai ƙarfi ta ƙara ja tana mai kallon Mommy, ganin Mommy ta ƙi kallon ta ne ya sa ta rufe ido tamkar mai bacci.
Chapter 14 · 0% Book details