Sashe 22
Mummunan Zato Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wani lamari na Allah, A'isha sai ta samu sauƙi sosai, Uncle ya kai ta gurin Likita,ya duba ta ya kuma tabbatar musu ciki yana nan lafiya lau. Ya keɓe da Likitan ya tambaye shi ko zaya iya saduwa da ita babu matsala? Likitan ya ce babu wata matsala,don haka ranar suna dawowa daga asibitin misalin ƙarfe huɗu na yamma,nan ko ya sa ma ƙofa key, ya kuma shiga yi mata wasanni, duk da tana fargaban wuyar da ta sha, kuma tana tunanin ita zata ƙara sha,bai sa ta nuna fargaba ba. Sai gashi itama bata sha wuyar da tayi tunani ba,haka nan tun daga ranar itama ta shiga sahun matan gida, sannan yanzun ne ta san me ake yi wa kishin?.
Don haka ta ƙara yarda zata ƙyautata mishi,duk ranar da ita ce da shi ta kan shiga kitchen ta yi mishi girki da kanta,ga zoɓo mai sanyi, sannan duk lokacin da ya buƙace ta ba ta ɓata rai,ko jan aji tana ba shi dukkan goyon bayan da ya dace, shi yasa ta ƙara ɗaukaka cikin ranshi, ta kuma zarce duk matan nashi, har ya dinga Allah-Allah girkin ya zagayo kanta, haka nan duk abinda ta ce yanzun nan za'ayi shi,ko da ta yi mishi batun makaranta ta ce tuni an wuce ta a karatu, sai ya ce za ya samu (P.C) ɗinsu ya ga me zasu yi, koda ya samu (P.C) da batun cewa bata da lafiya ga jarabawa yana son su yi mishi taimako kullum za a ringa kawo ta ko kuma in suna da abu mai mahimmanci (P.C) ya yarda. duk da ba hakan ya taso ba,taji daɗin samun hakan,nan ko ta shiga zuwa makaranta.
Su ko su Jummai, sai suka shiga cewa don yaga tana da ciki shi yasa ƙarara ya ke nuna tafi kowa kuma ko gaban wane ne. Don haka kowacce ta tsaya ɗacin ran ba ya sonta, ta shiga fushi, tare da shiga faɗi tashin neman asiri. Hakan da suka yi na yin watsi da shi ya bashi damar more amarcin shi da A'isha, wanda bai yi a baya ba.
Duk ran girkin ta ya kan makara Ofis kuma ya dawo da wuri. In ya kalli madubi sai ya ce Beby kin sani na yi ƙyau fa,ko ba ki lura ba ne? Sai ta ce ai kai Uncle kullum mai ƙyau ne, komai naka yana da ƙyau. Ya ce har da ƴar Bebyna? Ta ce ai ni ba'a saka ni cikin jerin masu ƙyau, ya ce inji wa? Kina kallon madubi kuwa? Ai Beby har yau ni ban ga me ƙyanki ba, cikin haka suka soma jarabawa, dole ta zauna a ɗakinsu na cikin makaranta saboda suna karatu ita da su Samira,su Samira sun dame ta wai wane irin ciwo ne wannan da ya sakata yin shegen ƙyau haka? Ga wasu (hips) da ta yi,ƙirji kuma ya ƙara cika ta ce zaman gida ne kawai,ai ba za'a haɗa zaman gida da makaranta ba,sai dai cikin ranta ta saka duk ranar da suka yi banƙwana zata sanar da su cewa ita matar Uncle ce, haka suka ci gaba da jarabawa har suka gama. Ranar da aka yaye su,sun yi hotuna tare da canja lambobin waya,su da ƴan ajinsu, lokacin da za su rabu, Uncle ya zo tafiya da ita. Samira Suka ce in za ta yi aure ta faɗi musu,sai ta ce musu sai dai in zata haihu. Ta gaya musu cewa dama ta ɗauki alƙawarin yau zata sanar da su cewa Uncle mijinta ne. Dukkansu baki suka saki cike da mamaki. Ta ce musu yanzun haka ma ina ɗauke da ciki wata uku, zan sanar da ku in na haihu,ku kuma ina jiran bikinku don Allah da zarar ya zo in sani,nan suka yi banƙwana suna kewar juna.
