Sashe 5
Mugunta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Dan Allah mama" Mariya ta fada tana daka tsalle kafin ta shige ɗakin da gudu.
Dariya delu ta yi sannan ta juya ta kalli malam surajo, "Kai kuma ka wani zauna kana kallo na , dallah ka tashi ka bani wuri ka wuce kayi bacci."
Sumsum malam surajo ya tashi ya shige dakin ya kwanta kamar wani wanda ake controlling, delu shewa tayi kafin ta ce "lallai malam na kan tudu ba wasa ba." sannan kuma ta ƙara sheqewa da wata dariyar.
Mariya ce ta fito cikin shaddar ta blue da mayafi red hade da takalmi da jaka duk red, ga shi ta ci Wata uwar kwalliya da acuci.
"Kai, Ma sha Allah, wannan kyau haka maririn baba, kinyi chass abinki." Mariya cike da jin dadi ta kalli uwar ta ta kafin tai ma ta sallama ta fita.
Tana fita kofar gida ta tarar da alhaji gabatari jingine gaban motar sa kirar golf irin ta kayan miyan nan.
Wata farar shadda ce a jikin shi, sai gilas da ya ƙwama a fuskar shi.
Cike da zumudi Mariya ta karasa kusa da shi, Dan ba'a taba kiran Mariya ba wai ana sallama da ita ba.
Alhaji gabatari ne ya bude bakinsa wanda in ban da warin sigari ba abinda yake, yace "Barka da fitowa gimbiya sarautar mata, fatan kina lapiya."
Wani farrr Mariya ta yi da Ido, kafin ta bude dashashun hakoran ta tace "yawwa alhaji , Ina lapiya ya kasuwa."
"Lapiya kalau mariri." alhaji gabatari ya kuma fade.
A haka suka cigaba da hirar su har dare ya tsala suka yi sallama.
Mariya na shiga gida ta ga delu ta dade da bacci, ita ma ta shige dakinta ta kwanta ba tare da ta damu ta sauya kaya ba.
Asuba ta gari!!!
*AYAMAN*
MAFARKI
Wata mata ta hango, zaune akan wata kujerar karfe wacce duk ta yi tsatsa ta lalace, kallon qurilla matar ta ke yi wa Ayaman wanda ya sa tai maza ta tashi ta fara gudu.
Tana cikin gudun ta fara hango wani haske mai matukar kyau, ta nufi hanyar da zai kaita wurin hasken ne wannan matar ta riqo kafarta da wata kaca ta qarfe, ihu ta fara yi tana neman taimako.
Yayin da wannan matar ke dada janyota, kusa da ita , tazo gab ta ita ne ta farka daga mafarkin.
"Hasbunallahu wani'imal wakeel." Ayaman ta fada tana tashi a firgice, kanta ne taji ya sara mata.
"innalillahi wa'inna i'laihi raji'un." ta faɗa cikin tashin hankali, addu'ar da taxo bakin ta kawai take yi kafin ta ji ciwon kan ya ragu.
Kiran sallar asuba da taji ana yi ne yasa ta tashi ta fita tsakar gidan nasu, hasken farin wata, da Kuma niimatacciyar iskar asuba ne yasa ta lumshe Ido.
Ta Dade a tsaye a wurin kafin ta shiga bandakin da ko arzikin fitila bai samu ba, tsarki tayi kafin tayi alwala ta fito.
Dakin ta koma tana tuna mafarkin da tayi.
Raka'atanul fajir ta fara yi kafin taji iqama a masallacin unguwar tasu sannan ta tada sallah.
Bayan ta idar da sallah ta yi azkhar sannan ta fito tsakar gidan, randa ta duba Taga da ruwa a ciki .
Kwanika ta debo ta fara wanke wa, tana yi tana mitar kazantar Ladiyo dan wasu kwanikan har sun bushe ba'a wanke ba.
Shara tayi bayan ta kammala wanke-wanken, sai da ta sha re gidan tsaf sannan ta zauna ta huta dan a lokacin takwas ta kusa .
Bokiti ta dauko zata debi ruwa, Taga ruwan ya qare, "ya salaam." ta fada tana dafe kanta da hannu. Harga Allah bata son debo ruwa Dan wannan ranar safiyar da zafinta.
Ba yadda ta iya, haka ta dauki bokitin ta fita debo ruwa.
Kamar kullum gurin borehole din nasu a cike yake da mutane manya da kanana ana ta diban ruwa.
"Wallahi na riga ki baki Isa ba" wata yarinya wacce bata wuce shekara 10 ba ta fada tana ture wata budurwa wacce ta Kai kusan shekara 15.
