Sashe 11
Mugunta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan ya gama ƴan tsubbace tsubaccen sa ya juyo ya kalli su Ladiyo, kamar wanda suke bautamai haka suka fara russunar da kai hade da kirari a garesa.
Maganganu suka yi na lokaci mai tsawo sannan ya dauko wata ƙaramar baƙar laya a cikin ƙoƙon jakin da ke wurin ya miƙa wa Ladiyo yana faɗin "Wannan shi ne ƙarshen matsalar ki, ki yi aiki da shi zaki bani labari."
Ya juya wurin Delu yace, "Duk abinda kike aikatawa ina ganin ki ta ƙwaryata, abinda zance shi ne ki bi a hankali ." Daga nan ya ja bakinsa ya yi shiru.
Sumsum suka fice daga kogon bayan biyansa da suka yi da mutuncinsu.
********************************
*Ayaman*
Baccinta take cikin kwanciyar hankali kawai taji alamar ana tashin ta daga bacci, a ɗan razane ta ja bargon ta rufe kanta tana karanto ayoyin Alkur'ani.
Kuma jin ana jan zanin da ta rufa da shi ta ji ana yi, da sauri ta ja ta kuma tofa addu'a kusa da ita.
Again aka kuma jan zanin, ta yi ta maza ta miƙe zaune, wayam babu kowa a ɗakin, chan ta hango wani abu kamar mutum a tsaye ya tunkaro ta.
Duk addu'ar da ta zo bakinta take yi har wannan abin ya cimma ta....
Love you all 💞 💙
More comment more typing ✍️
https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8
😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈
By
Khairat 💞💙
Page 29-30
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️*
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Lokaci na ta shuɗewa, abubuwa na ƙara haɓaka, ta ɓangaren Ayaman ma haka.
Lamura sai ƙara gaba suke dan yanzu Ladiyo ta yi yadda ta yi aka sa ranar aurenta da Anas, har yanzu bata gama mamakin Ladiyo ba har sai da ta ga saura watanni uku bikinta da Anas.
Tashi ta yi daga kan zanin da take sallah, tsayawa ta yi ta na kallon tsakar gidan, gari ya waye tangararan, rana ta fara fitowa alamar za'a yi rana mai zafi.
Ruwa ta ɗebo a randa ta shiga banɗaki, bayan ta fito ta fara aikin gidan, ta gama ta yi wanka tasa kaya.
Abin kari Ladiyo ta miƙo ma ta dan ba laifi ta ga sauyi sosai daga wurin Ladiyo wanda bata gama yadda da shi ba.
Ta kammala cin abincin ta fice zuwa gidan su tsahare dan bikin saura kwanaki uku.
Ta na shiga gidan ta tarar da tsahare ana shafa ma ta kurkur dan shi ne abinda yawancin ƴan garin ke amfani da domin gyaran amarya.
Bayan ta gaisa da Innar su tsaharen da wasu daga cikin ƴan uwansu tsahare, ta zauna aka fara fira tana taya su ayyuka har aka kammala gyaran jikin.
Wuraren ɗaya na rana suka fita rabon katin biki , sun zagaya gidaje da yawa na ƴan uwa da abokan arziki sun raba kati.
Sai ana kiran magriba suka shiga gidansu tsahare a gajiye.
Innar su da sauran ƴan uwa da suka fara zuwa na ɗaki su na gabatar da sallar magriba.
Bayan sun idar da sallah suka ci abinci sannan Ayaman ta yi ma ta sallama da niyyar gobe da wuri zata fito domin za'a yi sa lalle.
*******************************
*Farouk*
Ta ɓangaren Farouk da Ummu Kulsum abu sai ƙara tabarbarewa yake, dan yanzu an sa ranar auren Farouk da Nafee.
Ummu Kulsum ta yi kukan har ta gaji, har ga Allah ta gaji da rayuwar gidan Farouk, ga Amminsa ma kamar shi ta daina bata kulawa kamar da.
Dan akwai ranar da ta je gaishe ta, ta amsa ma ta ciki ciki kuma ta tashi ta bar falon.
A ganin Ummu Kulsum ba laifi ne ba dan ta shiga ɗakin Ammi dan ta saba da hakan, mafi yawancin lokuta Ammin da kanta take jan ta ɗaki tai ta bata haƙuri saboda ta san zaman da suke ita da Farouk .
Amma a wannan lokacin tana shiga ɗakin,Ammi ta hau ta da faɗa da masifa, "Banda tsabar munafirci, meye kuma na shigo min ɗaki? Tsaya kiji bazan dauki wannan abin ba dan haka fitar min a ɗaki!." Ammi ta ƙarasa cikin faɗa.
