Sashe 7
Mummunan Zato Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar ko runtsawa Hajiya Jummai bata yi ba,ta ma rasa me zata yi taji sanyi? Ta san Hajiya Lanti kamar yunwar cikinta, duk cikin dangin maigidan nata ɓarayin mahaifinshi ba mafaɗaciya irinta. In ma asirin ne take taƙama dashi ta san zasu goga,don haka dolenta ta nutsu kada ta yi saurin nuna za ta ɗauki wani mataki kan Hadiza,ta sani su Hajiya Lanti lashe money ce,ta jima tana son ƴarta Hadiza ta auri Alhaji Saddiƙ,don dukiyarshi. Wannan lokacin bata damu da cewa ƴar ta mutu ko tayi rai ba,in har za su samu kuɗi Hajiya Lanti gogaggiya ce ta samu duniya, ita ce mace mai faɗa a ji cikin matan Alhaji Sunusi,ku san ita ce ke juya gidan son ranta. Ta taɓa jin labarin ta gurin Boka na kan dutse. Lokacin da taje da buƙatar mallakar mijinta a hannu,Boka na kan dutse ya shaida mata cewa,wata Hajiya Lanti ita ce mace mai tsananin Sa'a, wadda ta samu mallaka ta ƙarshe a gurin Aljanunmu.
Tun daga kanta har zuwa yau ba mu kuma ba da irin wannan mallakar ba, bata samu matsala a gurin gano kowace ce Hajiya Lantin ba, sai dai ta gano dangin mijinta ce, don haka ta haƙura da ta so su haɗa ƙawance da ita, da irin waɗannan tunane-tunanen ne gari ya waye mata.
Ita ko A'isha ba ta san me ake ciki ba, suna ta fama da jarabawar da ke fuskanto su lokacin bikin Uncle baifi sati biyu ba, da yake Uncle bai É—auki bikin da wani muhimmanci ba, ya yi zuwa gurin A'isha ya kai nawa, amma bai ce mata komai ba game da bikin nashi,hasalima shi mantawa yake yi da batun wani auran shi. Bai ma san dalili ba,in dai yana tare da A'isha ya kan manta da duk wasu lamura na shi, ballantana ma yanzun da ta mallaki abin kallo.
Yana son ganinta cikin kayan makaranta,ko na zaman cikin makaranta , har dai ace bata saka hijabi ba,ƙirjinta yana mishi ƙyawun kallo. Sirantakarta ce kurum yake ganin matsala sai dai yana son yanda take da tsawo,dan tsayinta na sa shi jin alfaharin kasancewar ta matarshi,yana son taɓa jikinta sai dai yanda take ba shi girma na saka shi yaji nauyinta.
Wani daÉ—i yake ji duk lokacin da ya riki tafin hannunta, ta tsaya mishi cikin zuciya kuma bai rufe mata ba,yana yawan shaida mata yanda yake jinta cikin zuciyarshi, wanda ita kuma haka yana saka ta jin daÉ—i har ma tayi kewarshi,in ya yi kwanaki bai zo ba.
Yau saura sati ɗaya bikin shi,ya yi dai ta maza ya kira Abbanta a waya ya shaida mishi cewa an bashi mata,wan mahaifinshi ya cigaba da cewa Friend wallahi ba da son raina zan yi auren nan ba, zan yi ne kawai don bani da yanda zan yi, maganar ta biyo ta gurin Hajiyarmu da Alhajinmu ne. Abba ya ce, "Haba Friend,ai ko kai ne ka gani ka ce kana so koyi kayi da sunna, ina fata dai A'isha bata ɗaga hankalinta ba? Don ka san mata ba su da hankali, yanzun sai taga cewa ita ba'a yi mata daidai ba, bayan Allah ne da kanshi ya umurce mu, Uncle ya ce, "Ai ita wannan baiwar Allah ce, wallahi friend tunda yarinyar nan ta zo gidana ko sau ɗaya ban taɓa ganin fushinta ba, kullum cikin fara'a take. Abba ya ce, Alhamdulillah, sai in mun zo insha Allah zan zo ɗaurin aure."
Uncle ya ce "To shi kenan, sai ka zo kenan."
Washegari Sunday (lahadi), Uncle gurin Beby ya nufa, suna zaune suna fuskantar juna, ta rasa dalili in tana kusa da Uncle sai ta samu kanta cikin wani yanayi da ba zata iya cewa wane iri ba ne.
