Sashe 9
Mummunan Zato Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Cikin gatse ta ce,"To ba ga amarya ba." Sai bai fahimci gatse ta yi mishi ba, ya ce,"kin amince in tafi da ita?" Haushi ya kama A'isha, ta ce yardata ka ke nema? Ni kuma a wa?" Ya ce,ni fa duk abinda zai maido min da walwalarki shi nake son yi,a zuciyarta ta ce,ka ce dai kana son abinda zai baƙanta min rai,ya ce kin ji ni me zan miki ki huce? Ta ce,wai to ni ce maka aka yi ina fushi? Ya ce, amma ai da ba haka ki ke ba,ta ce to yanayin rayuwa ne yazo da haka, don haka mu duka sai mu ɗauki haƙuri da juna. Ya saki hannunta tare da cewa shikenan,ni zan wuce Beby sai na kira waya" Ta rakashi kamar yanda ta saba, suka yi sallama a gun mota.
A'isha ta koma ciki, zuciyarta da damuwa. Nata ganin Uncle ya samu wadda ta fita yanzun zaya daina damuwa da ita, shi ko ya tafi ne cike da kewarta tare da son ganin ta dawo tamkar da.
Ran da Jummai zata fita daga girki, Alhajin ya sanar da ita cewa,yana son tafiya da Hadiza tafiyar nan da zai yi. Nan Hajiya Jummai ta shafa ma idanunta toka, ta shiga masifar cewa, ita bata yarda ba, don ya ga komai ya ce tana shiru shine zai zalince ta,to ita fa bata amince da wannan zancan ba.
Shiru ya yi yana kallonta,ga mamakinta sai taga ya miƙe tare da cewa, tafiya da Hadiza babu fashi, saboda matanshi uku ba zai tafi shi kaɗai ba,ta ce to dole sai da Hadiza? Ya ce,to gaya min da wadda zan tafi, A'isha tana makaranta,ke kuma ina ne ba mu je da ke ba? In bazaki manta ba,lokacin da aka ɗaura mana aure dake ko sati ɗaya ba muyi garin nan ba muka bazama duniya, wata shidda muna yawon amarci. Cikin waɗannan wa ya samu haka? A'isha ko airport ta taɓa zuwa ne?"
Hajiya Jummai ta fito tana cewa,na barka da Allah. Da kallo ya bita, ita wannan watau rashin mutuncin da take yi wa wasu shi ne ya soma zuwa kaina,ya yi ƙwafa,ko a jikinshi ya ɗauki amaryarshi suka nufi Phoenix.
Harkokinshi suna tafiya yanda yake so gefe kuma ga amarya.
Hadiza irin matan nan ne masu fi'ilin tsiya da ƙwarƙwasa,gata da son komai ace ita ce gaba, sannan tana da son ƙyale-ƙyale. A da Hadiza baƙa ce, amma yanzun fara ce tas,sai dai in ka kalli ƙafar zaka gane farin na mai ne. Tana da ƙiba kuma bata da tsawo,ga tumbi. Gaskiya sun yi soyayya ko ince suna soyewa. Tana matuƙar son Alhaji Saddiƙ.
#######
[12/12, 13:22] Ummi Tandama😇: *📗📗Page 7*
Ta fi son ace daga ita sai shi bata son ganin kowace mace kusa da shi, shi yasa take jin haushin wannan shegiyar Beby É—in da bakin shi ke yawan kira, don ta kula yanda yake yawan cewa Beby ko Jummai ba ya kira haka,tana burin maye gurbin Beby É—in nan.
Tun saura ƙwana huɗu a yiwa su A'isha hutu, makarantar kamar yadda ta saba ta samo tura ma dukkan iyayan ɗaliban nasu text cewa rana kaza ne za'ayi hutu, lokacin da saƙon ya isa ga wayar Uncle ba layin ba ne cikin wayarshi, tunda baya ƙasar ma. Kan wayar da layin ke ciki ma bada ita ya tafi ba, don haka bai samu saƙon ba, ballantana ya ce aje a ɗauke ta, ƙa'idar makarantar ba sa ba da ɗalibai sai dai in iyayansu ne ko waɗanda suka ɗauki nauyinsu. Sam Uncle bai san taƙamaiman ranar hutun ba, don haka koda ranar hutun ta zo A'isha ba taga anzo ɗaukarta ba,a ƙarshe bayan kowa ya watse nan shugaban makarantar suka shiga neman shi a cikin waya. A'isha ta ce, musu ya yi tafiya baya ma ƙasar gaba ki ɗaya. Don haka sai suka ba da ta gidan wata Malama da ke nan cikin makarantar.
