← Book details Rashin Sani Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 11 OF 19

Chapter 61-66

Rashin Sani Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Wallahi zainab ki kiyaye ni kinsa nayi miki abin da ba halina bane kamar wani kububuwa ya huce fuuu ya bar ta dafe da kuncin ta ,,

Kamar wata zararriya ta ɗurƙusa a gaban pic ɗin da ya waɗo tace

"Kin zame min matsala nida iyalina wasu zafafan hawaye ne zuka zubo mata da yar dar Allah kin mutu ba zai saƙe ganin ki ba a rayuwa

Wannan kenan

Tamƙar ba abin da ya faru haka suka dinner tare da ƴa' ƴan sa cikin farin ciki da ƙaunar juna knocking bells yaji anyi da sauri ya tashi daman sunyi da abokin sa ɗan ƙasar Algeriya Mrs haris mahir zaizo cikin fara'a ya tarbe shi gaisawa sukai

Cire takalmin sa yayi ya shigo sosai yaran sukai farin cikin gani daddy Fahad barin miemie da Fahad yake abokin ta a school aguje ta rumgume shi cikin harshen Turkiyya tace

"Daddy Fahad ina Fahad yake ?"

Ja mata kumatu yayi yace

"yana gida amma nayi miki alkawari zuwa na gaba da zanyi da shi zan zo "

murna tayi ta sauka ƙasa cikin tarbiyya su isham suka gaishe da daddy Fahad suka bar gun

Favor favor cikin sauri yar aikin nasu ta zo baturiyar Birtaniya ce cikin ladabi ta gaida shi

kitchen ta nufa ta buɗe cabinet ta dauko plate sannan ta buɗe Fridge ta nufa ta dauko cake da lemo ta zuba acikin plate da ta ɗauko cikin ladabi ta ajjiye me matsawa tayi ta basu guri

Mrs haris yakake

Lafiya ƙalau Dr Mahmud

sai da ya bari ya danci cake da lemo sannan ya dube shi yace

"ɗazu na ganta ,,

Cikin sauri ya goge bakin sa yace

"Da gaske "

To inma ba ita bace me kamarta nagani sai yanzu da nake tunani ita wacce na gani yarinya ce amma Wallahi kamar su ɗaya da ita

Hmmmm anya kuwa abokina lamarin nan ba ya fara taɓa kaba dan Allah yau kabani labarin ta

Shiru yayi yau tsawon shekaru goma sha bakwai suna tare ya kama ya faɗa mai labarin sa cikin tsananin damuwa yace

in na baka labarin ta babu komai a ciki sai san zuciya da dana sani da ƙabilan ci bara amfani mahaifina ya nuna ƙarmin ikon da yake da shi a lokacin ya rabani da ita sai yanzu yake dana sani mara amfani

Please yau dan Allah da Manzonsa ka bani labarin ta

Kwallace ta taro a idonsa yace

"A shekara ta 1991 a nan na haɗu da ƙaddara ta

2:30 pm na rana a gajiye na taso daga federal college of education Kai tsaye gida na nufa gudu nake sosai har an isa unguwar jan bulo da a nan muke kafin mu tashi mu koma darmanawa parking mota ta nayi a waje na tora gate ɗin gidan mu wata mata nagani da yara alkalla yaran za sukai su bakwai da wata mata Hajiya salamatu da ke kawo wa Hajiyan daura wato mahaifiyar yar aikin ta tayi aure shine ta ce akwo mata wata

Aa Mahmud kai ne ba magana zaka wo ce ni

Juyowa yayi ganin ta gansa yace

Hajiya salamatu ina yini

Lafiya qalau ya karatu

Alhmdllh

Kaga na zo Hajiyan daura bata nan

Au daman bata dawo ba

Ehwllh

Ƙarar mota mukaji da sauri dukkan mu muka juyo ganin Hajiya ce ta dawo

Fito wa tayi cikin fara'a tace

aa Hajiya salamatu sannun ki

Yauwa Hajiya andawo lafiya

Lafiya qalau tawo mushi ga daga cikin

Hajiya ni zan shiga ɓangaran yaya domin Wallahi na ƙwaso yinwa

Uhmm a cici sai ka dawo

Kai tsaye ya huce ɓangaran anty Maryam wato mahaifiyar giwa

Wani haɗaddan floor suka shiga zama tayi a ƙasa yayin da yaran suka ra ƙuɓe a jikin bango

Hajiyan daura ta tashi ta shiga kitchen ta dauko plate ta ɓuɗe fridge ta dauko ruwa me sanyi da yake lokacin zafi ne da kofi sai ɗan kayan motsa baki ajjiye musu tayi ta ce bisimillah

La hajiya har da ɗaweniya Wallahi da kin bar shi saboda na biya wani gida nan bayan ku

Hijabin cikin ta ta cire tace

Ko yaya ne ko taɓa

"To, hajiya mun gode Allah ya ƙara girma ku ba ku iya gaisuwa ba ne ?"