"Ni sa'ar ki ce Amina? Iyi ." wannan budurwar ta fada tana hararar yarinyar.
"Ehh din ay ke kika zubar da girman ki shiyasa muka bi muka ta ke shi." yarinyar ta fada tana murguda baki irin na marasa kunya.
Nan fa fada ya kaure tsakanin yarinya da budurwa. Ayaman ta tsaya tana kallon I kon Allah taji an fincike bokitin hannun ta.
"Anas?"
"Ayaman."
Kallon shi take kafin ta gaishe shi , amsawa anas ya yi kafin ya amshi bokitin yace taho muje, "Ina zamu kuma? "
Binshi tai suka tafi, Mai ruwa ta samo mata ya kai shi har gida, amsar ruwan ta yi ta rinqa cika ko Ina na gidan har sai da ya cika taf.
Fitowa ta yi Taga anas har ya sallami mai ruwan, " nagode sosai ." Ayaman ta fada da wani murmushi a fuskarta.
"Bakomi, yiwa kaine" Anas ya fada yana mayar ma ta da martanin murmushin.
"Bari na shiga gida sai anjima"
"Dan tsaya Ayaman." tsayawa ta yi kafin ta cigaba da cewa "ya maganar mu ta waccan ranar"?
Rufe fuska ta yi ta shige gida da gudu, yayin da anas yayi tafiyar da Yana dariya.
Tana shiga gidan ta bige inna ladiyo wacce ke wanke fuskar ta, Dan da alama daga bacci ta tashi.
" Kam bala'i!! , tass !! inna ladiyo ta wanke fuskar Ayaman da Mari, " ba Kya Gani ne da Zaki buge ni?"
"Kiyi hakuri inna" Ayaman ta fada tana ƙasa da kai .
Tsaki ladiyo ta yi sannan ta wuce ta shige dakinta, sum sum AYAMAN ta wuce ta shiga dakin ta ta zauna akan zanin dake shimfide a kasa...
More comment more typing ✍️✍️
Love you all 😘 ❤️
Khairat 🖤🖤🖊️ 🖊️ 🖊
️https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈
By
Khairat 🖤🖊️✍️
This page is dedicated to aunty Reemah ❤️
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 15-16
Tsaki Ladiyo ta yi sannan ta wuce ta shige dakinta, sum sum Ayaman ta shige na ta dakin, zama ta yi a kan shimfidar zanin dake shimfide a kasan dakin.
Tunanin Anas ne ya fado ma ta a rai, wani lallausan murmushi ta saki tana qara jin soyayyar Anas a ranta, wadda bata ta'ba sanar Mai ba.
Tun mahaifiyar ta na da rai Anas ke hidima da ita,yana nuna ma ta ƙauna da so wanda bata fahimta ba a wannan lokacin, a gaskiya in ta yi rashin Anas ta yi babban rashi, Amma taya Ladiyo zata bari ya aure ta.
Tana yawan mamakin irin qeta ta ladiyo, qiri-qiri ladiyo ke dakile maganar auren ta da zarar ta taso, kusan Maza uku ne suka zo neman auren ta, ladiyo ke zuga malam isyaku ya hana auren.
Haka bayan rasuwar mahaifiyar ta, dangin ta su adda asiyah ƙanwar innar ta, tana iya tuna me ya faru sosai a ranar.
"Nifa babu inda za'a kai min 'ya, haka kawai, ku barmin ɗjya ta Ina da matar da zata kula da ita." malam isyaku ya karasa fada yana kallon su addah Asiyah ɗaiɗai.
"Haba malam isyaku, ay abun bai kai haka ba, naga Ayaman duk diyar mu ce, tunda ay 'ya'yan Zainab (mahaifiyar Ayaman) duk 'ya'yan mu ne koh koh?"
Adda suwaiba, babbar yayar inna ta , ta numfasa sannan tace "batun matar ka ay ba wanda bai san halin ladiyo ba, auren ta na farko, ta kori kishiyar ta, ta gallaza ma mijin nata daga karshe ya mutu wanda mutane ke zargin ita ta kashe shi, gashi wani irin uƙuba ne bata bawa Zainab ba duk da cewa ita ta ma ta sanadiyyar shigowa cikin gidan?"
"Wallahi ƙarya ce,munafikan banza da hofi kawai, wannan wace irin jaraba ce , habaa." Ladiyo da ta fito daga dakinta tana riqe da zani a hannu ta fada tana tura daurin dankwali gaban goshi.