Wannan lamarin ya ƙara sa A'isha yarda da cewa yanzun Uncle ya daina yi da ita, ya daina sonta inda da ne ba yanda za'ayi ya share ta, yanzun ya samu wata wadda ta fita, sanadin wannan yasa A'isha zama miskila.
Gidan Malama Salamatu, gida ne mai tsari da tarbiyyar Islama, tana da yara Æ´an biyu sa'annin A'isha, suna son Aisha sai dai ta kasa sakewa da su,ba ta cika magana ba, sai dai sun kula tana da yawan ibada. Malama Salamatu ma ta yaba da A'isha.
Ranar da ta cika ƙwana biyu ne ya ga saƙon ta cikin Internet ɗin shi, lokacin yana zaune yana duba saƙonni. Hadiza kuma an dage ana ta danƙara uwar ƙwalliya, faɗin innalillahi wa'inna ilaihir'raji'un ɗin da ya yi shi ne ya saka ta juyowa ta dubeshi,nan ya ɗauko wayarshi ya shiga neman layin Hajiya Jummai. Hajiya Jummai ta ɗauka lokacin ma tana gidan Kari, ya ce Jummai an ɗauko beby daga makaranta ne? Ta taɓa baki sannan ta ce, wacece haka? Cikin sauri ya ce "A'isha fa" ta ce,sallahu ka bari cewa a ɗauko ta? Sannan ta kashe wayarta, ta tsani wannan A'isha ballantana in yana faɗin Beby ɗin nan, ta ce ɗan rainin wayo, Kari ta ce,hala mutumin naki ne?" Ta ce shi ne mana,kin ji shi ne? A firgice wai an ɗauko A'isha daga makaranta? Karima ta ce, na kula duk da ya yi auran nan hankalinshi ya fi tafiya ga wannan A'ishan.
Jummai ta ce, shi yasa na tsane ta, har na fi jin kishinta akan Hadiza, duk da nasan Hadiza da uwarta Lanti ba ƙyalle ba ne? Kari ta ce"ai dole ne kifi jin kishin A'isha, tunda wanda ake kishin domin sa ya fi sonta,(ta ci gaba da cewa) ko me ya gani jikinta? Yarinya ba ƙugu ba sharaɓa babu nonon kirki. Koda yake kin san ƴan ƙauyan nan fa suna da mugayan malamai, sai a mallake miki miji a kan Naira ɗari ko ɗari biyu."
Tsaki Jummai ta ja,ai ba'a ƙwana a gado kullum, kuma nima na san ba don sun min asirin da duk abin da nayi kada ya ci ba wane su, shi yasa yanzun nake son in an gama aikin nan, ba makamin nan ya ce zai karya asirin da suka yi mini ba? Yana karyawa zan ɓalle tsiya nima duk in ga bayansu,don duk sai na kashe su,ni kishiya in ba a lahira na aikata ba ko mai nayi mata ban huce ƙwanciyar da tayi na gadon mijina ta ɗanɗani kalar soyayyarshi ba,ta sha min zumar da ba kowane namiji ne ya iya ba da ita ba". Kari ta yi dariya, tare da cewa, shegiya mutuniyata,in na tuna baya,ba ki da ƙyau, amma tunda naga Alhajinki ya riƙe ki daga wasu mazan na san ba ki da sauƙi. Jummai ta ce,ai wallahi duk mazan da aka yi harka a can da ba su san komai ba,ke dai bari kawai." Suka tafa tare da sakin dariya.