Ta dawo gida suka ci gaba da zama da mijinta lafiya. Uncle na kula da ita sosai, sannan ba ta damuwa da lamarin su Hajiya Jummai, musamman da suka haɗe kai da Hadiza. Sun haɗa kansu, sai su zauna falo suna zuba mata habaici tare da su Suwaiba, musamman ranar da ya kasance ita ce da girki,nan fa za su yi ta surutunsu na cewa salon banza ana yi wa miji girki alhalin ga mai girki sai wannan ta ce ba dole ba ke ko abar wani ya yi ana son a zuba asirin mallaka duk da dai ba ta kula su kuma bata taɓa gaya mishi ba, cikin wannan halin ne wata ranar Litinin yana ɗakinta misalin ƙarfe ɗaya da rabi, haka kawai ya bar komai ya zo wai ya ganta da yaronshi, tana ƙwance kanta na kan cinyarshi, ya shafi cikin ta ya ce, Beby naga cikin ya ƙi ya yi girma ya fito ki dinga tafiya da ƙyar da ƙyar,na ƙosa in ga lokacin. Ta ce Uncle to cikin ƙwata-ƙwata watan shi uku fa, ya ɗaga rigarta mararta a shafe tamkar ba ta da komai, ya ce ni dai wannan cikin naki wane iri ne? Bai ƙara komai ba Beby? Kafin ta ba shi amsa sai ga Hajiya Jummai ta banko ƙofa babu ko sallama, ta ce ashe gaske ne,dama an ce kana zuwa kana cin amanar mu, tunda ai naga yau ba ita ce da kai ba, kuma yanzun ba lokacin dawowarka ba ne ka sato jiki ka dawo. Kallonta kawai yake yi sai da ta kai aya sannan ya dube ta ya ce,haba Jummai,me zai sa ki tsaya kina zubar da girmanki a gurin wannan ƴar yarinyar,ya kamata ace yanda take baki girmanki ki riƙe shi ni a zatona kece mace ta farko da za ki kula min da A'isha,da halin da take ciki,in na tuna yanda a baya ki ka fi ni son ki ga na samu ɗa, sai naga akasin haka, maimakon haka ma sai ki ka yi watsi dani da lamarina, kuma ki ka nuna tamkar kina faɗa da Ubangijinki, saboda ya bani ƙyauta, shawarar da zan baki,ki sake hali ki rabu da mugayen ƙawaye za su kai ki su baro. Ta soma kuka,ai ni yanzu komai ya zo bakin ka gaya min zakayi tunda mahaifata ba zata iya ɗaukar cikinka ba.
A'isha ta ce, to kiyi haƙuri Hajiya, Uncle ka koma Ofis shi kenan. Jummai ta daka mata tsawa ke makira, yi min shiru ba ke ce sanadin canza min halin miji ba,an je makaranta an roro ciki an zo an manna mishi, shi kuma da yake yana neman haihuwa ido rufe ya amsa jiki na ɓari,in da ka iya cikin me zai hana Hadiza kai mata in ni ba zan haihu ba.....ya katse ta da tsawa mai tsanani. Jummai kina hauka ne? Wace magana ki ke yi haka? Ya kama hannun A'isha wannan yarinyar ƙaramar yarinya ta fi min duka manyan matan da na aura, wannan yarinyar ita ce mace mai daraja ta farko a idanuna ni nan nine na yi mata ciki tunda kin tono bari in sanar da ke. A ranar da na kauda budurcinta a ranar cikina ya shiga jikinta, dan haka ki kama bakinki Jummai.
Ta fita tana masifar cewa eh dole ka ce kai,ni dai ban yafe satar min ƙwana da ake yi ba.