Ta cigaba da fadin "Kuma yarinya tana nan, ko yanka naman ta zamu yi mu ci dole ku bar ta a nan." ta tsaya a kan tabarma da su addah asiyah da addah suwaiba da sauran yan uwan mahaifiya ta ke zaune.
"Kehh Ladiyo ki shiga tai tayin ki wallahi, Dan ruwa ba sa'an kwando bane, yawwa."Addah Asiyah ta fada tana miqewa daga zaman da take.
Yatsina fuska ladiyo ta yi sannan tace"wannan Kuma matsalar ku.", ta cigaba da baƙaƙen maganganun ta.
Addah asiyah ce ta tashi cikin fushi ta sabi jakar ta da takalmi zata fice addah suwaiba ta dakatar da ita.
"Wlh Yaya ki barni na tafi kar ayi abin kunya." addah Asiyah ta karasa fada cikin wata irin murya ta fushi.
"Munga Zaki ma karshen fushi, yarinya ce dai ba za'a bada ba tana nan gidan ubanta." ladiyo ta fada cikin izgili.
Shiru addah Asiyah ta yi ta tsaya suna bama malam isyaku baki amma biriss yaqi karshe ma ficewa ya yi daga gidan bisa umarnin ladiyo.
Tashi suka yi da niyyar tafiya gida dan ba gari daya suke da garin su ladiyo ba.
Tashin su ke da wuya ladiyo ta sheqe da wata munafukar dariya, tace "Allah ya raka taki gona." tana wani watsa yatsu a iska kamar ana kora awaki.
Addah Asiyah ce ta juyo ta mata magana wadda ta sa ladiyo hankada asiyah kusa da bakin rijiya.
"Dama haka nake so." ladiyo ta fada a zuciyar ta.
Addah Asiyah kuwa ta bige da bakin rijiyar, addah sadiyah karamar kanwar inna ta ce ta Kai ma ladiyo duka ta kufce.
Kafin kace me gidan malam isyaku ya kacame da fada, ta ko'ina, Dan ladiyo dama Masha Allah, akwai jibgegen jiki, ga addah asiyah ma mai karfin hali.
Kaf cikin ƴan uwan mahaifiyar tawa addah suwaiba ce kawai ke gefe riqe da kanta da aka buga ma karfe.
Ni kam da ban wuce shekara 10 ba na tsaya tsuru-tsuru Ina kallon wannan tashin hankali.
Dariya delu ta yi sannan ta juya ta kalli malam surajo, "Kai kuma ka wani zauna kana kallo na , dallah ka tashi ka bani wuri ka wuce kayi bacci."
Sumsum malam surajo ya tashi ya shige dakin ya kwanta kamar wani wanda ake controlling, delu shewa tayi kafin ta ce "lallai malam na kan tudu ba wasa ba." sannan kuma ta ƙara sheqewa da wata dariyar.
Mariya ce ta fito cikin shaddar ta blue da mayafi red hade da takalmi da jaka duk red, ga shi ta ci Wata uwar kwalliya da acuci.
"Kai, Ma sha Allah, wannan kyau haka maririn baba, kinyi chass abinki." Mariya cike da jin dadi ta kalli uwar ta ta kafin tai ma ta sallama ta fita.
Tana fita kofar gida ta tarar da alhaji gabatari jingine gaban motar sa kirar golf irin ta kayan miyan nan.
Wata farar shadda ce a jikin shi, sai gilas da ya ƙwama a fuskar shi.
Cike da zumudi Mariya ta karasa kusa da shi, Dan ba'a taba kiran Mariya ba wai ana sallama da ita ba.
Alhaji gabatari ne ya bude bakinsa wanda in ban da warin sigari ba abinda yake, yace "Barka da fitowa gimbiya sarautar mata, fatan kina lapiya."
Wani farrr Mariya ta yi da Ido, kafin ta bude dashashun hakoran ta tace "yawwa alhaji , Ina lapiya ya kasuwa."
"Lapiya kalau mariri." alhaji gabatari ya kuma fade.
A haka suka cigaba da hirar su har dare ya tsala suka yi sallama.
Mariya na shiga gida ta ga delu ta dade da bacci, ita ma ta shige dakinta ta kwanta ba tare da ta damu ta sauya kaya ba.
Asuba ta gari!!!
*AYAMAN*
MAFARKI
Wata mata ta hango, zaune akan wata kujerar karfe wacce duk ta yi tsatsa ta lalace, kallon qurilla matar ta ke yi wa Ayaman wanda ya sa tai maza ta tashi ta fara gudu.