Shi ko Uncle tsaye ya miƙe rike da waya yana jan tsaki layin Jabir ya nema, bayan ya ɗauka ya ce Jabiru don Allah maza-maza gobe da asubahi ka nufi makarantar su Beby,sun yi hutu ba'a ɗauko ta ba." Jabir ya ce,ko aje yanzun ne? Uncle ya ce a'a bana son tafiyar dare,kai dai don Allah kayi sammako. Sannan ya kashe wayar, ya dubi Hadiza wadda ta cika ta yi dam sakamakon yanda yake kiran Beby, ta ce to ita bata san hanya ba ne? Da bazata koma gida ba? Ya dube ta cike da haushin abinda Jummai ta mishi, sannan ya ja tsaki ya fita, takaici ya rufe ta,lallai zata ɗauki mataki a kan A'isha.
Daran dai Alhaji Saddiƙ sun yi ƙwanan doya da manja ne, shi da amarya.
Washegari Jabir yana idar da sallar Asubahi ya ɗauki hanyar makarantar su A'isha. Maigadin ya yi wa bayani tare kuma da neman taimakonshi,kan cewa gurin wa zai je yanzu? Maigadin ya ce "Gaskiya gara ka koma in dai ba sunanka aka saka ba kan cewa,kaine zaka ringa zuwa ɗaukar ta ba,don ba zasu ba ka ba, lokacin da Jabiru ya kira maigidanshi ya shaida mishi yanda suka yi da maigadi,shiru ya yi lokacin yana shirin zuwa mitin ne ya ce, "Jabiru ka koma gida nima zan taho yau insha Allahu,in na ɗaukota na dawo." Furucin ya firgita Hadiza saboda ɗauko ta daga makaranta za su koma gida? Ta hura hanci gami da girgiza kai, dole ma tasan me wannan yarinyar take taƙama dashi.
Ƙarfe taƙwas na dare suka sako ƙafa cikin gidan,ban da wayar shi da yake son ɗauka da ke cikin gidan,da baza ya shiga gidan ba,ko ta kan Hadiza be bi ba ya barta da ƴan aiki suna ta ya ta ɗiban kaya,ya yi cikin gidan,kai tsaye ɗakinshi ya nufa,ya ɗauko wayar da number ɗin (P.C) ɗin su A'isha ke ciki matsalar babu caji. Batir ɗin ta,ta hannunshi ya cire ya saka sim ɗin ya fito ya leƙa gurin Jummai kamar yanda ya zata bata nan sai su Suby ya nufi waje. Yana fita su Hadiza na shigowa, ya ce mata sai ya dawo bata amsa shi ba dama bai jira amsar ta ba ya tafi abinshi.
A'isha ta koma ciki, zuciyarta da damuwa. Nata ganin Uncle ya samu wadda ta fita yanzun zaya daina damuwa da ita, shi ko ya tafi ne cike da kewarta tare da son ganin ta dawo tamkar da.
Ran da Jummai zata fita daga girki, Alhajin ya sanar da ita cewa,yana son tafiya da Hadiza tafiyar nan da zai yi. Nan Hajiya Jummai ta shafa ma idanunta toka, ta shiga masifar cewa, ita bata yarda ba, don ya ga komai ya ce tana shiru shine zai zalince ta,to ita fa bata amince da wannan zancan ba.
Shiru ya yi yana kallonta,ga mamakinta sai taga ya miƙe tare da cewa, tafiya da Hadiza babu fashi, saboda matanshi uku ba zai tafi shi kaɗai ba,ta ce to dole sai da Hadiza? Ya ce,to gaya min da wadda zan tafi, A'isha tana makaranta,ke kuma ina ne ba mu je da ke ba? In bazaki manta ba,lokacin da aka ɗaura mana aure dake ko sati ɗaya ba muyi garin nan ba muka bazama duniya, wata shidda muna yawon amarci. Cikin waɗannan wa ya samu haka? A'isha ko airport ta taɓa zuwa ne?"
Hajiya Jummai ta fito tana cewa,na barka da Allah. Da kallo ya bita, ita wannan watau rashin mutuncin da take yi wa wasu shi ne ya soma zuwa kaina,ya yi ƙwafa,ko a jikinshi ya ɗauki amaryarshi suka nufi Phoenix.