Cikin tsoro Ummu Kulsum tace "Kiyi haƙuri Ammi, na zata ba laifi ne dan na shigo ɗakin ki ba."
"Tunda na uwarki ne ay dole baza ki ɗauka laifi ne ba, fita kafin ki ƙarasa ɓata min rai."
Ammi ta faɗa tana rufe idanu irin na wanda ke masifa.
Sumsum Ummu Kulsum ta fita daga ɗaki tana mamakin me ya samu Ammi.
Ta ɓangaren Ammi kuwa, hakanan taji ta tsani ganin Ummu Kulsum a kusa da ita, babu dalili ko ɗaya.
Ummu Kulsum ta zauna a falon cike da zullumi, dan dama ta zo ne domin gayama Ammi halin da take ciki sai gashi ta tarar da Ammi a wani yanayi da bata taɓa ganin ta ba.
********************************
*Nafee*
Yanzu kam Nafee ranta fess an sa ranar aurenta da Farouk sai bankar magungunan mata take ita ala dole sai ta koma budurwa, ga Lubna dake gefe tana ƙara zuga ta.
Su na zaune a falon Nafee, Lubna na kallon wayarta sai ƙawar Lubna Zainab tana cin kayan marmari, ita luma Nafee ta na jujjuya wani abu a hannunta.
"Lubna anya kuwa?" Nafee ta faɗa cikin rashin yadda da tantama tana juya maganin a hannu.
"Nafee, kina tantama ne? Tsaya kiji wannan maganin sai da na tsallake rijiyoyi biyar kafin na amso miki su."
Lubna ta numfasa sannan ta cigaba da faɗin, "Wannan ɗan ƙaramin, hmm." Ta faɗa ta a ɗaga sa sama.
"Cika aiki kenan, in dai kika yi amfani da shi, hmmm wai inji mai ciwon haƙori ba'a magana kawai." Lubna ta ƙarasa faɗa tana yin alamar rufe baki kamar zip.
Haka suka cigaba da hirarsu,su na ta shewa kamar an yi musu hajji da Umrah.
********************************
*Ladiyo*
Abubuwa su na tafiyar ma ta yadda take so, dan yanzu ta sa malam Isyaku a gaba har sai da aka sa ranar auren Ayaman.
Matsalarta, Nabila sai Yunusa amma wannan bai dame ta ba kamar Ayaman, ta tsani ganinta cikin farin ciki ko walwala.
Ita da Delu ne suke kiɗansu suke rawarsu..
Love you all 💞 💙
More comment more typing ✍️
Khairat ✍️🤍https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈
By
Khairat 💞
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 31-32
Ita da delu ke kiɗansu su na rawarsu...
Dan ayanzu haka, alhaji Gabatari ya nemi auren Mariya kuma Delu ta yi uwa ta yi makarɓiya sai da aka yadda da shi.
Rayuwa ta yi ma ta sumul, bata da wata damuwa, dan yanzu ma Alhaji Gabatari ya aiko masu aikin gini zasu rushe gidan ayi musu sabo dal.
Ta ɓangaren Malam Surajo kam ba'a magana, dan yanzu duk ya susuce duk wanda ya sanshi a baya ya ganshi yanzu sai ya kasa gane shi.
Har ranar auren Mariya da aka sa bai da masaniya a matsayin sa na mahaifinta, sai lemu da Delu ta bashi tace an saka rana.
Yanzu ma masu aiki ne ke ta fama da aiki, dan an ruguje gidan tass , Delu ta shigo gidan da yake a gidan wasu ƴan uwanta suke zaune kafin a kammala aikin.
Washe baki ta yi tace "Sannun ku da ƙoƙari , kuna ta fama, kai sannunku sannunku." Ta ƙarashe maganar tana kallon ma'aikatan.
Wani saurayi ne ya amsa ma ta suka gaisa cikin mutunci.
Bayan ta gama zagaye gidan, ta fito tana mamakin wannan duniyar da ake ƙoƙarin gina musu.
Kichibis ta yi da Ladiyo a hanya tana ta zabga sauri kamar ƴar maula.
"Ahh ah , Ladiyo sai ina kuma?" Delu ta tambaya tana tsare Ladiyo da idanu.
"Gidanki na yi
niyyar zuwa, sai...." Sauran maganar ta maƙale ma ta a maƙoshi sakamakon ganin gidan Delu a ruguje dai aiki ake.
"Wallahi da gaske ne, wayyo!" Ladiyo ta faɗa kamar zautacciya.