Tana cikin gudun ta fara hango wani haske mai matukar kyau, ta nufi hanyar da zai kaita wurin hasken ne wannan matar ta riqo kafarta da wata kaca ta qarfe, ihu ta fara yi tana neman taimako.
Yayin da wannan matar ke dada janyota, kusa da ita , tazo gab ta ita ne ta farka daga mafarkin.
"Hasbunallahu wani'imal wakeel." Ayaman ta fada tana tashi a firgice, kanta ne taji ya sara mata.
"innalillahi wa'inna i'laihi raji'un." ta faɗa cikin tashin hankali, addu'ar da taxo bakin ta kawai take yi kafin ta ji ciwon kan ya ragu.
Kiran sallar asuba da taji ana yi ne yasa ta tashi ta fita tsakar gidan nasu, hasken farin wata, da Kuma niimatacciyar iskar asuba ne yasa ta lumshe Ido.
Ta Dade a tsaye a wurin kafin ta shiga bandakin da ko arzikin fitila bai samu ba, tsarki tayi kafin tayi alwala ta fito.
Dakin ta koma tana tuna mafarkin da tayi.
Raka'atanul fajir ta fara yi kafin taji iqama a masallacin unguwar tasu sannan ta tada sallah.
Bayan ta idar da sallah ta yi azkhar sannan ta fito tsakar gidan, randa ta duba Taga da ruwa a ciki .
Kwanika ta debo ta fara wanke wa, tana yi tana mitar kazantar Ladiyo dan wasu kwanikan har sun bushe ba'a wanke ba.
Shara tayi bayan ta kammala wanke-wanken, sai da ta sha re gidan tsaf sannan ta zauna ta huta dan a lokacin takwas ta kusa .
Bokiti ta dauko zata debi ruwa, Taga ruwan ya qare, "ya salaam." ta fada tana dafe kanta da hannu. Harga Allah bata son debo ruwa Dan wannan ranar safiyar da zafinta.
Ba yadda ta iya, haka ta dauki bokitin ta fita debo ruwa.
Kamar kullum gurin borehole din nasu a cike yake da mutane manya da kanana ana ta diban ruwa.
"Wallahi na riga ki baki Isa ba" wata yarinya wacce bata wuce shekara 10 ba ta fada tana ture wata budurwa wacce ta Kai kusan shekara 15.
"Ni sa'ar ki ce Amina? Iyi ." wannan budurwar ta fada tana hararar yarinyar.
"Ehh din ay ke kika zubar da girman ki shiyasa muka bi muka ta ke shi." yarinyar ta fada tana murguda baki irin na marasa kunya.
Nan fa fada ya kaure tsakanin yarinya da budurwa. Ayaman ta tsaya tana kallon I kon Allah taji an fincike bokitin hannun ta.
"Anas?"
"Ayaman."
Kallon shi take kafin ta gaishe shi , amsawa anas ya yi kafin ya amshi bokitin yace taho muje, "Ina zamu kuma? "
Binshi tai suka tafi, Mai ruwa ta samo mata ya kai shi har gida, amsar ruwan ta yi ta rinqa cika ko Ina na gidan har sai da ya cika taf.
Fitowa ta yi Taga anas har ya sallami mai ruwan, " nagode sosai ." Ayaman ta fada da wani murmushi a fuskarta.
"Bakomi, yiwa kaine" Anas ya fada yana mayar ma ta da martanin murmushin.
"Bari na shiga gida sai anjima"
"Dan tsaya Ayaman." tsayawa ta yi kafin ta cigaba da cewa "ya maganar mu ta waccan ranar"?
Rufe fuska ta yi ta shige gida da gudu, yayin da anas yayi tafiyar da Yana dariya.
Tana shiga gidan ta bige inna ladiyo wacce ke wanke fuskar ta, Dan da alama daga bacci ta tashi.
" Kam bala'i!! , tass !! inna ladiyo ta wanke fuskar Ayaman da Mari, " ba Kya Gani ne da Zaki buge ni?"
"Kiyi hakuri inna" Ayaman ta fada tana ƙasa da kai .
Tsaki ladiyo ta yi sannan ta wuce ta shige dakinta, sum sum AYAMAN ta wuce ta shiga dakin ta ta zauna akan zanin dake shimfide a kasa...
More comment more typing ✍️✍️
Love you all 😘 ❤️
Khairat 🖤🖤🖊️ 🖊️ 🖊
️https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈
By
Khairat 🖤🖊️✍️
This page is dedicated to aunty Reemah ❤️
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 15-16
Tsaki Ladiyo ta yi sannan ta wuce ta shige dakinta, sum sum Ayaman ta shige na ta dakin, zama ta yi a kan shimfidar zanin dake shimfide a kasan dakin.