Harkokinshi suna tafiya yanda yake so gefe kuma ga amarya.
Hadiza irin matan nan ne masu fi'ilin tsiya da ƙwarƙwasa,gata da son komai ace ita ce gaba, sannan tana da son ƙyale-ƙyale. A da Hadiza baƙa ce, amma yanzun fara ce tas,sai dai in ka kalli ƙafar zaka gane farin na mai ne. Tana da ƙiba kuma bata da tsawo,ga tumbi. Gaskiya sun yi soyayya ko ince suna soyewa. Tana matuƙar son Alhaji Saddiƙ.
#######
[12/12, 13:22] Ummi Tandama😇: *📗📗Page 7*
Ta fi son ace daga ita sai shi bata son ganin kowace mace kusa da shi, shi yasa take jin haushin wannan shegiyar Beby É—in da bakin shi ke yawan kira, don ta kula yanda yake yawan cewa Beby ko Jummai ba ya kira haka,tana burin maye gurbin Beby É—in nan.
Tun saura ƙwana huɗu a yiwa su A'isha hutu, makarantar kamar yadda ta saba ta samo tura ma dukkan iyayan ɗaliban nasu text cewa rana kaza ne za'ayi hutu, lokacin da saƙon ya isa ga wayar Uncle ba layin ba ne cikin wayarshi, tunda baya ƙasar ma. Kan wayar da layin ke ciki ma bada ita ya tafi ba, don haka bai samu saƙon ba, ballantana ya ce aje a ɗauke ta, ƙa'idar makarantar ba sa ba da ɗalibai sai dai in iyayansu ne ko waɗanda suka ɗauki nauyinsu. Sam Uncle bai san taƙamaiman ranar hutun ba, don haka koda ranar hutun ta zo A'isha ba taga anzo ɗaukarta ba,a ƙarshe bayan kowa ya watse nan shugaban makarantar suka shiga neman shi a cikin waya. A'isha ta ce, musu ya yi tafiya baya ma ƙasar gaba ki ɗaya. Don haka sai suka ba da ta gidan wata Malama da ke nan cikin makarantar.
Wannan lamarin ya ƙara sa A'isha yarda da cewa yanzun Uncle ya daina yi da ita, ya daina sonta inda da ne ba yanda za'ayi ya share ta, yanzun ya samu wata wadda ta fita, sanadin wannan yasa A'isha zama miskila.
Gidan Malama Salamatu, gida ne mai tsari da tarbiyyar Islama, tana da yara Æ´an biyu sa'annin A'isha, suna son Aisha sai dai ta kasa sakewa da su,ba ta cika magana ba, sai dai sun kula tana da yawan ibada. Malama Salamatu ma ta yaba da A'isha.
Ranar da ta cika ƙwana biyu ne ya ga saƙon ta cikin Internet ɗin shi, lokacin yana zaune yana duba saƙonni. Hadiza kuma an dage ana ta danƙara uwar ƙwalliya, faɗin innalillahi wa'inna ilaihir'raji'un ɗin da ya yi shi ne ya saka ta juyowa ta dubeshi,nan ya ɗauko wayarshi ya shiga neman layin Hajiya Jummai. Hajiya Jummai ta ɗauka lokacin ma tana gidan Kari, ya ce Jummai an ɗauko beby daga makaranta ne? Ta taɓa baki sannan ta ce, wacece haka? Cikin sauri ya ce "A'isha fa" ta ce,sallahu ka bari cewa a ɗauko ta? Sannan ta kashe wayarta, ta tsani wannan A'isha ballantana in yana faɗin Beby ɗin nan, ta ce ɗan rainin wayo, Kari ta ce,hala mutumin naki ne?" Ta ce shi ne mana,kin ji shi ne? A firgice wai an ɗauko A'isha daga makaranta? Karima ta ce, na kula duk da ya yi auran nan hankalinshi ya fi tafiya ga wannan A'ishan.
