Sashe 16
Mugunta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hira suka fara sama-sama kana Anas ya shigo ya tarar da su, zama ya yi a kan bokiti yana faɗin "Nima ayi hirar da ni."
Anan zamu dakata sai Allah ya kaimu, more comment more typing ✍️
Khairat ce ✍️ 🤍
Love you all 💞😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈
By
Khairat ✍️🤍
https://chat.whatsapp.com/Js1xb4FBd2v0o5mxXpssVr
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/FYbZw86FTfQDpyIkILlMuN
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.
_With strong passion, we change pain into strength,and dreams into stories. We are Jajirtattu Writers born to share powerful words.🤌💪_
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 47-48
----------Hira suka fara yi sama-sama kana Anas ya shigo yace "Nima ayi hirar da ni."
Ƙasa Ayaman tayi da kanta ta kasa magana, ta na jinsu su na hira iya kaci in abin dariya suka yi ta yi in na girgiza kai ne shi ma ta yi.
Chan zuwa hantsi Anas ya shirya ya fita nema, yayin da Ayaman ke ƙoƙarin taya mahaifiyarsa wasu ayyukan.
Su na kammala girkin innar Anas ta umarce ta da ta ɗauko flask ta zuba musu nasu, haka kuwa aka yi bayan sun gama komai da komai suka zauna ƙarƙashin rumfar innar Anas su na taɓa hira.
Kayan saƙa Inna ta ɗauko tana yi yayin da Ayaman ke kallon komai kuma ta fara yunƙurin iya wa.
********************************
*_Ladiyo_*
Gari na wayewa ta fara kichiniyar yadda zata gyara gidan da kuma girki domin tarbar baƙi.
Wurin Habu mahauci ta nufa domin siyo nama, ai kuwa ta samu anyi sabon yanka dana haka aka zuba mata namanta ta yi gaba.
Tayo sauran chefanen kama daga lemukan kwalba, kayan miya, shinkafa da sauransu.
Tana isa gida ta ɗaura tunkuya ta hau aiki gadan-gadan.
Nabeela na ɗaki tana kwance ko tunanin taya mahaifiyarta aiki bata yi ba, hasali ma ita ba iya wani aikin gida tayi ba dan tun tasowarsu da ƴanmatanci Ayaman ce baiwarsu dan ita take komai a gidan, dan its Nabeela bata ƙi wanka ma Ayaman tayi mata ba.
Zuwa bayan azahar Ladiyo ta kammala wasu daga cikin ayyukan, shinkafa da waken da tayi duk ta chaɓe tayi ta ruwa, miyar kam ƙarni kamar me ita s ganinta tayi komai dai-dai.
Sabuwar tabarmarta ts ɗauko ta shimfiɗa a ƙarƙashin bishiyar mangwaron da ke tsakar gidan, ra ɗauko komai ta ajiye sa inda ya dace.
Tana aiki tana magana ita kaɗai, "Ay wallahi Nabeela tayi goshi, kai kai kai ." Sai kuma ta cigi yatsa kamar taɓabɓiya.
Wuraren la'asar Malam Isyaku da amininsa sai wani ƙaninsa da sai da aka sha gumurzo kafin ya yadda yazo dan Ladiyo ba irin wulaƙancin da bata musu, daga tace ɗangin matsiyata sai tace masu ƙashin tsiya abubuwa dai iri-iri.
Wani yaro ne ya shigo ya same su a kan tabarma su uku, "Ina wuninku, wai ana sallama da malam Isyaku."
"Toh maza je kace yana zuwa." Ladiyo tayi charaf ta amsa mai.
Haka kuwa aka yi, Malam Isyaku ya mike ya fita, manyan mutane ne su huɗu sun sha babbar riga wadda daka gani kasan sai an sa kuɗi mai yawa za'a iya siya.
"Assalamu Alaikum." Malam Isyaku ya faɗa ya na miƙa musu hannu domin suyi musabaha.
"Waalaikumus salaam." Suka amsa suna gaisawa cikin mutunta juna.
Iso ya yi musu zuwa cikin gidan, suna shiga suka zazzauna a kan tabarma suka gaisa da su kawu Bello.