Ya dube ta da murmushi, Beby kullum ƙara ƙyau da girma ki ke yi,ta ce ko dai tsawo? Ya ce,kinsan cewa tsawonki yana ɗaya daga cikin abinda yasa nake sonki? Ta rufe fuska da dogayen tafukan hannunta, sannan ta ce, wai da gaske kana sona? Ya ce, sosai ma, kada ki ga yanda na ƙosa kuyi hutu wannan karon domin na san yanzun kinsan abinda ake yi a samu ciki ko? Cikin cinya ta saka kanta, sannan ta ce ni ban sani ba fa,ya ce to ai koya miki zan yi,kina so? Ta girgiza kai alamun a'a,ya ce amma da ai kin ce in nuna miki kenan kin bincika kamar yanda na ce,kafin ta yi magana wayarshi ta soma ruri,yana cirowa yaga Hadiza ce, bayan sun gaisa take cewa wai ƙawayanta zasu zo amsar kuɗi gurinshi zasu zo ko gurin abokanshi? Ya ce, mata ba ko ɗaya,su gaya mata ko nawa ne sai tayo mishi waya zaya aiko a kawo mata, ta ce shi kenan. Ya dubi A'isha wadda zuciyarta ke son sanin wacece Hadiza? Ya ce Beby dama na zo ne da magana sai kuma na manta kin san cewa in ina kusa da ke ina manta komai da komai ne? Ta yi ƴar dariya tare da cewa, wace magana ce? Ya ce, "Beby mata aka bani." Ta kafa mishi idanu,ko ƙiftawa sannan ta ce,ban gane ba? Sai kuma ya samu kanshi da ɗari-ɗarin gaya mata, sai dai dole ne ma ya daure ya sanar da ita saboda ance magana zarar bunu, kuma ya riga ya furta. Ya ce, "kin san Baba Alhaji Sunusi?" Ta girgiza kai ni ban san shi ba,ya ce kin san Hadiza? Haushi ya ma hanata magana, kallonshi kawai takeyi,ya ce ita ce aka bani ƴar wan Babanmu ce,yau saura ƙwana shida bikin."
Idanu A'isha ta zaro, saura ƙwana shidda? Ta taɓe baki, sannan ta miƙe tsaye tare da cewa, "Allah ya ba da zaman lafiya." Ta nufi cikin makaranta,sam bai za ci haka daga gareta ba, ita ko ko gani batayi, ta isa ɗakinsu kan gado ta ƙwanta, ga mamakin ta sai kurum ta ji hawaye suna ƙwaranya a kan kumatunta.
Wato ita Uncle zaya yi wa haka? Wai an bashi mata kenan, ita ba son ta yake ba,dama bai wani damu da ita ba,shi kenan yanzun zaya daina gaya mata kalamai masu daɗi, haba ita ta sani in ba baya son ta ba ai bazai kasa kula ta ba,bai taɓa neman ta ba haba ya ci ace tun tuni ma ta gano wannan matsalar, amma ba komai yaje ya yi ta yin auran, Umma ta ce,in bana gyara mishi shimfiɗa sai ya ƙara aure, duk hutu sai ta gyara mishi ɗaki amma hakan bai sa ya sota ba. Tana cikin wannan halin su Samira suka shigo, cikin sauri suka isa gurinta, nan suka shiga tambayarta abinda ya same ta. Sun ruɗe ƙwarai,domin ba su taɓa ganin A'isha musty cikin wannan halin ba.
Samira ta ce,"A'isha Musty me ya same ki ne? Don Allah tashi ki ji mu." Jin lallashin da suke mata ya saka ta kukan sosai,ba ta iya cewa komai ba,sai da tayi ma isarta sannan ta share hawayenta. Samira ta ce,me ya same ki? Wane ne ya ɓata miki rai? Ta ce, Uncle ɗina ne. Amina ta ce,me ya yi miki suka haɗa baki gurin cewa, Uncle ɗin ki dake matuƙar ji da ke? Ta ce,wai fa aure zai yi, dariya ta kama su,don zai yi aure ke ba abin murnarki ba ne? Ta yi shiru ita ta manta ma da ba su san cewa Uncle mijinta ne ba,don haka sai ta ce ai ba zaku gane ba ne, duk yanda muke da Uncle wai ace sai yau zai gayan bikinshi saura ƙwana shida bayan duk sati sai ya zo,ni kun ji damuwata." Suka ce ki mishi uzuri,ki ka sani ko abin ne yazo mishi ba cikin shiri ba?" Ta ce,Umh, daga nan ba ta sake cewa ƙala ba, domin ta gane ba zasu fahimce ta ba.