Tunanin Anas ne ya fado ma ta a rai, wani lallausan murmushi ta saki tana qara jin soyayyar Anas a ranta, wadda bata ta'ba sanar Mai ba.
Tun mahaifiyar ta na da rai Anas ke hidima da ita,yana nuna ma ta ƙauna da so wanda bata fahimta ba a wannan lokacin, a gaskiya in ta yi rashin Anas ta yi babban rashi, Amma taya Ladiyo zata bari ya aure ta.
Tana yawan mamakin irin qeta ta ladiyo, qiri-qiri ladiyo ke dakile maganar auren ta da zarar ta taso, kusan Maza uku ne suka zo neman auren ta, ladiyo ke zuga malam isyaku ya hana auren.
Haka bayan rasuwar mahaifiyar ta, dangin ta su adda asiyah ƙanwar innar ta, tana iya tuna me ya faru sosai a ranar.
"Nifa babu inda za'a kai min 'ya, haka kawai, ku barmin ɗjya ta Ina da matar da zata kula da ita." malam isyaku ya karasa fada yana kallon su addah Asiyah ɗaiɗai.
"Haba malam isyaku, ay abun bai kai haka ba, naga Ayaman duk diyar mu ce, tunda ay 'ya'yan Zainab (mahaifiyar Ayaman) duk 'ya'yan mu ne koh koh?"
Adda suwaiba, babbar yayar inna ta , ta numfasa sannan tace "batun matar ka ay ba wanda bai san halin ladiyo ba, auren ta na farko, ta kori kishiyar ta, ta gallaza ma mijin nata daga karshe ya mutu wanda mutane ke zargin ita ta kashe shi, gashi wani irin uƙuba ne bata bawa Zainab ba duk da cewa ita ta ma ta sanadiyyar shigowa cikin gidan?"
"Wallahi ƙarya ce,munafikan banza da hofi kawai, wannan wace irin jaraba ce , habaa." Ladiyo da ta fito daga dakinta tana riqe da zani a hannu ta fada tana tura daurin dankwali gaban goshi.
Ta cigaba da fadin "Kuma yarinya tana nan, ko yanka naman ta zamu yi mu ci dole ku bar ta a nan." ta tsaya a kan tabarma da su addah asiyah da addah suwaiba da sauran yan uwan mahaifiya ta ke zaune.
"Kehh Ladiyo ki shiga tai tayin ki wallahi, Dan ruwa ba sa'an kwando bane, yawwa."Addah Asiyah ta fada tana miqewa daga zaman da take.
Yatsina fuska ladiyo ta yi sannan tace"wannan Kuma matsalar ku.", ta cigaba da baƙaƙen maganganun ta.
Addah asiyah ce ta tashi cikin fushi ta sabi jakar ta da takalmi zata fice addah suwaiba ta dakatar da ita.
"Wlh Yaya ki barni na tafi kar ayi abin kunya." addah Asiyah ta karasa fada cikin wata irin murya ta fushi.
"Munga Zaki ma karshen fushi, yarinya ce dai ba za'a bada ba tana nan gidan ubanta." ladiyo ta fada cikin izgili.
Shiru addah Asiyah ta yi ta tsaya suna bama malam isyaku baki amma biriss yaqi karshe ma ficewa ya yi daga gidan bisa umarnin ladiyo.
Tashi suka yi da niyyar tafiya gida dan ba gari daya suke da garin su ladiyo ba.
Tashin su ke da wuya ladiyo ta sheqe da wata munafukar dariya, tace "Allah ya raka taki gona." tana wani watsa yatsu a iska kamar ana kora awaki.
Addah Asiyah ce ta juyo ta mata magana wadda ta sa ladiyo hankada asiyah kusa da bakin rijiya.
"Dama haka nake so." ladiyo ta fada a zuciyar ta.
Addah Asiyah kuwa ta bige da bakin rijiyar, addah sadiyah karamar kanwar inna ta ce ta Kai ma ladiyo duka ta kufce.
Kafin kace me gidan malam isyaku ya kacame da fada, ta ko'ina, Dan ladiyo dama Masha Allah, akwai jibgegen jiki, ga addah asiyah ma mai karfin hali.
Kaf cikin ƴan uwan mahaifiyar tawa addah suwaiba ce kawai ke gefe riqe da kanta da aka buga ma karfe.
Ni kam da ban wuce shekara 10 ba na tsaya tsuru-tsuru Ina kallon wannan tashin hankali.