Jummai ta ce, shi yasa na tsane ta, har na fi jin kishinta akan Hadiza, duk da nasan Hadiza da uwarta Lanti ba ƙyalle ba ne? Kari ta ce"ai dole ne kifi jin kishin A'isha, tunda wanda ake kishin domin sa ya fi sonta,(ta ci gaba da cewa) ko me ya gani jikinta? Yarinya ba ƙugu ba sharaɓa babu nonon kirki. Koda yake kin san ƴan ƙauyan nan fa suna da mugayan malamai, sai a mallake miki miji a kan Naira ɗari ko ɗari biyu."
Tsaki Jummai ta ja,ai ba'a ƙwana a gado kullum, kuma nima na san ba don sun min asirin da duk abin da nayi kada ya ci ba wane su, shi yasa yanzun nake son in an gama aikin nan, ba makamin nan ya ce zai karya asirin da suka yi mini ba? Yana karyawa zan ɓalle tsiya nima duk in ga bayansu,don duk sai na kashe su,ni kishiya in ba a lahira na aikata ba ko mai nayi mata ban huce ƙwanciyar da tayi na gadon mijina ta ɗanɗani kalar soyayyarshi ba,ta sha min zumar da ba kowane namiji ne ya iya ba da ita ba". Kari ta yi dariya, tare da cewa, shegiya mutuniyata,in na tuna baya,ba ki da ƙyau, amma tunda naga Alhajinki ya riƙe ki daga wasu mazan na san ba ki da sauƙi. Jummai ta ce,ai wallahi duk mazan da aka yi harka a can da ba su san komai ba,ke dai bari kawai." Suka tafa tare da sakin dariya.
Shi ko Uncle tsaye ya miƙe rike da waya yana jan tsaki layin Jabir ya nema, bayan ya ɗauka ya ce Jabiru don Allah maza-maza gobe da asubahi ka nufi makarantar su Beby,sun yi hutu ba'a ɗauko ta ba." Jabir ya ce,ko aje yanzun ne? Uncle ya ce a'a bana son tafiyar dare,kai dai don Allah kayi sammako. Sannan ya kashe wayar, ya dubi Hadiza wadda ta cika ta yi dam sakamakon yanda yake kiran Beby, ta ce to ita bata san hanya ba ne? Da bazata koma gida ba? Ya dube ta cike da haushin abinda Jummai ta mishi, sannan ya ja tsaki ya fita, takaici ya rufe ta,lallai zata ɗauki mataki a kan A'isha.
Daran dai Alhaji Saddiƙ sun yi ƙwanan doya da manja ne, shi da amarya.
Washegari Jabir yana idar da sallar Asubahi ya ɗauki hanyar makarantar su A'isha. Maigadin ya yi wa bayani tare kuma da neman taimakonshi,kan cewa gurin wa zai je yanzu? Maigadin ya ce "Gaskiya gara ka koma in dai ba sunanka aka saka ba kan cewa,kaine zaka ringa zuwa ɗaukar ta ba,don ba zasu ba ka ba, lokacin da Jabiru ya kira maigidanshi ya shaida mishi yanda suka yi da maigadi,shiru ya yi lokacin yana shirin zuwa mitin ne ya ce, "Jabiru ka koma gida nima zan taho yau insha Allahu,in na ɗaukota na dawo." Furucin ya firgita Hadiza saboda ɗauko ta daga makaranta za su koma gida? Ta hura hanci gami da girgiza kai, dole ma tasan me wannan yarinyar take taƙama dashi.
Ƙarfe taƙwas na dare suka sako ƙafa cikin gidan,ban da wayar shi da yake son ɗauka da ke cikin gidan,da baza ya shiga gidan ba,ko ta kan Hadiza be bi ba ya barta da ƴan aiki suna ta ya ta ɗiban kaya,ya yi cikin gidan,kai tsaye ɗakinshi ya nufa,ya ɗauko wayar da number ɗin (P.C) ɗin su A'isha ke ciki matsalar babu caji. Batir ɗin ta,ta hannunshi ya cire ya saka sim ɗin ya fito ya leƙa gurin Jummai kamar yanda ya zata bata nan sai su Suby ya nufi waje. Yana fita su Hadiza na shigowa, ya ce mata sai ya dawo bata amsa shi ba dama bai jira amsar ta ba ya tafi abinshi.