Delu kam tsayawa ganin ikon Allah ta yi, dan ganin Ladiyo ta yi kamar mahaukaciya sai ɗaura hannu a kai take.
Koma dai mene Delu tasan baƙin ciki ne Ladiyo ke nuna wa ƙarara.
Wucewar ta ta yi ta bar Ladiyo na ta kwasar drama ita da leburorin.
Gida Ladiyo ta koma zuciyarta cike da baƙin ciki, taya Delu zata samu wannan duniyar ita kuma ta na nan zaune? "Kai bazai yiwu ba!" Ta faɗa a karo na ba adadi.
Nabila ce ta shigo gidan, kallon Ladiyo ta yi wacce duk ta susuce saboda ruɗewa.
"Toh fah, Ladiyo lafiya kika zauna anan kike ta surutai kamar sabuwar kamu?"
Shiru Ladiyo ta yi tana kallon Nabila, kai duk yadda za'a yi ma sai dai Nabila ta auri Alhaji Gabatari ko kuma kowa ya rasa.
Gaya ma Nabila abinda ke faruwa ta yi suka tsaya suna shawarwari, a ƙarshe dai suka yanke cewa Ladiyo zata samu bokan kan tudu su zanta.
*Ayaman*
Shirye shiryen biki suke ba abinda ya dame su, dan yanzu ma kiɗan kwarya ake ta zabgawa a tsakar gidan su tsahare ana ta rausayawa.
Sai wurin la'asar aka kammala kiɗan ƙwaryan, mutane sun fara raguwa tunda an kammala bikin yau saura kuma gobe da za'a ɗaura aure.
Bayan sun gama hutawa suka kama hanyar gidan yayar tsahare, su kusan tara dan ba laifi ƴan uwan tsahare sun zo da dama.
Hirarsu suke cikin kwanciyar hankali har dare ya tsaga, dan Anty Nusaiba ba ruwanta akwai hira.
Da asuba da suka farka basu koma bacci ba suka shiga shirye shirye, gidansu tsahare suka nufa dan a chan ne amarya zata shirya.
Wurin ƙarfe goma na safe aka ɗaura auren tsahare wanda asalin sunanta Fatima ita da angonta Usman.
Biki kam ya yi biki dan kofar gidansu tsahare ya cika tanƙam da mutane ana shaida daurin aure yayin da mata ke cikin gida suna ta hidimar abinci.
Maganganu suka yi na lokaci mai tsawo sannan ya dauko wata ƙaramar baƙar laya a cikin ƙoƙon jakin da ke wurin ya miƙa wa Ladiyo yana faɗin "Wannan shi ne ƙarshen matsalar ki, ki yi aiki da shi zaki bani labari."
Ya juya wurin Delu yace, "Duk abinda kike aikatawa ina ganin ki ta ƙwaryata, abinda zance shi ne ki bi a hankali ." Daga nan ya ja bakinsa ya yi shiru.
Sumsum suka fice daga kogon bayan biyansa da suka yi da mutuncinsu.
********************************
*Ayaman*
Baccinta take cikin kwanciyar hankali kawai taji alamar ana tashin ta daga bacci, a ɗan razane ta ja bargon ta rufe kanta tana karanto ayoyin Alkur'ani.
Kuma jin ana jan zanin da ta rufa da shi ta ji ana yi, da sauri ta ja ta kuma tofa addu'a kusa da ita.
Again aka kuma jan zanin, ta yi ta maza ta miƙe zaune, wayam babu kowa a ɗakin, chan ta hango wani abu kamar mutum a tsaye ya tunkaro ta.
Duk addu'ar da ta zo bakinta take yi har wannan abin ya cimma ta....
Love you all 💞 💙
More comment more typing ✍️
https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8
😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈
By
Khairat 💞💙
Page 29-30
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️*
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Lokaci na ta shuɗewa, abubuwa na ƙara haɓaka, ta ɓangaren Ayaman ma haka.
Lamura sai ƙara gaba suke dan yanzu Ladiyo ta yi yadda ta yi aka sa ranar aurenta da Anas, har yanzu bata gama mamakin Ladiyo ba har sai da ta ga saura watanni uku bikinta da Anas.
Tashi ta yi daga kan zanin da take sallah, tsayawa ta yi ta na kallon tsakar gidan, gari ya waye tangararan, rana ta fara fitowa alamar za'a yi rana mai zafi.
Ruwa ta ɗebo a randa ta shiga banɗaki, bayan ta fito ta fara aikin gidan, ta gama ta yi wanka tasa kaya.
