← Book details Rashin Sani Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 9 OF 19

Chapter 51-55

Rashin Sani Complete Hausa Novel · about 4 min read

Mussa'af shiru yayi yana lalibo mafita domin yasan Wallahi haɗuwar su da Giwa ba dadi

Wata uwar dariya Ihsan ta fara harda ruƙe cikin

A fusace ya biyo ta aikuwa ta zuba aguje ta bar shashin su baki ɗaya mom aysha mom aysha kinga yaya mussa'af ko

Wata mata nagani akalla zata kai shekara talatin taci ado da wani haɗaddan leshi pink colour anme adon flower blue saai ƙamshi take zubawa da sauri ta rumgume ihsan tace

"Haba mussa'af me yasa kullum kana girma kana ƙara shiga dawa mu da muke shirinyin yar gida ,

Saƙar baki yayi yana kallon ta

Cikin tora haushi tace

"Kaga yarinya kyakkyawa san kowa ƙin wanda ya rasa shine ka ta kurawa rayuwar ta to Ni de bazan bayar ba sai nasa mutum kuka babyn zo mu zauna ta kamo hannunta ta zaunar da ita a sofa ,

Shi kuwa mussa'af rasa bakin magana yayi ya ja ƙwafa yace

Mom aysha wa zai aure lukutar yar ki kiyi addu'a Allah yasa ta samo lukuti irinta amma ina ni ina jimgegiya amma bara in dawo daga kotun Shari'a ta Giwa zan zo mu zauna a samo muku mafita

Wani uban ihu ta saki tana buga ƙafafu tace

Mom aysha bakin ce adena ce min lukuta ba

Babyn kƴale shi we burin kunya yake yi

Hannu ya yarfa yace owo ku ta shafa Ni na tafi

Uncle sulaiman ne ya fito yace


"Habibty kamar Muryar mussa'af nake ji daman be koma makaranta ba ?"

Eh shine ya biyo min babyn Wallahi lamarin su har dariya yake bani yawa masu ganin hanjin juna shi girman kai ita tsoka na

Allah ya kyauta

"Ameen"

Uncle sulaiman ina huni

Lafiya qalau ihsan

Uncle ina my boy

Yana barci

A guje ta tashi zata ta doshi

Da sauri mom aysha ta sha gaban ta tace

Babyn bacci yaron ki yake ki bari inya tashi zan kawo miki shi

Zun ɓuro baki tayi tace

Zan faɗawa ya Giwa ya samo min jariri a asibitin shi tunda kullum hanani naki kike

Duban uncle tayi tana dariya tace

Ihsan kenan mala'ikan yara honey kaji abin da take cewa

Hmm so take a kama su ita da Giwa a Ina zai samo miki wani baby tab lalle da sauranki

Wannan kenan

Mussa'af mussa'af mussa'af Wallahi ka fita a idona wato har zaka iya daukan mota kuyi yar tsaire a makaranta har kuna koƙarin buge dalibai

Dan girman Allah yaya kai haƙuri daga yau na dena

Karma Ka dena Wallahi dedai nake dakai a gidan nan ta shi ka tafi sannan daga yau driver ne zai dinga kai ka yana dauko ka baza ka sake daukar mota ba

"To, na gode sosai Allah ya saka da alkhairi ,

Banza yayi mai ya dauki lapton ɗinsa ya fara duba saƙon da aka turomai

Washe gari

A sanyaye take komai shirya wa tayi tsab cikin Fararan kaya tas yau kuma hijabin tane pink colour haka ƙafar wando anmai ratsin pink wata hadaddiyar kimono baka tasa an mata adon duwatsu na golding glass dinta tasa ta dauki wayar ta tace

Lailai mu tafi 8:30 zai shigo tara yace inje

"Okay fanna kinyi kyau yau ina barimar ki ne ta faɗa tana danne dariyar da ta taso mata ?"

A fusace tace

" ban sani ba sai kin shaƙeni zan faɗa miki "

Ooo tawo matafiya

Harara ta hurga mata yawa idanunta zaso waɗu ƙasa ta fiya suke jikin nutsuwa

Wow tafida kalli wata hadaddiyar yarinya ita fa nake baka labari kaf makarantar nan ba wanda take kulawa sai wannan kanwar Giwa gaskiya ta haɗu

Boss aini kaga na kasa magana ji na shiga computer lab naji su munnir suna zancan ta anya wannan ba Balarabe ya ce ba kalli shigar ta fa

Tafida kenan ai daga gani ba tambaya sai de sufa basa auran bare

"Kai boss Wallahi ta tafi da imanina,

Ko ina ta huce kowa bin ta yake da kallo

Lecture suka shiga a layin farko ta zauna kafin malamin ya zo ta fara charting a wayar ta ji tayi an dena surutu da sauri ta ɗago wa zata gani zaro ido tayi ganin ya harɗe hannuwansa agirji ya zuba mata ido tuni ta shiga rudani lefi kan lefi cikin rawar murya tace

Sorry sir.....✍🏼


RASHIN SANI


By

Oum yasmeen
Chapter 9 · 0% Book details