← Book details Rashin Sani Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 10 OF 19

Chapter 56-60

Rashin Sani Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ƙara haɗe fuska yayi yace

Bani wayar ki kuma ki fitar min daga aji doka na sa duk wanda ana lecture ya dan na waya ko yayi surutu fita zai yi amma ke na shigo Bama kisan na shigo ba

Rumtsai idanuwanta tayi ganin kowa yana ganin ta ba ta ƙara cewa komai ba ta tashi jiki a sanyaye ta fita

Gu tasama ta zuba ta gumi wani baƙin ciki ya To kare mata zuciya ta nayi tana duba agogo har lokacin fitar sa yayi bayan ya fito sauran yan aji suka fito fanna

Da sauri ta ɗago ta kalli Laila cikin sanyin murya ta ce

"Na'am Laila ya fito ko ?"

Hmmmm ajiyar zuciya ta sauke tace

"Eh ya fito tashi muje ko "

Okay mu tafi

Fanna kinga mukiyaye duk abin da zai hadamu da Dr Giwa mu yi taka tsantsan

Kai kawe ta ɗaga mata domin bata da bakin magana har suka isa chamber mansion ɗin sa tun daga bakin filin da aka ƙawata da bishiyu aka zube security Laila tace

Sannu da aiki sir

Tsohon yace

"Yauwa ina zaki ?"

gun Dr Giwa shi yace muzo

Okay bara inyawa sakatariyar sa magana

kujerun da aka tana dar a gun suka sami daya daga cikin gabion chairs suka zauna sosai suka shiga damuwa in yace bashi da lokacin ganin su sun shiga ukku

Juyowa yayi ya kalle su yace

Yace ku shiga

Mun gode sai da suka huce e-potal San nan suka iso na shi bugawa sukai

Ta na daga zaune ta basu izinin shigowa

Lailai tace

Sannu da aiki Dr yana ciki

Wani banzan kallo lubna tayi wa fanna zuciyar ta yi wani irin baƙi ko tantama ba tayi wannan ita sir Yusuf birnin kudu yake cewa sun da ce da oga

Wayar ta ta dauka ta fara dan nawa tana taunar chingum jika ke ƙas ƙas tush ta fasa ƙwai

Kallal kallo a ka shiga tsakanin lailah da fanna tuni zuciyar fanna ta sosu domin ta tsani hulaƙanci cikin sanyin nan nata tace

"Baiwar Allah muna magana fa,

Tuni zuciyar lubna ta zu iya huya ta tashi tsaye tace

Kinga Malama da kata mini tunda kuka ga nace ku shigo ai kunsan yana nan

Hararta fanna tayi ta buɗe kofar sa bakin ta dauke da sallama

Be ɗago ba in ma ya amsa to a zuciya ya amsa ci gaba yayi da ɗanna loptop da alama aiki yake samin gu sukai suka zauna cikin rawar murya fanna tace

Itama lailai ta gaishe shi

"Good morning sir"

kan sa a ƙasa yace

''Me ya kawo ki nan ?"

Wane irin baƙin ciki ne ya to kare zuciyar fanna ga wani rainin hankali

Kace inzo kuma ka dinga maganar me ya kawo ni nan ai ba tasan tayi ka tiɓarar zance ba a she a fili ta faɗa da sauri ya ɗago ya cire glass ɗin sa ya zu ba mata ido yayi da lailah gumi ya fara wanke ta domin yau tsiwar fanna ta jaja musu

File ya ɗauko ya ce

"Ke ce Fatima bukar gana ?"

Kai ta ɗaga domin a yaran barebari fanna ta na nufin Fatima

Cikin husky voice ɗin sa yace

"baki da bakin magana ne ?"

