Sashe 10
Mummunan Zato Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jabir ke jan motar har suka iso, ya kira (P.C) a waya in da ya tabbatar mishi cewa tana nan gidan wata Malama nan cikin makarantar yanzun zai yiwa Malamar waya,ya ƙara da cewa ba ya gari ne da yazo, amma su shiga Malamar zata fito, har ƙofar gidan Malama Salamatu wani malami ya kai su, sannan ya yi musu sallama a gidan lokacin A'isha har sun ƙwanta batayi bacci ba amma ta yi shiru cikin tunanin Uncle da abinda ya yi mata,sai taji ƙwanƙwasa ƙofa gami da sallama,ta amsa, sannan ta tashi ta buɗe Malama ta ce an zo ɗaukar ki A'isha kunna wuta. A'isha ta kunna wuta tare da cewa da wannan daren Momy? Haka ta ji ƴan biyu suna kiranta don haka ɗan zamanta a gidan itama take mata duk abinda taga yaran suna yi. Ta ce eh, fito da jakarki,ta koma ta kinkimo jakar Momy ta amsa tare da cewa ɗauko ɗayar, A'isha ta ce gashi su Hassana suna bacci ba mu yi sallama ba,ta ce ba komai zan sanar da su,in hutu ya ƙare ki ka dawo ina fata zaki zo? Ta ce insha Allah, har mota ta rakata. Sun gaisa da Uncle ya yi mata godiya sosai sannan ya yi mata alkhairi kamar yanda ya saba babu ƙirgawa. Aisha dai ta shige bayan mota ta yi shiru sam bata son komawa gidan rayuwar ƙwana uku a gidan Malama Salamatu ta yi mata daɗi.
Jabir na jan mota suna zaune a baya ƙala dai bata ce mishi ba tunda ya shigo motar suka ɗau hanya kasa jurewa ya yi ya lalibo hannunta ya saƙala yatsunshi cikin nata,bata hanashi ba sai dai bata kalleshi ba yanayin salon da yake yi gurin murza hannun nata kansa ta ji wani irin yanayi. Saitin kunnanta ya rusuna, ya raɗa mata cewa ki yi haƙuri Beby, nayi laifi,ba tare da ta dube shi ba ta ce name? Ya ce na manta na tafi na barki,ta girgiza kai tare da ɗaga kafaɗu,ai ba komai, rashin sakin fuskarta shi ne ya hanashi yi mata hira shiru har suka shiga harabar gidan sai dai hannunshi yana cikin nata. Jabir yana tsayawa ya fito ya buɗewa maigida ƙofa, Uncle ya ce kai mata kayan ciki Jabiru. Tana ƙoƙarin buɗe ƙofa ya jawo hannunta tsaya mana Beby ta koma ta zauna. Ya fuskance ta sosai, Beby kiyi haƙuri,ta ce me kayi min ne Uncle wai shin? Ya zuba mata idanu. Kina nufin ban miki komai ba? Ta girgiza kai tare da cewa, a'a. Ya ce,to in haka ne meye ki ka canza min,ki ka dake min ba kamar da ba? Na shiga wani hali Beby,hakan yana soya raina fa. Sai a nan ta dubeshi zuciyarta na gaya mata cewa da gaske ne zancan da yake miki da bai manta da ke har na tsawon kwana uku ba, duk da an mishi text amma a fili sai ta ce, kayi haƙuri to yanayin rayuwa ne ka san ya kan canza wata rana ƙila zan daina ya sake yin ƙasa da murya tare da cewa,haba Beby,wata rana fa ki ka ce? Ta ɗaga kai ya ce kenan ni da farin ciki sai wata rana kenan? Ta ce, Uncle ai kai ba zaka zama cikin baƙin ciki ba saboda kana da amarya in ba kaga fara'a ta ba ai zaka ga tata. Ga mamakin ta sai taji ya ce, haka ne, amma sai dai ni nafi son ganin taki ɗin,ta yi shiru,ya ce kin ji me nace? Ta dube shi duk da a duhu ne amma tana iya ganin annurin angonci a fuskarshi, kuma gashi ya tabbatar mata cewa yana ganin fara'ar amarya. Ƙila da amaryar ce zata ɗaure fuskar da sai yafi haka ruɗewa, ya ɗan matsa hannunta da ke cikin nashi,ta yi firgigit ta kalli gurin da yake, ya ce na sani kina tunanin abinda na yi miki ne ko? Ya ci gaba da sam ban za ci yin auran nan nawa zai ɓata ranki ba, da ban yi ba, ba tasan sanda ta ce Uhum ba, saboda ta san labari Uncle ya ke,wai kace baka san ran mace zai ɓaci ba,za ka yi mata fa kishiya ne, amma ka ce baka san yin hakan zai ɓata ranta ba, wannan ma hira ne,shi kam da ya fuskanci ba zata lallasu ba, sai ya ce shikenan mu shiga ciki.