Tun daga ranar ba ta da sukuni, duk bayan awa ɗaya sai ta lissafa sauran ƙwanakin da suka rage na bikin Uncle ɗin nata,su ko su Samira mita suke mata kan cewa ta yi wa Uncle ɗinta afuwa, tare da ba shi uzuri. Ita ko Amina cewa take ina ma ba lokacin makaranta ba ne,su zo mata biki har ma su ga Antin tata,wato amaryar Uncle ɗin nata,a cewarsu ta yi dacen miji. A'isha kan ja tsaki tare da cewa, "Allah ya sutura,ta zama Antynta,su kuma suce dole ne tunda tana auren Uncle ɗinta. Aisha kan yi tsaki ta yi shiru kurum.
Shima Uncle na shi gefen yana cikin damuwa, wato damuwar Beby ita ce ta É—aga hankalinshi. In ya tuna yanda ta wuce yana kiranta Beby-beby tamkar ba ta ji shi ba haka ta yi. Dama Beby tana fushi? Itama kishi kenan gare ta? To me yasa ba ta kishi da Jummai sam? Koda yaushe tunanin A'isha ke ranshi, tamkar ya ce ya fasa auran yake ji. Cikin haka aka shiga bikin.
Abba ya shigo Katsina,ana gobe ɗaurin aure ka ji daren da ya hana mutum huɗu bacci, A'isha ƙwana tayi sallah tare da addu'o'i, tafi maida hankali ne ga roƙon Allah ya rage mata kishi cikin zuciyarta. Jummai kuwa ƙwana ta yi neman mafita inda ta farka da mummunan ciwon kai...
########
[12/11, 21:33] Ummi Tandama😇: *📗📗 Page 6*
Hadiza kuwa ta ƙwana da farin cikin samun mijin nunawa Sa'a ga kuɗi ga ƙwarjini,shi kuwa Uncle tunanin Beby ne ya hanashi bacci,ya ƙosa gari ya waye sati ya je school ɗin shi da Abbanta.
Aisha ta farka damuwar da ɗan sauki,ta yi tunanin gara ta rungumi ƙaddara tunda auren babu fashi,sai dai matsalarta ɗaya,dama Uncle ba ya son ta? Ta kan ba kanta amsa da cewa eh,tunda gashi ya yi wata a madadinta. Tana son samun natsuwa badan komai ba sai don jarabawar da ke tunkaro su,nan da satin da zasu shiga,ta sani ƙarƙari nan da sati uku za su yi hutu maimakon Uncle ya bari sai sunyi hutun ya yi auran. Sai kuma tayi tsaki ta ce, ita dai tana son cire batun auren nan na Uncle daga zuciyarta.
An ɗaura auran Uncle da Hadiza da misalin ƙarfe ɗaya da rabi na ranar asabar, bayan an tashi daga sallah,ko jiran walimar abokan da nashi suka shirya bai yi ba,yaja Abba da cewa su zo suje gurin Beby a makaranta, Abba ya ce a'a ka barta kawai,ni yanzun zan ɗauki hanyar garinmu."
Tun daga kanta har zuwa yau ba mu kuma ba da irin wannan mallakar ba, bata samu matsala a gurin gano kowace ce Hajiya Lantin ba, sai dai ta gano dangin mijinta ce, don haka ta haƙura da ta so su haɗa ƙawance da ita, da irin waɗannan tunane-tunanen ne gari ya waye mata.
Ita ko A'isha ba ta san me ake ciki ba, suna ta fama da jarabawar da ke fuskanto su lokacin bikin Uncle baifi sati biyu ba, da yake Uncle bai É—auki bikin da wani muhimmanci ba, ya yi zuwa gurin A'isha ya kai nawa, amma bai ce mata komai ba game da bikin nashi,hasalima shi mantawa yake yi da batun wani auran shi. Bai ma san dalili ba,in dai yana tare da A'isha ya kan manta da duk wasu lamura na shi, ballantana ma yanzun da ta mallaki abin kallo.
Yana son ganinta cikin kayan makaranta,ko na zaman cikin makaranta , har dai ace bata saka hijabi ba,ƙirjinta yana mishi ƙyawun kallo. Sirantakarta ce kurum yake ganin matsala sai dai yana son yanda take da tsawo,dan tsayinta na sa shi jin alfaharin kasancewar ta matarshi,yana son taɓa jikinta sai dai yanda take ba shi girma na saka shi yaji nauyinta.
Wani daÉ—i yake ji duk lokacin da ya riki tafin hannunta, ta tsaya mishi cikin zuciya kuma bai rufe mata ba,yana yawan shaida mata yanda yake jinta cikin zuciyarshi, wanda ita kuma haka yana saka ta jin daÉ—i har ma tayi kewarshi,in ya yi kwanaki bai zo ba.
