Sashe 23
Hibbatullah Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read
Dan malam yayi murna sosai da wannan kyautar da Malaminsa yayi masa don dama can ya jima yana fama sa soyayyar Fulani acikin xuciyarsa kawai yadai gagara gaya mata ne ganin ita dai Alu takeso.Bayan auransu Alu ya shiga gwada mata qauna da kuma bata kulawa daidai gwargwado amma ita kuwa rashin mutuncin yau daban haka kuma na gobe daban,sau daya suka tab'a hada shimfid'a shima din cewa tayi kaddarace.Fulani zata haqura amma ina ta kasa cire Alu aranta,ita dashi suka hada plan akan cewa yazo gidanta ya zauna adakin auranta,watakila dan malam na ganinshi zaice kwartonci yazo yi sannan kuma ya sauwake mata,bayan ya sawwake mata sai su gudu.
Sosai Alu yayi na'am da wannan shawarar data kawo masa ranar da suka hade awani wuri asirrance.Ai kuwa ranar da Dan Malam ya fita,sai ga Alu yazo,kuma harga Allah babu abinda ya shiga tsakaninsu,sai akayi rashin sa'a da Dan Malam ya tashi dawowa sai suka taho had'e da sirikinsa wato Mal.Aminu.
Mal.Aminu har kuka yayi da ganin wannan abin kunyar da 'yarsa ta jawo masa agidan auranta,shi kuwa Dan Malam jikinsa ne yayi sanyi qalau harma ya kasa furta komai,kafin sukai ga daukar wani mataki Alu ya tsere,kuma garin ya bari gabaki daya.Malam ya zane Fulani sosai kuma yace dolene Dan Malam ya sawwake mata,dan malam kuma yace shi bazai iya ba ayi haquri yana son matarsa ahakan.Babu yadda suka iya illa barinsa da matar tasa,ita kuwa Fulani taci kuka sosai sanda taji labarin wai an nemi Alu an rasa, bayan watanni biyar saiga ciki ya bullo ajikinta,mahaifinta yace wannan cikin bana Dan malam bane,shima Dan malam ya soma zarginta don tunda sukayi aure sau daya ya kusanceta,sai yayi tunanin kila cikin na Alun ne.
Malam ya matsa masa akan dole saiya saketa kuma saita bar kauyen don bazai bari ta janyo masa abin fada ba agarin.Babu yadda dan malam ya iya illa sawwake matan sabida mutane suna ganin cikin za'ace ai cikin Alu ne.
Babu irin rokan da fulani batayi ba akan mahaifinta yayi haquri karya koreta amma fir! yaki.Yayunta da mamanta ma sukace babu ruwansu da ita ta tafi can ta karata da shegen danta.Bata da kalmar da zata kare kanta dashi don an riga an kama Alu adakinta,don haka komai zata fada akan babu abinda ya shiga tsakaninsu ba yadda zasuyi ba,amma harga Allah cikin jikinta na Dan malam ne.
Haka ta baro kauyen tana kuka,Mal.Muhammadu sarkin taimako alokacin yazo siyen sa ne akauyen,sai yaga yadda take kuka tana tafiya,kiranta yayi ya tambayeta abinda ke damunta ta gaya masa,yace ta masa jagora xuwa gidansu,bayan sunce yayi roko amma fir! Mal.Aminu yace bazai karbeta ba.
Haka dai suka baro gidan rai ba dadi,mal.Muhammadu yace"Toh yarinya idan zaki iya bina garinmu har xuwa lokacin da Allah zai saukeki lafiya asannan kuma mahaifinki ya huce sai mu dawo toh bismillah muje...."
"Ni kowani gari ne muje idan har kana da mata wacce zan zauna agunta...." Fulani ta fada tana mai kuka.
Murmushi yayi yace"Matana biyu saidai babu wacce ta taba haihuwa...." Fulani duk ta rasa abinyi shiyasa kawai ta yanke shawara ta bishi minna.
Acan kuwa rigimace babba ta kaure tsakaninsa da matansa musamman da suka ga Fulani dauke da ciki,sai suke ganin kamar karuwarsa ce,kila cikin da tayi ne yasa aka koreta daga gida shi kuma ya rasa abinyi shiyasa ya kawota nan. Kan kuce meye wannan har magana ya bazu agari cewa ai mai unguwa ya kawo karuwarsa ga iyalinsa.
Shi kuwa ya nuna ikonsa akansu,ya nuna musu cewa ya isa da gidansa,ya baiwa Fulani dakin da zata zauna ta reni cikinta harta haihu.Ya sayo mata wasu en kayaччαkí na amfaninta ya xuba adakin.