Addu'a ce a bakinta, har ta buɗe ɗakinta, ta shiga. Da wanke toilet ta soma sannan ta kakkaɓe gadonta,ta kulle ƙofarta ta ƙwanta, cikin bacci ta ke jin ƙwanƙwasa ƙofa,ta kalli agogo sha biyu,a ranta ta ce to wanene? Maida kai ta yi ta ci gaba da baccinta, don bata zaci Uncle ba ne, tunda ba ya ƙwana ɗakinta ko ma ya ƙwanan baya kula ta.
Washegari da aiki ta tashi, ta yi sallar Asubahi,ci gaba ta yi da aikace-aikacenta, ta share ko'ina ta goge ta kunna turarukan wuta ko'ina ya ɗauki ƙamshi,ta faɗa toilet ta yo wanka ta fito tana yin filla-filla da kayanta. Nan ta dinga ɗago kayan da Uncle ya yi mata, lokacin yana ji da ita, ta cire su gefe. Sannan ta ciro zannuwa da lesuka tun na cikin aƙwatinta,ta zube su duk zata ba da a ɗin ke mata su ne. Yanzu tana son English wears gashi ba ta sa su ba, duk sun mata kaɗan. Sai wani (3)ne da t-shirt ɗin shi ta saka,ta cire saura ta zuba su cikin wata leda da niyyar zata ba Mima ƴar gidan Anty Sadiya, wanda zata ɗinka ɗin ma Anty Nafisa zata yi ma waya ta bada a ɗinko mata, tunda ba ta san inda zata kai ɗinkin ba, duk zamanta a gidan ba tayi wani ɗinki ba, sai dai Uncle ya siyo mata (r) kawai, zama da su Samira ya sa ta iya zama gaban madubi, duk da basa yi a makaranta, amma suna labarin mahimmancin yin ƙwalliya a gurin mace,su kan ce mata mace doki ce sai da gayu,su kan yi labarin cewa in sun yi aure zasu ringa yin ƙwalliya ga mazan nasu. Amina kan ce ai in auranta ya kusa ƙananan kaya zata shiga kasuwa ta jibgo, A'isha tana gaban madubi tana tuna hirarsu,nan ko ta zage ta zabga ƙwalliya ta saka sarƙa (passion) har da ta ƙafa da ƴankunne zobuna da warwaro da ta kalli kanta a madubi sai da ta furta ni ce kuwa? Ta gyara gashinta,tana cikin saka wayarta a caji taji ƙwanƙwasa ƙofa,ta zo bakin ƙofar ta ce, "Wane ne?" Muryar Uncle taji ya ce,ni ne Beby buɗe min,ta buɗe fuskarta ya soma kallo a ranshi ya ce jiya i yau waton babu fara'a kenan.
Ta kauce ya shiga sannan ta kulle ƙofar cike da mamaki ya bita da kallo ta burge shi fiye da tunaninta,sumar kanta da ke ƙwance a dokin wuyanta ta tsuma shi, kamar yanda ta saba ta tsugunna ta gaishe shi duk da ba fara'a ya ji daɗi ya amsa tare da cewa lafiya lau Beby,kai amma fa kin yi ƙyau, shiru ta yi tana zaune nan inda ta gaishe shin, tana wasa da zoben dake ƙaramin yatsanta,ya dubi ɗakin a zuciyarshi ya ce yarinyar tana da tsafta sosai, ya ce Beby ina so in Zauna da ku in kin gama yanzun cikin falona, ta ce, to ina zuwa.