Yau saura sati ɗaya bikin shi,ya yi dai ta maza ya kira Abbanta a waya ya shaida mishi cewa an bashi mata,wan mahaifinshi ya cigaba da cewa Friend wallahi ba da son raina zan yi auren nan ba, zan yi ne kawai don bani da yanda zan yi, maganar ta biyo ta gurin Hajiyarmu da Alhajinmu ne. Abba ya ce, "Haba Friend,ai ko kai ne ka gani ka ce kana so koyi kayi da sunna, ina fata dai A'isha bata ɗaga hankalinta ba? Don ka san mata ba su da hankali, yanzun sai taga cewa ita ba'a yi mata daidai ba, bayan Allah ne da kanshi ya umurce mu, Uncle ya ce, "Ai ita wannan baiwar Allah ce, wallahi friend tunda yarinyar nan ta zo gidana ko sau ɗaya ban taɓa ganin fushinta ba, kullum cikin fara'a take. Abba ya ce, Alhamdulillah, sai in mun zo insha Allah zan zo ɗaurin aure."
Uncle ya ce "To shi kenan, sai ka zo kenan."
Washegari Sunday (lahadi), Uncle gurin Beby ya nufa, suna zaune suna fuskantar juna, ta rasa dalili in tana kusa da Uncle sai ta samu kanta cikin wani yanayi da ba zata iya cewa wane iri ba ne.
Ya dube ta da murmushi, Beby kullum ƙara ƙyau da girma ki ke yi,ta ce ko dai tsawo? Ya ce,kinsan cewa tsawonki yana ɗaya daga cikin abinda yasa nake sonki? Ta rufe fuska da dogayen tafukan hannunta, sannan ta ce, wai da gaske kana sona? Ya ce, sosai ma, kada ki ga yanda na ƙosa kuyi hutu wannan karon domin na san yanzun kinsan abinda ake yi a samu ciki ko? Cikin cinya ta saka kanta, sannan ta ce ni ban sani ba fa,ya ce to ai koya miki zan yi,kina so? Ta girgiza kai alamun a'a,ya ce amma da ai kin ce in nuna miki kenan kin bincika kamar yanda na ce,kafin ta yi magana wayarshi ta soma ruri,yana cirowa yaga Hadiza ce, bayan sun gaisa take cewa wai ƙawayanta zasu zo amsar kuɗi gurinshi zasu zo ko gurin abokanshi? Ya ce, mata ba ko ɗaya,su gaya mata ko nawa ne sai tayo mishi waya zaya aiko a kawo mata, ta ce shi kenan. Ya dubi A'isha wadda zuciyarta ke son sanin wacece Hadiza? Ya ce Beby dama na zo ne da magana sai kuma na manta kin san cewa in ina kusa da ke ina manta komai da komai ne? Ta yi ƴar dariya tare da cewa, wace magana ce? Ya ce, "Beby mata aka bani." Ta kafa mishi idanu,ko ƙiftawa sannan ta ce,ban gane ba? Sai kuma ya samu kanshi da ɗari-ɗarin gaya mata, sai dai dole ne ma ya daure ya sanar da ita saboda ance magana zarar bunu, kuma ya riga ya furta. Ya ce, "kin san Baba Alhaji Sunusi?" Ta girgiza kai ni ban san shi ba,ya ce kin san Hadiza? Haushi ya ma hanata magana, kallonshi kawai takeyi,ya ce ita ce aka bani ƴar wan Babanmu ce,yau saura ƙwana shida bikin."
Idanu A'isha ta zaro, saura ƙwana shidda? Ta taɓe baki, sannan ta miƙe tsaye tare da cewa, "Allah ya ba da zaman lafiya." Ta nufi cikin makaranta,sam bai za ci haka daga gareta ba, ita ko ko gani batayi, ta isa ɗakinsu kan gado ta ƙwanta, ga mamakin ta sai kurum ta ji hawaye suna ƙwaranya a kan kumatunta.
Wato ita Uncle zaya yi wa haka? Wai an bashi mata kenan, ita ba son ta yake ba,dama bai wani damu da ita ba,shi kenan yanzun zaya daina gaya mata kalamai masu daɗi, haba ita ta sani in ba baya son ta ba ai bazai kasa kula ta ba,bai taɓa neman ta ba haba ya ci ace tun tuni ma ta gano wannan matsalar, amma ba komai yaje ya yi ta yin auran, Umma ta ce,in bana gyara mishi shimfiɗa sai ya ƙara aure, duk hutu sai ta gyara mishi ɗaki amma hakan bai sa ya sota ba. Tana cikin wannan halin su Samira suka shigo, cikin sauri suka isa gurinta, nan suka shiga tambayarta abinda ya same ta. Sun ruɗe ƙwarai,domin ba su taɓa ganin A'isha musty cikin wannan halin ba.