Bayan wani lokaci sai ga Ladiyo ta fito a cikwikwiye cikin gumi da alama ko wanka bata yi ba.
Tana fitowa ta fara washe musu baki tana gaishesu, amsawa suka yi sannan suka fara gabatar da abinda ya kawo su.
Kawu Bello ne ganin rashin dacewar zaman Ladiyo a wurin ganin duk masu gemu ne a wurin ya sa shi faɗin, "Ladiyo ki shiga daga ciki mana ay bai kamata ki tsaya anan ba."
Kallon banza ta bishi da shi kafin tace "Ƴar ka ko tawa? Ina ruwanka da ni? Wato salon ana bada kuɗin ku yagi rabonku ko? Toh wallahi ina nan sai an yi komai a gabana." Ts ƙarashe tana wani juyar da kai haɗe da murguɗa baki.
Rasa mai kawu Bello zai ce ya yi, kawai ya ja bakinsa ya yi shiru.
Malam Isyaku sam bai ji daɗin abinda ya faru ba, amma ganin baƙi yasa sa ya yi shiru dan yanzu Ladiyo ta faɗa mai maganar da ta so.
Buɗe taron da addu'a aka yi sannan aka fara gabatar da abinda ya tara su a wurin, Babban yayan Alhaji Gabatari, wato Alhaji Aminu ne ya nemar wa Gabatari auren Nabeela.
Ladiyo tayi charaf tace"Ay an riga da an gama kawai ku gayi nawa kuka zo da shi da kuma ranar da kuke son ayi bikin."
Sakin baki Alhaji Aminu ya yi da sauran mutanen wurin dan ganin wannan lamari na Ladiyo.
Kallon juna Alhaji Aminu da Alhaji Ahmed abokin Alhaji Gaɓatari.
Ganin yadda Ladiyo tayi babakere a kan lamarin, yasa suka amince a kan nan da kwana ishirin da ɗaya za'a ɗaura aure, sannan kuma suka bada kuɗin tambaya naira dubu ɗari biyar.
Suma ne kawai Ladiyo bata yi ba sakamakon ganin wannan zunzurutun kuɗi, ai kuwa suna ajiye wa tayi saurin ɗauke kuɗin ta maƙe su a hammata.
"Ai Alhaji kuje kawai, auren Nabeela da Alhaji kawa an riga da anyi ne." Ta faɗa tana miƙe wa har da taka rawa sannan tayi cikin gidan da kuɗin.
Alhaji Aminu da Alhaji Ahmed ne suka kalli juna suna murmushi.
Sallama suka yi kafin kowa ya tafi harkokin gabansa, shi dai kawu Bello cike da takaicin matar yayan nasa ya tafi yana Allah wadai da abinda tayi.
Shi kuma malam Sani aminin malam Isyaku ya same shi yace "Kaga dai yadda tayi komai ba tare da ko kunyar idanunmu ba, dan haka ya kamata ka gyara ɓarakar da take gidanka, na bar ka lafiya." Ya ƙarashe yana barin wurin.
Ladiyo kuwa a cikin gida hauka ne kawai bata yi ba, sakamakon ganin wannan zunzurutun kuɗaɗe.
********************************
*_Nafee da Farouk _*
Ko kaɗan Nafee ta ƙi barin Farouk ya fita, ko sallah ma s gida ta umarce sa ya yi shi kuwa da yake an riga an shanye shi, ba abinda ya isa ya yi.
Yanzun ma tana jikinsa ta maƙale mai kamar mayya, shi ya rasa wannan jaraba irin ta Nafee ace kusan duk bayan wasu awanni sai ta buƙaci namiji? Gashi ita kamar ba mace ba haka yake jinta, wallahi a ƴan kwanakin nan ya yi missing ɗin Ummu Kulsum, ga kyau ga hankali ga shi ta san ta yadda take gamsar da shi ko ba tare da sun yi sex ba.
Ita kuwa Nafee banda muguwar ƙazanta da rashin sanin ya kamata ba abinda ta iya sai kuma yawan buƙatarta kamar me.