Duk sun hallara a falon A'isha kurum suke jira. Hadiza takaici Hajiya Jummai takaici gashi su kansu sun ƙi kallon juna tsakanin Jumman da Hadiza sai ƴan harare-harare. Aisha kamar ta saka hijabi sai kuma ta fasa,ta ɗauki hula baƙa kalar wandon tasa, gashinta kuma ya bazu a bayanta,silifas baƙi ta saka sannan ta ɗauki wayarta ta nufi falon.
Hadiza da ta ƙosa taga A'isha sai da numfashinta ya kusa ɗaukewa lokacin da A'ishar ta shigo da sallama, Uncle ne kurum ya amsa. A'isha ta ƙara tsare gida, ganin amaryar ta su duk suna zaune ne kan kujera mai zaman mutum uku sun sa shi a tsakiya.
########
[12/13, 07:51] Ummi Tandama😇: *📗📗Page 8*
Aisha me ladabi sai kurum ta zauna kasa a gabanshi ta kalli hajiya Jummai ta ce,Hajiya ina kwana? Itama ta cije ta ce,lafiya lau Aisha kin dawo kalau? Ba tare da ta dubu Hadiza ba,ta ce ina kwana? Yi tayi tamkar ba ta ji ta ba,sai da Uncle ya ce ana gaishe ki,cikin yatsina ta amsa,shi ko sai kallon Aisha yake yi,ta dube shi ta ce Uncle gani.
Hadiza ta kuma cika da mamaki ta maimaita kalmar tace Uncle? Lallai wannan yar bariki ce,dubi yanda tayi wata shiga tana ta yatsina sai kace yar wani da wata ga wani ladabin kinibibi za a wani zauna gabanshi,maigidan ya yi gyaran murya ya ce,dalilin tara ku a nan shi ne,ina so in kara tunatar daku cewa yanzun kun zama ku uku don haka sai ku yi ta hakuri da juna,musamman ke Jummai,tunda ke ce babba,ku ma dole ne kuyi mata biyayya ban da raini,sannan ga masu aiki nan ni nake biya,don haka na kowane in ma basu isa ba a nemo wasu,haka nan duk mai wata bukata sai ya tambaye ni ,game da kwana kuma sai kuyi shawara dai dai ko bibbiyu?."
Hajiya Jummai ta ce,bibbiyun za'ayi, Hadiza ta dube ta gami da tabe baki ta ce,bibbiyu? Gaskiya ba zan iya kwana hudu ban gan shi ba,Hajiya Jummai ta dube ta,ko Aisha mamaki ya cika ta,wannan tana nufin tafi kowa son shi kenan? Jummai kuwa cewa tayi sannunki da karfin hali,kina nufin kin fini son shi ne? Hadiza ta ce kina shakka kenan? Wani murmushi Jummai ta yi irin wanda ya ke nufin baki san da wadda ki ke magana ba. Sannan ta ce kin tafka kuskure,amma za ki ga aya.