Cikin rawar murya suka h
Gaishe da Hajiyan daura ban da wata me kama da sadakar yallah ta sadda kanta ƙasa tana wasa da ɗan ya tsunta

Wata uwar tsawa haniya salamatu tace

Keee kaltum uwar ruƙon nake bata koya miki gaisuwa ba

Cikin rawar jiki hausar ta bata fita tace

"Kayi haƙuri ta koyamin ,,

Haba hajiya salamatu be kamata kiyi mata haka ba

da sauri ta juyo tace

Wallahi Bature yaran ne sai da haka

Zuba musu ido hajiyan daura tayi ajiyar zuciya ta sauke tace

Hajiya na zaɓi wacce ta nuna wacce aka kira da kaltum

To to hajiya ba matsala

Amma kin faɗa mata aikin ta sannan bana son ƙazan ta

Wallahi hajiya duk na faɗa musu sai da sukai sati ɗaya a gidana na ƙoya musu abubuwa tuƙunna na kawo miki su ki zaɓa

"Nawa"

Wallahi hajiya bazan faɗaba duk yarda ki kabani dedene

"Okay Mahmud jika ɗaki ka buɗe cabinet ɗin jikin gadona ka buɗe zaka ga kudi ka dauko min,,

To hajiya

Wayar ta ta shiga ɗannawa ɗago wa tayi tace

Na tora miki kuɗin ki ta account ga kuma wanda zaki bawa iyayen ta

To to ina godiya Allah ya ƙara girma da daukaka

Ameen tace

Hajiya ga shi

Miƙa mata

Hannu biyu tasa ta amsa ta tattara sauran zata tafi da sauri kaltum ta tashi hawaye sun cika mata ido a nan ne nasami damar ƙare mata kallo

Wata irin lufaya ce a jikin ta duk ta koɗe wani gun ma ya fashe

Cikin faɗa hajiya salamatu tace

"We ke kaltum yau she zaki hankali ne Wallahi zan faɗawa matar ubanki,,

Jikin ta narawa ta koma ta zauna tace

bazan ƙara ba

muje in nona miki ɗakin ki

To bayan zuwan kaltum gidan mu ita take komai tun idanuwana basa kai kanta har na kamu da wata iriyar soyayyar ta ba ruwan ta magana bata dame ta ba rainon Giwa ya koma hannun ta duk da ƙarancin shekarun ta sosai sukai wata shaƙuwa in jadda ya dawo daga kotu to tana zaune a ɗakin ta har sai gobe da safe waka Hajiya ta faɗa mata

Abu ɗaya ke cikine zuciya shine

Family ɗin giwa basa auran bare musamman ƙabilal barebari saboda kowa yasani buzaye da barebari basa haɗuwa gu ɗaya har yau jadda besan a wacce ƙabila take ba domin inda ya sani to datuni tabar gidan sa ni kuma ba maganar dake haɗa mu da ita inba gaisuwa ba a sannu a hankali na fara janta da soyayya ta duk da na ƙasa hana kai na dena son ta duba da irin halin da zan shiga in Hajiya ta gane

Bayan wata biyar da zuwanta ni kuma na gama karatuna

Ina zaune a floor duk yan uwana sun zo taya ni murna mu tarane a gun mahaifan mu yaya Dawud sai yaya Abdullahi sai anty zulaihat sai anty Amina sai yaya sulaiman sai yaya Yasir sai anty Sa'adatu sai yaya mansur sai ni duk suna da aure ni da yaya mansur ne bamu da shi ko wanne a cikin su auran haɗi akai musu har matan a taron ne jadda ya faɗamin abin da ya kusan sandarar dani a zaune ta ƙarda ya meƙomin da sauri na ƙarɓa ina dubawa admission ne na tafiya America university of United Kingdom duk da son karatun da nake amma Wallahi ina tunanin in tafi inbar kaltum haka na ƙakalo farin cikin dole nayi mai godiya na ta shi na shiga ɗaki na alamar shigowa naji da sauri na ta shi zaune ganin Hajiya

zama tayi cikin damuwa yace

"Bature ina me baka umarni na shawara ba duk abin da kake yi a gidan nan ina kallon ka wanne irin halin kake so ka jefani a gidan nan kasan halin mahaifin ku ka fita a sabgar kaltum ko Wallahi in me da ita gida ,,

Dan Allah Hajiya karki rabani da kaltum

A fusace ta ɗaga hannu ta zabga mai mari tace .....✍🏼


RASHIN SANI


By

Oum yasmeen
Chapter 11 · 0% Book details