Wallahi har ga Allah ya fara gajiya da Nafee, kwana uku da aure har ta ɗauko ƴar aiki dan ita tace ita ba baiwa bace dan haka ba ruwanta da wani aiki.
Haka ma ta ɓangaren girki ko cokali bata ɗaga wa, Ummu ce ta zama kukun sun ita take girka musu na safe, na rana da na dare har na da wasu tsirface-tsirfacen Nafee duk ita take yi.
(Kaɗan ma ka fara gani Farouk)
********************************
*_Ummu_*
Lallashin Mu'ayyad take ta faman yi dan kwana biyu ya sako ta a gaba banda rigima ba abinda ya iya.
Dare ne ga wata uwar gajiya da ta tara dan Nafee yau girke-girke ba wanda bata sata ba, har meat pie ta sata yi duk dan ta wahalar da ita.
Gashi dare ya yi maimakon ta huta sai ma wata sabuwar gajiyar da Mu'ayyad yake son ɗaura mata, ringing ɗin wayarta ne ya tayar ta ita taje ta ciro ta a chaji, number Farouk ce wadda ta yi saving da Abban Mu'ayyad.
Ɗaga wa ta yo kafin tace komai taji muryar Nafee, ki dafo min tea ki kawo min yanzu.
Kamar zata kurma ihu haka ta dafa tea ta juye a flask ta dauki hijabi da Mu'ayyad ta nufi sashen Nafee.
Su na zaune a falo su na kallon wani American film ta shiga ta samesu, Nafee ta yi luff a jikin Farouk wanda ya lulluɓe ta a bargo da alama ko kaya babu a jikinsu.
Ajiye tea ɗin ta yi ta miƙe da niyyar fita, "Ɗumamamin meat pie a microwave ki kawo min nan." Taji muryar Nafee cike da izza.
Kitchen ta nufa ta aikata abinda aka sa ta kafin ta bar sashen.
Tana fita ta shaqi wata iska mai daɗi, dan indai tana sashen Nafee bata iya numfashi da kyau dan ba ƙaramin tsoronta take ji ba.
Tana shiga sashenta ta lallaɓa Mu'ayyad ya yi bacci finally ita ma dai ta samu lokacin kanta.
Sai mun haɗu a next page more comment more typing ✍️
Khairat ce ✍️ 🤍
Love you all 💞 🥰😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈
By
Khairat ✍️🤍
https://chat.whatsapp.com/Js1xb4FBd2v0o5mxXpssVr. (Posting room)
My WhatsApp group comment section 👇 👇 👇 👇
https://chat.whatsapp.com/FYbZw86FTfQDpyIkILlMuN
Wannan page ɗin ma sadaukar da shi zuwa ma karanta littafin MUGUNTA da masu comment, ina godiya I love you lodi lodi🙈❤️🩹💋♥️♥️♥️♥️♥️♥️♥️.
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.
_With strong passion, we change pain into strength,and dreams into stories. We are Jajirtattu Writers born to share powerful words.🤌💪_
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 49-50
*END OF BOOK ONE*
Haka ana kiran asuba ta farka kamar birkitacciya, alwala ta ɗauro ta tayar da sallah.
Tana jin Mu'ayyad na maganganunsa tayi mai shiru.
Ko ƙarasa azkhar baya yi ba ta fara gyangyaɗi, ay kuwa ta koma gado taja blanket tayi baccinta.
********************************
*_Ladiyo_*
Anan zamu dakata sai Allah ya kaimu, more comment more typing ✍️
Khairat ce ✍️ 🤍
Love you all 💞😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈
By
Khairat ✍️🤍
https://chat.whatsapp.com/Js1xb4FBd2v0o5mxXpssVr
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/FYbZw86FTfQDpyIkILlMuN
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.
_With strong passion, we change pain into strength,and dreams into stories. We are Jajirtattu Writers born to share powerful words.🤌💪_
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 47-48
----------Hira suka fara yi sama-sama kana Anas ya shigo yace "Nima ayi hirar da ni."
Ƙasa Ayaman tayi da kanta ta kasa magana, ta na jinsu su na hira iya kaci in abin dariya suka yi ta yi in na girgiza kai ne shi ma ta yi.