Jabir na jan mota suna zaune a baya ƙala dai bata ce mishi ba tunda ya shigo motar suka ɗau hanya kasa jurewa ya yi ya lalibo hannunta ya saƙala yatsunshi cikin nata,bata hanashi ba sai dai bata kalleshi ba yanayin salon da yake yi gurin murza hannun nata kansa ta ji wani irin yanayi. Saitin kunnanta ya rusuna, ya raɗa mata cewa ki yi haƙuri Beby, nayi laifi,ba tare da ta dube shi ba ta ce name? Ya ce na manta na tafi na barki,ta girgiza kai tare da ɗaga kafaɗu,ai ba komai, rashin sakin fuskarta shi ne ya hanashi yi mata hira shiru har suka shiga harabar gidan sai dai hannunshi yana cikin nata. Jabir yana tsayawa ya fito ya buɗewa maigida ƙofa, Uncle ya ce kai mata kayan ciki Jabiru. Tana ƙoƙarin buɗe ƙofa ya jawo hannunta tsaya mana Beby ta koma ta zauna. Ya fuskance ta sosai, Beby kiyi haƙuri,ta ce me kayi min ne Uncle wai shin? Ya zuba mata idanu. Kina nufin ban miki komai ba? Ta girgiza kai tare da cewa, a'a. Ya ce,to in haka ne meye ki ka canza min,ki ka dake min ba kamar da ba? Na shiga wani hali Beby,hakan yana soya raina fa. Sai a nan ta dubeshi zuciyarta na gaya mata cewa da gaske ne zancan da yake miki da bai manta da ke har na tsawon kwana uku ba, duk da an mishi text amma a fili sai ta ce, kayi haƙuri to yanayin rayuwa ne ka san ya kan canza wata rana ƙila zan daina ya sake yin ƙasa da murya tare da cewa,haba Beby,wata rana fa ki ka ce? Ta ɗaga kai ya ce kenan ni da farin ciki sai wata rana kenan? Ta ce, Uncle ai kai ba zaka zama cikin baƙin ciki ba saboda kana da amarya in ba kaga fara'a ta ba ai zaka ga tata. Ga mamakin ta sai taji ya ce, haka ne, amma sai dai ni nafi son ganin taki ɗin,ta yi shiru,ya ce kin ji me nace? Ta dube shi duk da a duhu ne amma tana iya ganin annurin angonci a fuskarshi, kuma gashi ya tabbatar mata cewa yana ganin fara'ar amarya. Ƙila da amaryar ce zata ɗaure fuskar da sai yafi haka ruɗewa, ya ɗan matsa hannunta da ke cikin nashi,ta yi firgigit ta kalli gurin da yake, ya ce na sani kina tunanin abinda na yi miki ne ko? Ya ci gaba da sam ban za ci yin auran nan nawa zai ɓata ranki ba, da ban yi ba, ba tasan sanda ta ce Uhum ba, saboda ta san labari Uncle ya ke,wai kace baka san ran mace zai ɓaci ba,za ka yi mata fa kishiya ne, amma ka ce baka san yin hakan zai ɓata ranta ba, wannan ma hira ne,shi kam da ya fuskanci ba zata lallasu ba, sai ya ce shikenan mu shiga ciki.
Addu'a ce a bakinta, har ta buɗe ɗakinta, ta shiga. Da wanke toilet ta soma sannan ta kakkaɓe gadonta,ta kulle ƙofarta ta ƙwanta, cikin bacci ta ke jin ƙwanƙwasa ƙofa,ta kalli agogo sha biyu,a ranta ta ce to wanene? Maida kai ta yi ta ci gaba da baccinta, don bata zaci Uncle ba ne, tunda ba ya ƙwana ɗakinta ko ma ya ƙwanan baya kula ta.
Washegari da aiki ta tashi, ta yi sallar Asubahi,ci gaba ta yi da aikace-aikacenta, ta share ko'ina ta goge ta kunna turarukan wuta ko'ina ya ɗauki ƙamshi,ta faɗa toilet ta yo wanka ta fito tana yin filla-filla da kayanta. Nan ta dinga ɗago kayan da Uncle ya yi mata, lokacin yana ji da ita, ta cire su gefe. Sannan ta ciro zannuwa da lesuka tun na cikin aƙwatinta,ta zube su duk zata ba da a ɗin ke mata su ne. Yanzu tana son English wears gashi ba ta sa su ba, duk sun mata kaɗan. Sai wani (3)ne da t-shirt ɗin shi ta saka,ta cire saura ta zuba su cikin wata leda da niyyar zata ba Mima ƴar gidan Anty Sadiya, wanda zata ɗinka ɗin ma Anty Nafisa zata yi ma waya ta bada a ɗinko mata, tunda ba ta san inda zata kai ɗinkin ba, duk zamanta a gidan ba tayi wani ɗinki ba, sai dai Uncle ya siyo mata (r) kawai, zama da su Samira ya sa ta iya zama gaban madubi, duk da basa yi a makaranta, amma suna labarin mahimmancin yin ƙwalliya a gurin mace,su kan ce mata mace doki ce sai da gayu,su kan yi labarin cewa in sun yi aure zasu ringa yin ƙwalliya ga mazan nasu. Amina kan ce ai in auranta ya kusa ƙananan kaya zata shiga kasuwa ta jibgo, A'isha tana gaban madubi tana tuna hirarsu,nan ko ta zage ta zabga ƙwalliya ta saka sarƙa (passion) har da ta ƙafa da ƴankunne zobuna da warwaro da ta kalli kanta a madubi sai da ta furta ni ce kuwa? Ta gyara gashinta,tana cikin saka wayarta a caji taji ƙwanƙwasa ƙofa,ta zo bakin ƙofar ta ce, "Wane ne?" Muryar Uncle taji ya ce,ni ne Beby buɗe min,ta buɗe fuskarta ya soma kallo a ranshi ya ce jiya i yau waton babu fara'a kenan.