Abin kari Ladiyo ta miƙo ma ta dan ba laifi ta ga sauyi sosai daga wurin Ladiyo wanda bata gama yadda da shi ba.
Ta kammala cin abincin ta fice zuwa gidan su tsahare dan bikin saura kwanaki uku.
Ta na shiga gidan ta tarar da tsahare ana shafa ma ta kurkur dan shi ne abinda yawancin ƴan garin ke amfani da domin gyaran amarya.
Bayan ta gaisa da Innar su tsaharen da wasu daga cikin ƴan uwansu tsahare, ta zauna aka fara fira tana taya su ayyuka har aka kammala gyaran jikin.
Wuraren ɗaya na rana suka fita rabon katin biki , sun zagaya gidaje da yawa na ƴan uwa da abokan arziki sun raba kati.
Sai ana kiran magriba suka shiga gidansu tsahare a gajiye.
Innar su da sauran ƴan uwa da suka fara zuwa na ɗaki su na gabatar da sallar magriba.
Bayan sun idar da sallah suka ci abinci sannan Ayaman ta yi ma ta sallama da niyyar gobe da wuri zata fito domin za'a yi sa lalle.
*******************************
*Farouk*
Ta ɓangaren Farouk da Ummu Kulsum abu sai ƙara tabarbarewa yake, dan yanzu an sa ranar auren Farouk da Nafee.
Ummu Kulsum ta yi kukan har ta gaji, har ga Allah ta gaji da rayuwar gidan Farouk, ga Amminsa ma kamar shi ta daina bata kulawa kamar da.
Dan akwai ranar da ta je gaishe ta, ta amsa ma ta ciki ciki kuma ta tashi ta bar falon.
A ganin Ummu Kulsum ba laifi ne ba dan ta shiga ɗakin Ammi dan ta saba da hakan, mafi yawancin lokuta Ammin da kanta take jan ta ɗaki tai ta bata haƙuri saboda ta san zaman da suke ita da Farouk .
Amma a wannan lokacin tana shiga ɗakin,Ammi ta hau ta da faɗa da masifa, "Banda tsabar munafirci, meye kuma na shigo min ɗaki? Tsaya kiji bazan dauki wannan abin ba dan haka fitar min a ɗaki!." Ammi ta ƙarasa cikin faɗa.
Cikin tsoro Ummu Kulsum tace "Kiyi haƙuri Ammi, na zata ba laifi ne dan na shigo ɗakin ki ba."
"Tunda na uwarki ne ay dole baza ki ɗauka laifi ne ba, fita kafin ki ƙarasa ɓata min rai."
Ammi ta faɗa tana rufe idanu irin na wanda ke masifa.
Sumsum Ummu Kulsum ta fita daga ɗaki tana mamakin me ya samu Ammi.
Ta ɓangaren Ammi kuwa, hakanan taji ta tsani ganin Ummu Kulsum a kusa da ita, babu dalili ko ɗaya.
Ummu Kulsum ta zauna a falon cike da zullumi, dan dama ta zo ne domin gayama Ammi halin da take ciki sai gashi ta tarar da Ammi a wani yanayi da bata taɓa ganin ta ba.
********************************
*Nafee*
Yanzu kam Nafee ranta fess an sa ranar aurenta da Farouk sai bankar magungunan mata take ita ala dole sai ta koma budurwa, ga Lubna dake gefe tana ƙara zuga ta.
Su na zaune a falon Nafee, Lubna na kallon wayarta sai ƙawar Lubna Zainab tana cin kayan marmari, ita luma Nafee ta na jujjuya wani abu a hannunta.
"Lubna anya kuwa?" Nafee ta faɗa cikin rashin yadda da tantama tana juya maganin a hannu.
"Nafee, kina tantama ne? Tsaya kiji wannan maganin sai da na tsallake rijiyoyi biyar kafin na amso miki su."
Lubna ta numfasa sannan ta cigaba da faɗin, "Wannan ɗan ƙaramin, hmm." Ta faɗa ta a ɗaga sa sama.
"Cika aiki kenan, in dai kika yi amfani da shi, hmmm wai inji mai ciwon haƙori ba'a magana kawai." Lubna ta ƙarasa faɗa tana yin alamar rufe baki kamar zip.
Haka suka cigaba da hirarsu,su na ta shewa kamar an yi musu hajji da Umrah.
********************************
*Ladiyo*
Abubuwa su na tafiyar ma ta yadda take so, dan yanzu ta sa malam Isyaku a gaba har sai da aka sa ranar auren Ayaman.