ɗan ƙaramin bakin ta ta motsa yawa na jarire yayi pink colour har sheƙi yake tace

"Eh nice "

Kamar zai lumshe idanuwan sa sai kuma ya buɗe su yace

"David yayi test ɗin Chemistry inda ya haɗa ku da yan level two yayi muku ta zaɓen fitda gwanin shekara da muke yi in sababbin ɗalibai sun zo domin mu kara musu ƙarfin gwuiwar karatu,,

eh sir yayi

"Zan sake miki test ɗin domin inga da gasken ki ki kayi ko kuwa sata ki kayi domin doka ce a makarantar nan duk wanda yayi satar amsa ko rarshi za muyi

Wani ta ƙaici ne ya kama ta wato gani yake satar amsa tayi to Allah ne ya bata iƙon kayar da yan level two

"Kin shirya "

Eh na shirya

Ya dubi lailai tace

Ke koma waccan kujerar

Tashi tayi tace

"To sir ,

H.O.D na ko wanne dipertment suka shigo suka zauna harda sir Yusuf birnin kudu

Question paper ya miƙo mata yace

Bisimillah

Amsa tayi ta fara duba wa addu'a take yi cikin ran ta Allah ya te maketa tasa kimono a saman kayan ta da bata san ya zata yi ba mi ƙo mai tayi ta gama

Ƙar ɓar ta ƙardar yayi ya fara duba wa sosai yarinyar ta bashi mamaki a hankali yace

Good girl

matsowa kusa da shi birnin kudu yayi ya ce

"Oga yade ko ka ƙƴa sane ya kanne mai ido ɗaya ?"

Cije lips ɗi sa na ƙasa yayi ya Jefawa birnin kudu wani irin kallo

yace

"Zaku iya ta fiya ,,

Cikin sanyin murya fanna tace

"Sir wayata ,,

Zuciyar sa yaji tayi sanyi ya yafe mata abin da tayi kuma ta sami wani matsayi a zuciyarsa wanda shima be san wanne matsayi bane miƙo mata yayi yace

"Ƙar ki ƙara "

Kai ta ɗaga mai suka fito cikin sauri lubna ta sha gaban su tace

"Wallahi yarinya kikiyaye dan ruwa ba sa'an kwando bane ki fita daga sabgar Dr "

Wani kallon sha sha fanna tayi mata ta huce

Cizon ɗan yatsa tayi ta koma ta dubi kawar ta tace

kinga abin da nake faɗa miki ko da kin barnin na naɗa mata duka yar da ba zata sake kallon office ɗin nan ba

Lubna kina haukane to ita rayuwar duniya siyasa ce ki jawo ta ajiki kiji ko soyayya suke sai kisan ta wanne ɓangare zaki rusa ta faɗa ba naki bane

Hmmmm nabihat ba zaki gane bane Wallahi kullum san Giwa ƙaruwa yake a zuciya ta

Wannan kenan

*Turkiyya Istanbul*

9:30 na dare

Wani dattijo ne ya fito daga wani haɗaddan super market hannun sa ruƙe da jaƙun kuna yana sanye da t shirt fara da wando baƙi yana amsa waya da sauri ya zubar da kayan dake hannu sa ganin wata matashiya akalla zata kai shekara ashirin da biyar tana sanye da bakar abaya hannunta ruƙe da jakar kayan da ta siyo alamun daga super market ɗin ta fito ta buɗe motar ta tashi ga

"da sauri shima ya buɗe motar sa ya shi ga ya fara bin bayan ta ganin ana binta yasa ta ƙara gudun motar ta ,

da sauri yake shara ra gudu idanuwan sa na zubda siraran hawaye tambas in idanuwan sa ba gizo sukai mai ba tambas ita yaga ni wani sha shi na zuciyar sa ya bashi tabbacin ita ce amma me ya kawo ta ƙasar bayan barin ta shekara goma sha takwas

Nima tuni na gyara biro na da taƙar da ta abin mamaki ne dattijo kamar sa yana kuka domin a ƙalla zai yi shekaru arba'in da biyar glass ɗin idanunsa ya cire yayi da ya kifa kansa alan sitiyarin motar sa domin motar da yake bi ta ɓacewa ganin sa kuka yake kamar ransa zai fita ya rasa damar sa