Chan zuwa hantsi Anas ya shirya ya fita nema, yayin da Ayaman ke ƙoƙarin taya mahaifiyarsa wasu ayyukan.
Su na kammala girkin innar Anas ta umarce ta da ta ɗauko flask ta zuba musu nasu, haka kuwa aka yi bayan sun gama komai da komai suka zauna ƙarƙashin rumfar innar Anas su na taɓa hira.
Kayan saƙa Inna ta ɗauko tana yi yayin da Ayaman ke kallon komai kuma ta fara yunƙurin iya wa.
********************************
*_Ladiyo_*
Gari na wayewa ta fara kichiniyar yadda zata gyara gidan da kuma girki domin tarbar baƙi.
Wurin Habu mahauci ta nufa domin siyo nama, ai kuwa ta samu anyi sabon yanka dana haka aka zuba mata namanta ta yi gaba.
Tayo sauran chefanen kama daga lemukan kwalba, kayan miya, shinkafa da sauransu.
Tana isa gida ta ɗaura tunkuya ta hau aiki gadan-gadan.
Nabeela na ɗaki tana kwance ko tunanin taya mahaifiyarta aiki bata yi ba, hasali ma ita ba iya wani aikin gida tayi ba dan tun tasowarsu da ƴanmatanci Ayaman ce baiwarsu dan ita take komai a gidan, dan its Nabeela bata ƙi wanka ma Ayaman tayi mata ba.
Zuwa bayan azahar Ladiyo ta kammala wasu daga cikin ayyukan, shinkafa da waken da tayi duk ta chaɓe tayi ta ruwa, miyar kam ƙarni kamar me ita s ganinta tayi komai dai-dai.
Sabuwar tabarmarta ts ɗauko ta shimfiɗa a ƙarƙashin bishiyar mangwaron da ke tsakar gidan, ra ɗauko komai ta ajiye sa inda ya dace.
Tana aiki tana magana ita kaɗai, "Ay wallahi Nabeela tayi goshi, kai kai kai ." Sai kuma ta cigi yatsa kamar taɓabɓiya.
Wuraren la'asar Malam Isyaku da amininsa sai wani ƙaninsa da sai da aka sha gumurzo kafin ya yadda yazo dan Ladiyo ba irin wulaƙancin da bata musu, daga tace ɗangin matsiyata sai tace masu ƙashin tsiya abubuwa dai iri-iri.
Wani yaro ne ya shigo ya same su a kan tabarma su uku, "Ina wuninku, wai ana sallama da malam Isyaku."
"Toh maza je kace yana zuwa." Ladiyo tayi charaf ta amsa mai.
Haka kuwa aka yi, Malam Isyaku ya mike ya fita, manyan mutane ne su huɗu sun sha babbar riga wadda daka gani kasan sai an sa kuɗi mai yawa za'a iya siya.
"Assalamu Alaikum." Malam Isyaku ya faɗa ya na miƙa musu hannu domin suyi musabaha.
"Waalaikumus salaam." Suka amsa suna gaisawa cikin mutunta juna.
Iso ya yi musu zuwa cikin gidan, suna shiga suka zazzauna a kan tabarma suka gaisa da su kawu Bello.
Bayan wani lokaci sai ga Ladiyo ta fito a cikwikwiye cikin gumi da alama ko wanka bata yi ba.
Tana fitowa ta fara washe musu baki tana gaishesu, amsawa suka yi sannan suka fara gabatar da abinda ya kawo su.
Kawu Bello ne ganin rashin dacewar zaman Ladiyo a wurin ganin duk masu gemu ne a wurin ya sa shi faɗin, "Ladiyo ki shiga daga ciki mana ay bai kamata ki tsaya anan ba."
Kallon banza ta bishi da shi kafin tace "Ƴar ka ko tawa? Ina ruwanka da ni? Wato salon ana bada kuɗin ku yagi rabonku ko? Toh wallahi ina nan sai an yi komai a gabana." Ts ƙarashe tana wani juyar da kai haɗe da murguɗa baki.