A'isha tana zaune ta zabga tagumi mamaki take yi wannan kuma wanne irin sharri ne? Hawaye suna zubowa daga idanunta,ya zo yana bata baki ta ce ka tafi Uncle ba komai. Ya ce, Beby ki zama mai haƙuri, ina nufin ki ƙara kan naki, ta share hawayenta tana murmushi ka koma Ofis Uncle, ya dinga bata haƙuri har sai da ta tabbatar mishi da cewa ita fa hayaniyar da suka yi ne wato sa'in'sar da suka yi ne yasa ta hawaye, nan ya fita yana shi mata albarka, A'isha ko ta maida ƙofa ta rufe.
Bayan sallar la'asar Wani bacci A'isha ta ringa ji,ta ƙi ƙwanciya saboda ta san cewa baccin la'asar ba shi da ƙyau,ko a musulunce, ta zauna tana kallo wai don kada baccin ya ɗauke ta. Da yake an ce gwanin sata ne baccin, sai ko ya sace ta har ma bata san lokacin da ta ƙwanta ba.
Can cikin baccin sai take jin numfashinta yana yin sama, ta soma kokowa da numfashinta, buɗe idanunta ke da wuya sai taga hayaƙi ta kowanne bangon ɗakin,nan ta shiga salati da ƙarfi tare da ihu, amma muryarta ba ta fita. Nan fa hayaƙin ya cika ɗaki, ya toshe mata numfashi.
Biyar dai-dai Uncle ya shigo gidan, ya nufi ɗakin Beby domin zuciyarshi ta kasa nutsuwa,yana shiga ya same ta kan gado tana ta mutsu-mutsu, numfashinta yana wuya ko sauka ƙirjinta ba ya yi, bakinta na ta motsi. Amma ba a jin me take cewa, sannan shi bai ga hayaƙin ba, ya ɗauke ta yana jijjiga ta,yana cewa Beby! Beby!! Ai ina ta daina ma motsin ta yi lagaf ƙasan zaninta kuma wata laima ya ji mai ɗumi,tana sauka a hannunshi, da sauri ya duba kun san me ya gani? Jini. Da ƙarfi ya furta jini?.
Tabbas jini ne, sai mun haÉ—u cikin kashi na uku don jin shin cikin da ake nema shekara da shekaru a ka sha wuya kanshi,ya zube? Asirin Hajiya Jummai zai tonu? Da sauran wasu abubuwan. Daga taku har kullum Halima K/Mashi.
Na gode
Don haka ta ƙara yarda zata ƙyautata mishi,duk ranar da ita ce da shi ta kan shiga kitchen ta yi mishi girki da kanta,ga zoɓo mai sanyi, sannan duk lokacin da ya buƙace ta ba ta ɓata rai,ko jan aji tana ba shi dukkan goyon bayan da ya dace, shi yasa ta ƙara ɗaukaka cikin ranshi, ta kuma zarce duk matan nashi, har ya dinga Allah-Allah girkin ya zagayo kanta, haka nan duk abinda ta ce yanzun nan za'ayi shi,ko da ta yi mishi batun makaranta ta ce tuni an wuce ta a karatu, sai ya ce za ya samu (P.C) ɗinsu ya ga me zasu yi, koda ya samu (P.C) da batun cewa bata da lafiya ga jarabawa yana son su yi mishi taimako kullum za a ringa kawo ta ko kuma in suna da abu mai mahimmanci (P.C) ya yarda. duk da ba hakan ya taso ba,taji daɗin samun hakan,nan ko ta shiga zuwa makaranta.
Su ko su Jummai, sai suka shiga cewa don yaga tana da ciki shi yasa ƙarara ya ke nuna tafi kowa kuma ko gaban wane ne. Don haka kowacce ta tsaya ɗacin ran ba ya sonta, ta shiga fushi, tare da shiga faɗi tashin neman asiri. Hakan da suka yi na yin watsi da shi ya bashi damar more amarcin shi da A'isha, wanda bai yi a baya ba.