Wayar sace taki ruri alamar shigowar kira ɗago jajayan idanuwan sa yayi ya kalli wayar isham ne tushu ya dauko ya goge fusƙar sa ya daidai ta nutsuwar sa ya ɗaga kiran

Daga can matashi yace

"dinner is ready Abbu muna ta jiran ka ,,

A jiyar zuciya yayi yace

Isham ina kan hanya gani nan zuwa

Okay ya kashe wayar ta fiya yayi me nisa sannan ya isa wani haɗaddan mansion ba wani babba ne amma iya kyau da tsaruwa ya tsaru ya tsaru horn yayi getman ya buɗe mai a jikin get ɗin gida an yi rubutu da golding colour an rubuta Dr Mahmud sa'eed Giwa shiga cikin gidan yayi ya yi parking ya fito da sauri yaran suka rumgume mahaifinsu su muhibbat tace

" welcome back Abbu,

kiss yayi mata a kumatu

Yace

"ina Ummin ku take "

Da sauri miemie tace

Abbu tana ɗaki ta ce mana bata da lafiya

Dau kan ta yayi yace

Kuzo mu shiga ciki binsa sukai kallo ɗaya zakai wa yaran kasan hutu da jin dadi ya zauna musu miemie tana sanye da baby gownt sky blue an mata ado da white flower ƙafar ta sanyi da wani slippers me kyau an raba mata gashin ta gida biyu

Yayin da budurwa da ba zata huce shekara tara ba tana sanye da riga da wando

Wani haɗaddan floor suka shiga wanda ya gaji da haɗuwa ajjiye miemie yayi yace

My mommy na bara in dubu ummin ku

"Okay Abbu I m waiting for you ,

Kai ya jinjina mata bedroom din ummin ya nufa bakin sa dauke da sallama ya shiga tana kwance akan wani luxury bed ta lulluɓa a wani haɗaddan blanket milk colour a hankali wani sassanyan ƙamshi ke ta shi bakin gadon ya zauna cikin kulawa ya dube ta yace

"Ya jikin na ki ?"

Zuba mai ido tayi tuni wasu hawaye suka zubo mata

Sa hannu yayi ya goge mata hawaye yace

"Me ya same ki ?"

Me maƙon ta bashi amsar sa sai tace

"Hmmmm yaya dan girma Allah ka dena neman ta ni baka ga yarda ka koma ba duk kabi ka rame kullum da irin zancan da za'a fada maka ni da ya'yan mu mun isheka rayuwar duniya "

What Please zainab ki bar ɓatawa kanki lokaci neman ta yanzu na fara me isa kika damu kai ki akan abun da bazai yiwu ba ƙar ki ɓata mana zaman lafiyar da muke ciki nida ƴa'ƴa na

Wasu zafafan hawaye ne suka zubo a kuncin ta tace

"ko dan kaga auran haɗi akai mana shi yasa ka fifita bare akai na ,

Da sauri ya tashi ransa a ɓaci yace

ta soni alokacin da bani da komai ta zaɓi zama dani ta guje ahalinta ta fuskanci ta kura gallazawa a cikin yan uwanta da yaranta ta sadaukar min da farin cikin ta dan haka ƙar ki ƙara kwatan ce da ita

ya fita a ɗakin da sauri ta bishi har ɗakin sa wani haɗaddan hoto ne ya kusan cinye rabi bango da sauri ta sa hannu ta fusgo shi tuni ya bashe ya waɗo ƙasa tana haƙi tace

Dan kaga na ƙƴale ka har a cikin gidana ka samin hotan banza ƙabila

bata ƙarasa ba taji saukar mari tuni idon sa yayi ja abin ka da farar fata fusƙar shi tayi ja yace.........✍🏼


*RASHIN SANI*


By

Oum yasmeen
Chapter 10 · 0% Book details