Matsalarta, Nabila sai Yunusa amma wannan bai dame ta ba kamar Ayaman, ta tsani ganinta cikin farin ciki ko walwala.
Ita da Delu ne suke kiɗansu suke rawarsu..
Love you all 💞 💙
More comment more typing ✍️
Khairat ✍️🤍https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈
By
Khairat 💞
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 31-32
Ita da delu ke kiɗansu su na rawarsu...
Dan ayanzu haka, alhaji Gabatari ya nemi auren Mariya kuma Delu ta yi uwa ta yi makarɓiya sai da aka yadda da shi.
Rayuwa ta yi ma ta sumul, bata da wata damuwa, dan yanzu ma Alhaji Gabatari ya aiko masu aikin gini zasu rushe gidan ayi musu sabo dal.
Ta ɓangaren Malam Surajo kam ba'a magana, dan yanzu duk ya susuce duk wanda ya sanshi a baya ya ganshi yanzu sai ya kasa gane shi.
Har ranar auren Mariya da aka sa bai da masaniya a matsayin sa na mahaifinta, sai lemu da Delu ta bashi tace an saka rana.
Yanzu ma masu aiki ne ke ta fama da aiki, dan an ruguje gidan tass , Delu ta shigo gidan da yake a gidan wasu ƴan uwanta suke zaune kafin a kammala aikin.
Washe baki ta yi tace "Sannun ku da ƙoƙari , kuna ta fama, kai sannunku sannunku." Ta ƙarashe maganar tana kallon ma'aikatan.
Wani saurayi ne ya amsa ma ta suka gaisa cikin mutunci.
Bayan ta gama zagaye gidan, ta fito tana mamakin wannan duniyar da ake ƙoƙarin gina musu.
Kichibis ta yi da Ladiyo a hanya tana ta zabga sauri kamar ƴar maula.
"Ahh ah , Ladiyo sai ina kuma?" Delu ta tambaya tana tsare Ladiyo da idanu.
"Gidanki na yi
niyyar zuwa, sai...." Sauran maganar ta maƙale ma ta a maƙoshi sakamakon ganin gidan Delu a ruguje dai aiki ake.
"Wallahi da gaske ne, wayyo!" Ladiyo ta faɗa kamar zautacciya.
Delu kam tsayawa ganin ikon Allah ta yi, dan ganin Ladiyo ta yi kamar mahaukaciya sai ɗaura hannu a kai take.
Koma dai mene Delu tasan baƙin ciki ne Ladiyo ke nuna wa ƙarara.
Wucewar ta ta yi ta bar Ladiyo na ta kwasar drama ita da leburorin.
Gida Ladiyo ta koma zuciyarta cike da baƙin ciki, taya Delu zata samu wannan duniyar ita kuma ta na nan zaune? "Kai bazai yiwu ba!" Ta faɗa a karo na ba adadi.
Nabila ce ta shigo gidan, kallon Ladiyo ta yi wacce duk ta susuce saboda ruɗewa.
"Toh fah, Ladiyo lafiya kika zauna anan kike ta surutai kamar sabuwar kamu?"
Shiru Ladiyo ta yi tana kallon Nabila, kai duk yadda za'a yi ma sai dai Nabila ta auri Alhaji Gabatari ko kuma kowa ya rasa.
Gaya ma Nabila abinda ke faruwa ta yi suka tsaya suna shawarwari, a ƙarshe dai suka yanke cewa Ladiyo zata samu bokan kan tudu su zanta.
*Ayaman*
Shirye shiryen biki suke ba abinda ya dame su, dan yanzu ma kiɗan kwarya ake ta zabgawa a tsakar gidan su tsahare ana ta rausayawa.
Sai wurin la'asar aka kammala kiɗan ƙwaryan, mutane sun fara raguwa tunda an kammala bikin yau saura kuma gobe da za'a ɗaura aure.
Bayan sun gama hutawa suka kama hanyar gidan yayar tsahare, su kusan tara dan ba laifi ƴan uwan tsahare sun zo da dama.
Hirarsu suke cikin kwanciyar hankali har dare ya tsaga, dan Anty Nusaiba ba ruwanta akwai hira.
Da asuba da suka farka basu koma bacci ba suka shiga shirye shirye, gidansu tsahare suka nufa dan a chan ne amarya zata shirya.
Wurin ƙarfe goma na safe aka ɗaura auren tsahare wanda asalin sunanta Fatima ita da angonta Usman.
Biki kam ya yi biki dan kofar gidansu tsahare ya cika tanƙam da mutane ana shaida daurin aure yayin da mata ke cikin gida suna ta hidimar abinci.