Duk ran girkin ta ya kan makara Ofis kuma ya dawo da wuri. In ya kalli madubi sai ya ce Beby kin sani na yi ƙyau fa,ko ba ki lura ba ne? Sai ta ce ai kai Uncle kullum mai ƙyau ne, komai naka yana da ƙyau. Ya ce har da ƴar Bebyna? Ta ce ai ni ba'a saka ni cikin jerin masu ƙyau, ya ce inji wa? Kina kallon madubi kuwa? Ai Beby har yau ni ban ga me ƙyanki ba, cikin haka suka soma jarabawa, dole ta zauna a ɗakinsu na cikin makaranta saboda suna karatu ita da su Samira,su Samira sun dame ta wai wane irin ciwo ne wannan da ya sakata yin shegen ƙyau haka? Ga wasu (hips) da ta yi,ƙirji kuma ya ƙara cika ta ce zaman gida ne kawai,ai ba za'a haɗa zaman gida da makaranta ba,sai dai cikin ranta ta saka duk ranar da suka yi banƙwana zata sanar da su cewa ita matar Uncle ce, haka suka ci gaba da jarabawa har suka gama. Ranar da aka yaye su,sun yi hotuna tare da canja lambobin waya,su da ƴan ajinsu, lokacin da za su rabu, Uncle ya zo tafiya da ita. Samira Suka ce in za ta yi aure ta faɗi musu,sai ta ce musu sai dai in zata haihu. Ta gaya musu cewa dama ta ɗauki alƙawarin yau zata sanar da su cewa Uncle mijinta ne. Dukkansu baki suka saki cike da mamaki. Ta ce musu yanzun haka ma ina ɗauke da ciki wata uku, zan sanar da ku in na haihu,ku kuma ina jiran bikinku don Allah da zarar ya zo in sani,nan suka yi banƙwana suna kewar juna.
Ta dawo gida suka ci gaba da zama da mijinta lafiya. Uncle na kula da ita sosai, sannan ba ta damuwa da lamarin su Hajiya Jummai, musamman da suka haɗe kai da Hadiza. Sun haɗa kansu, sai su zauna falo suna zuba mata habaici tare da su Suwaiba, musamman ranar da ya kasance ita ce da girki,nan fa za su yi ta surutunsu na cewa salon banza ana yi wa miji girki alhalin ga mai girki sai wannan ta ce ba dole ba ke ko abar wani ya yi ana son a zuba asirin mallaka duk da dai ba ta kula su kuma bata taɓa gaya mishi ba, cikin wannan halin ne wata ranar Litinin yana ɗakinta misalin ƙarfe ɗaya da rabi, haka kawai ya bar komai ya zo wai ya ganta da yaronshi, tana ƙwance kanta na kan cinyarshi, ya shafi cikin ta ya ce, Beby naga cikin ya ƙi ya yi girma ya fito ki dinga tafiya da ƙyar da ƙyar,na ƙosa in ga lokacin. Ta ce Uncle to cikin ƙwata-ƙwata watan shi uku fa, ya ɗaga rigarta mararta a shafe tamkar ba ta da komai, ya ce ni dai wannan cikin naki wane iri ne? Bai ƙara komai ba Beby? Kafin ta ba shi amsa sai ga Hajiya Jummai ta banko ƙofa babu ko sallama, ta ce ashe gaske ne,dama an ce kana zuwa kana cin amanar mu, tunda ai naga yau ba ita ce da kai ba, kuma yanzun ba lokacin dawowarka ba ne ka sato jiki ka dawo. Kallonta kawai yake yi sai da ta kai aya sannan ya dube ta ya ce,haba Jummai,me zai sa ki tsaya kina zubar da girmanki a gurin wannan ƴar yarinyar,ya kamata ace yanda take baki girmanki ki riƙe shi ni a zatona kece mace ta farko da za ki kula min da A'isha,da halin da take ciki,in na tuna yanda a baya ki ka fi ni son ki ga na samu ɗa, sai naga akasin haka, maimakon haka ma sai ki ka yi watsi dani da lamarina, kuma ki ka nuna tamkar kina faɗa da Ubangijinki, saboda ya bani ƙyauta, shawarar da zan baki,ki sake hali ki rabu da mugayen ƙawaye za su kai ki su baro. Ta soma kuka,ai ni yanzu komai ya zo bakin ka gaya min zakayi tunda mahaifata ba zata iya ɗaukar cikinka ba.