_*чαnzu wαccє írín zαmα nє fulαní tαчí αgídαn?*_
_*чα αkαчí mαl.muhαmmαdu чα cαnzα mαtα dαgα вαчα?*_
_*ѕαnnαn kumα чα αkαчí tα kαmu dα cutαr чσчσn fítѕαrí (fíѕtulα)?*_
_*ínα kumα lαвαrín tαfíчαr mαí mαrtαвα umαr fαruwα?*_
*ku вíчσ hαfnαn*
Sosai Alu yayi na'am da wannan shawarar data kawo masa ranar da suka hade awani wuri asirrance.Ai kuwa ranar da Dan Malam ya fita,sai ga Alu yazo,kuma harga Allah babu abinda ya shiga tsakaninsu,sai akayi rashin sa'a da Dan Malam ya tashi dawowa sai suka taho had'e da sirikinsa wato Mal.Aminu.
Mal.Aminu har kuka yayi da ganin wannan abin kunyar da 'yarsa ta jawo masa agidan auranta,shi kuwa Dan Malam jikinsa ne yayi sanyi qalau harma ya kasa furta komai,kafin sukai ga daukar wani mataki Alu ya tsere,kuma garin ya bari gabaki daya.Malam ya zane Fulani sosai kuma yace dolene Dan Malam ya sawwake mata,dan malam kuma yace shi bazai iya ba ayi haquri yana son matarsa ahakan.Babu yadda suka iya illa barinsa da matar tasa,ita kuwa Fulani taci kuka sosai sanda taji labarin wai an nemi Alu an rasa, bayan watanni biyar saiga ciki ya bullo ajikinta,mahaifinta yace wannan cikin bana Dan malam bane,shima Dan malam ya soma zarginta don tunda sukayi aure sau daya ya kusanceta,sai yayi tunanin kila cikin na Alun ne.
Malam ya matsa masa akan dole saiya saketa kuma saita bar kauyen don bazai bari ta janyo masa abin fada ba agarin.Babu yadda dan malam ya iya illa sawwake matan sabida mutane suna ganin cikin za'ace ai cikin Alu ne.
Babu irin rokan da fulani batayi ba akan mahaifinta yayi haquri karya koreta amma fir! yaki.Yayunta da mamanta ma sukace babu ruwansu da ita ta tafi can ta karata da shegen danta.Bata da kalmar da zata kare kanta dashi don an riga an kama Alu adakinta,don haka komai zata fada akan babu abinda ya shiga tsakaninsu ba yadda zasuyi ba,amma harga Allah cikin jikinta na Dan malam ne.
Haka ta baro kauyen tana kuka,Mal.Muhammadu sarkin taimako alokacin yazo siyen sa ne akauyen,sai yaga yadda take kuka tana tafiya,kiranta yayi ya tambayeta abinda ke damunta ta gaya masa,yace ta masa jagora xuwa gidansu,bayan sunce yayi roko amma fir! Mal.Aminu yace bazai karbeta ba.
Haka dai suka baro gidan rai ba dadi,mal.Muhammadu yace"Toh yarinya idan zaki iya bina garinmu har xuwa lokacin da Allah zai saukeki lafiya asannan kuma mahaifinki ya huce sai mu dawo toh bismillah muje...."
"Ni kowani gari ne muje idan har kana da mata wacce zan zauna agunta...." Fulani ta fada tana mai kuka.
Murmushi yayi yace"Matana biyu saidai babu wacce ta taba haihuwa...." Fulani duk ta rasa abinyi shiyasa kawai ta yanke shawara ta bishi minna.
Acan kuwa rigimace babba ta kaure tsakaninsa da matansa musamman da suka ga Fulani dauke da ciki,sai suke ganin kamar karuwarsa ce,kila cikin da tayi ne yasa aka koreta daga gida shi kuma ya rasa abinyi shiyasa ya kawota nan. Kan kuce meye wannan har magana ya bazu agari cewa ai mai unguwa ya kawo karuwarsa ga iyalinsa.
Shi kuwa ya nuna ikonsa akansu,ya nuna musu cewa ya isa da gidansa,ya baiwa Fulani dakin da zata zauna ta reni cikinta harta haihu.Ya sayo mata wasu en kayaччαkí na amfaninta ya xuba adakin.
_*чαnzu wαccє írín zαmα nє fulαní tαчí αgídαn?*_
_*чα αkαчí mαl.muhαmmαdu чα cαnzα mαtα dαgα вαчα?*_
_*ѕαnnαn kumα чα αkαчí tα kαmu dα cutαr чσчσn fítѕαrí (fíѕtulα)?*_
_*ínα kumα lαвαrín tαfíчαr mαí mαrtαвα umαr fαruwα?*_
*ku вíчσ hαfnαn*