Samira ta ce,"A'isha Musty me ya same ki ne? Don Allah tashi ki ji mu." Jin lallashin da suke mata ya saka ta kukan sosai,ba ta iya cewa komai ba,sai da tayi ma isarta sannan ta share hawayenta. Samira ta ce,me ya same ki? Wane ne ya ɓata miki rai? Ta ce, Uncle ɗina ne. Amina ta ce,me ya yi miki suka haɗa baki gurin cewa, Uncle ɗin ki dake matuƙar ji da ke? Ta ce,wai fa aure zai yi, dariya ta kama su,don zai yi aure ke ba abin murnarki ba ne? Ta yi shiru ita ta manta ma da ba su san cewa Uncle mijinta ne ba,don haka sai ta ce ai ba zaku gane ba ne, duk yanda muke da Uncle wai ace sai yau zai gayan bikinshi saura ƙwana shida bayan duk sati sai ya zo,ni kun ji damuwata." Suka ce ki mishi uzuri,ki ka sani ko abin ne yazo mishi ba cikin shiri ba?" Ta ce,Umh, daga nan ba ta sake cewa ƙala ba, domin ta gane ba zasu fahimce ta ba.
Tun daga ranar ba ta da sukuni, duk bayan awa ɗaya sai ta lissafa sauran ƙwanakin da suka rage na bikin Uncle ɗin nata,su ko su Samira mita suke mata kan cewa ta yi wa Uncle ɗinta afuwa, tare da ba shi uzuri. Ita ko Amina cewa take ina ma ba lokacin makaranta ba ne,su zo mata biki har ma su ga Antin tata,wato amaryar Uncle ɗin nata,a cewarsu ta yi dacen miji. A'isha kan ja tsaki tare da cewa, "Allah ya sutura,ta zama Antynta,su kuma suce dole ne tunda tana auren Uncle ɗinta. Aisha kan yi tsaki ta yi shiru kurum.
Shima Uncle na shi gefen yana cikin damuwa, wato damuwar Beby ita ce ta É—aga hankalinshi. In ya tuna yanda ta wuce yana kiranta Beby-beby tamkar ba ta ji shi ba haka ta yi. Dama Beby tana fushi? Itama kishi kenan gare ta? To me yasa ba ta kishi da Jummai sam? Koda yaushe tunanin A'isha ke ranshi, tamkar ya ce ya fasa auran yake ji. Cikin haka aka shiga bikin.
Abba ya shigo Katsina,ana gobe ɗaurin aure ka ji daren da ya hana mutum huɗu bacci, A'isha ƙwana tayi sallah tare da addu'o'i, tafi maida hankali ne ga roƙon Allah ya rage mata kishi cikin zuciyarta. Jummai kuwa ƙwana ta yi neman mafita inda ta farka da mummunan ciwon kai...
########
[12/11, 21:33] Ummi Tandama😇: *📗📗 Page 6*
Hadiza kuwa ta ƙwana da farin cikin samun mijin nunawa Sa'a ga kuɗi ga ƙwarjini,shi kuwa Uncle tunanin Beby ne ya hanashi bacci,ya ƙosa gari ya waye sati ya je school ɗin shi da Abbanta.
Aisha ta farka damuwar da ɗan sauki,ta yi tunanin gara ta rungumi ƙaddara tunda auren babu fashi,sai dai matsalarta ɗaya,dama Uncle ba ya son ta? Ta kan ba kanta amsa da cewa eh,tunda gashi ya yi wata a madadinta. Tana son samun natsuwa badan komai ba sai don jarabawar da ke tunkaro su,nan da satin da zasu shiga,ta sani ƙarƙari nan da sati uku za su yi hutu maimakon Uncle ya bari sai sunyi hutun ya yi auran. Sai kuma tayi tsaki ta ce, ita dai tana son cire batun auren nan na Uncle daga zuciyarta.
An ɗaura auran Uncle da Hadiza da misalin ƙarfe ɗaya da rabi na ranar asabar, bayan an tashi daga sallah,ko jiran walimar abokan da nashi suka shirya bai yi ba,yaja Abba da cewa su zo suje gurin Beby a makaranta, Abba ya ce a'a ka barta kawai,ni yanzun zan ɗauki hanyar garinmu."