A'isha ta ce, to kiyi haƙuri Hajiya, Uncle ka koma Ofis shi kenan. Jummai ta daka mata tsawa ke makira, yi min shiru ba ke ce sanadin canza min halin miji ba,an je makaranta an roro ciki an zo an manna mishi, shi kuma da yake yana neman haihuwa ido rufe ya amsa jiki na ɓari,in da ka iya cikin me zai hana Hadiza kai mata in ni ba zan haihu ba.....ya katse ta da tsawa mai tsanani. Jummai kina hauka ne? Wace magana ki ke yi haka? Ya kama hannun A'isha wannan yarinyar ƙaramar yarinya ta fi min duka manyan matan da na aura, wannan yarinyar ita ce mace mai daraja ta farko a idanuna ni nan nine na yi mata ciki tunda kin tono bari in sanar da ke. A ranar da na kauda budurcinta a ranar cikina ya shiga jikinta, dan haka ki kama bakinki Jummai.
Ta fita tana masifar cewa eh dole ka ce kai,ni dai ban yafe satar min ƙwana da ake yi ba.
A'isha tana zaune ta zabga tagumi mamaki take yi wannan kuma wanne irin sharri ne? Hawaye suna zubowa daga idanunta,ya zo yana bata baki ta ce ka tafi Uncle ba komai. Ya ce, Beby ki zama mai haƙuri, ina nufin ki ƙara kan naki, ta share hawayenta tana murmushi ka koma Ofis Uncle, ya dinga bata haƙuri har sai da ta tabbatar mishi da cewa ita fa hayaniyar da suka yi ne wato sa'in'sar da suka yi ne yasa ta hawaye, nan ya fita yana shi mata albarka, A'isha ko ta maida ƙofa ta rufe.
Bayan sallar la'asar Wani bacci A'isha ta ringa ji,ta ƙi ƙwanciya saboda ta san cewa baccin la'asar ba shi da ƙyau,ko a musulunce, ta zauna tana kallo wai don kada baccin ya ɗauke ta. Da yake an ce gwanin sata ne baccin, sai ko ya sace ta har ma bata san lokacin da ta ƙwanta ba.
Can cikin baccin sai take jin numfashinta yana yin sama, ta soma kokowa da numfashinta, buɗe idanunta ke da wuya sai taga hayaƙi ta kowanne bangon ɗakin,nan ta shiga salati da ƙarfi tare da ihu, amma muryarta ba ta fita. Nan fa hayaƙin ya cika ɗaki, ya toshe mata numfashi.
Biyar dai-dai Uncle ya shigo gidan, ya nufi ɗakin Beby domin zuciyarshi ta kasa nutsuwa,yana shiga ya same ta kan gado tana ta mutsu-mutsu, numfashinta yana wuya ko sauka ƙirjinta ba ya yi, bakinta na ta motsi. Amma ba a jin me take cewa, sannan shi bai ga hayaƙin ba, ya ɗauke ta yana jijjiga ta,yana cewa Beby! Beby!! Ai ina ta daina ma motsin ta yi lagaf ƙasan zaninta kuma wata laima ya ji mai ɗumi,tana sauka a hannunshi, da sauri ya duba kun san me ya gani? Jini. Da ƙarfi ya furta jini?.
Tabbas jini ne, sai mun haÉ—u cikin kashi na uku don jin shin cikin da ake nema shekara da shekaru a ka sha wuya kanshi,ya zube? Asirin Hajiya Jummai zai tonu? Da sauran wasu abubuwan. Daga taku har kullum Halima K/Mashi.
Na gode