Ta kauce ya shiga sannan ta kulle ƙofar cike da mamaki ya bita da kallo ta burge shi fiye da tunaninta,sumar kanta da ke ƙwance a dokin wuyanta ta tsuma shi, kamar yanda ta saba ta tsugunna ta gaishe shi duk da ba fara'a ya ji daɗi ya amsa tare da cewa lafiya lau Beby,kai amma fa kin yi ƙyau, shiru ta yi tana zaune nan inda ta gaishe shin, tana wasa da zoben dake ƙaramin yatsanta,ya dubi ɗakin a zuciyarshi ya ce yarinyar tana da tsafta sosai, ya ce Beby ina so in Zauna da ku in kin gama yanzun cikin falona, ta ce, to ina zuwa.
Duk sun hallara a falon A'isha kurum suke jira. Hadiza takaici Hajiya Jummai takaici gashi su kansu sun ƙi kallon juna tsakanin Jumman da Hadiza sai ƴan harare-harare. Aisha kamar ta saka hijabi sai kuma ta fasa,ta ɗauki hula baƙa kalar wandon tasa, gashinta kuma ya bazu a bayanta,silifas baƙi ta saka sannan ta ɗauki wayarta ta nufi falon.
Hadiza da ta ƙosa taga A'isha sai da numfashinta ya kusa ɗaukewa lokacin da A'ishar ta shigo da sallama, Uncle ne kurum ya amsa. A'isha ta ƙara tsare gida, ganin amaryar ta su duk suna zaune ne kan kujera mai zaman mutum uku sun sa shi a tsakiya.
########
[12/13, 07:51] Ummi Tandama😇: *📗📗Page 8*
Aisha me ladabi sai kurum ta zauna kasa a gabanshi ta kalli hajiya Jummai ta ce,Hajiya ina kwana? Itama ta cije ta ce,lafiya lau Aisha kin dawo kalau? Ba tare da ta dubu Hadiza ba,ta ce ina kwana? Yi tayi tamkar ba ta ji ta ba,sai da Uncle ya ce ana gaishe ki,cikin yatsina ta amsa,shi ko sai kallon Aisha yake yi,ta dube shi ta ce Uncle gani.
Hadiza ta kuma cika da mamaki ta maimaita kalmar tace Uncle? Lallai wannan yar bariki ce,dubi yanda tayi wata shiga tana ta yatsina sai kace yar wani da wata ga wani ladabin kinibibi za a wani zauna gabanshi,maigidan ya yi gyaran murya ya ce,dalilin tara ku a nan shi ne,ina so in kara tunatar daku cewa yanzun kun zama ku uku don haka sai ku yi ta hakuri da juna,musamman ke Jummai,tunda ke ce babba,ku ma dole ne kuyi mata biyayya ban da raini,sannan ga masu aiki nan ni nake biya,don haka na kowane in ma basu isa ba a nemo wasu,haka nan duk mai wata bukata sai ya tambaye ni ,game da kwana kuma sai kuyi shawara dai dai ko bibbiyu?."
Hajiya Jummai ta ce,bibbiyun za'ayi, Hadiza ta dube ta gami da tabe baki ta ce,bibbiyu? Gaskiya ba zan iya kwana hudu ban gan shi ba,Hajiya Jummai ta dube ta,ko Aisha mamaki ya cika ta,wannan tana nufin tafi kowa son shi kenan? Jummai kuwa cewa tayi sannunki da karfin hali,kina nufin kin fini son shi ne? Hadiza ta ce kina shakka kenan? Wani murmushi Jummai ta yi irin wanda ya ke nufin baki san da wadda ki ke magana ba. Sannan ta ce kin tafka kuskure,amma za ki ga aya.