Rasa mai kawu Bello zai ce ya yi, kawai ya ja bakinsa ya yi shiru.
Malam Isyaku sam bai ji daɗin abinda ya faru ba, amma ganin baƙi yasa sa ya yi shiru dan yanzu Ladiyo ta faɗa mai maganar da ta so.
Buɗe taron da addu'a aka yi sannan aka fara gabatar da abinda ya tara su a wurin, Babban yayan Alhaji Gabatari, wato Alhaji Aminu ne ya nemar wa Gabatari auren Nabeela.
Ladiyo tayi charaf tace"Ay an riga da an gama kawai ku gayi nawa kuka zo da shi da kuma ranar da kuke son ayi bikin."
Sakin baki Alhaji Aminu ya yi da sauran mutanen wurin dan ganin wannan lamari na Ladiyo.
Kallon juna Alhaji Aminu da Alhaji Ahmed abokin Alhaji Gaɓatari.
Ganin yadda Ladiyo tayi babakere a kan lamarin, yasa suka amince a kan nan da kwana ishirin da ɗaya za'a ɗaura aure, sannan kuma suka bada kuɗin tambaya naira dubu ɗari biyar.
Suma ne kawai Ladiyo bata yi ba sakamakon ganin wannan zunzurutun kuɗi, ai kuwa suna ajiye wa tayi saurin ɗauke kuɗin ta maƙe su a hammata.
"Ai Alhaji kuje kawai, auren Nabeela da Alhaji kawa an riga da anyi ne." Ta faɗa tana miƙe wa har da taka rawa sannan tayi cikin gidan da kuɗin.
Alhaji Aminu da Alhaji Ahmed ne suka kalli juna suna murmushi.
Sallama suka yi kafin kowa ya tafi harkokin gabansa, shi dai kawu Bello cike da takaicin matar yayan nasa ya tafi yana Allah wadai da abinda tayi.
Shi kuma malam Sani aminin malam Isyaku ya same shi yace "Kaga dai yadda tayi komai ba tare da ko kunyar idanunmu ba, dan haka ya kamata ka gyara ɓarakar da take gidanka, na bar ka lafiya." Ya ƙarashe yana barin wurin.
Ladiyo kuwa a cikin gida hauka ne kawai bata yi ba, sakamakon ganin wannan zunzurutun kuɗaɗe.
********************************
*_Nafee da Farouk _*
Ko kaɗan Nafee ta ƙi barin Farouk ya fita, ko sallah ma s gida ta umarce sa ya yi shi kuwa da yake an riga an shanye shi, ba abinda ya isa ya yi.
Yanzun ma tana jikinsa ta maƙale mai kamar mayya, shi ya rasa wannan jaraba irin ta Nafee ace kusan duk bayan wasu awanni sai ta buƙaci namiji? Gashi ita kamar ba mace ba haka yake jinta, wallahi a ƴan kwanakin nan ya yi missing ɗin Ummu Kulsum, ga kyau ga hankali ga shi ta san ta yadda take gamsar da shi ko ba tare da sun yi sex ba.
Ita kuwa Nafee banda muguwar ƙazanta da rashin sanin ya kamata ba abinda ta iya sai kuma yawan buƙatarta kamar me.
Wallahi har ga Allah ya fara gajiya da Nafee, kwana uku da aure har ta ɗauko ƴar aiki dan ita tace ita ba baiwa bace dan haka ba ruwanta da wani aiki.
Haka ma ta ɓangaren girki ko cokali bata ɗaga wa, Ummu ce ta zama kukun sun ita take girka musu na safe, na rana da na dare har na da wasu tsirface-tsirfacen Nafee duk ita take yi.
(Kaɗan ma ka fara gani Farouk)
********************************
*_Ummu_*
Lallashin Mu'ayyad take ta faman yi dan kwana biyu ya sako ta a gaba banda rigima ba abinda ya iya.
Dare ne ga wata uwar gajiya da ta tara dan Nafee yau girke-girke ba wanda bata sata ba, har meat pie ta sata yi duk dan ta wahalar da ita.
Gashi dare ya yi maimakon ta huta sai ma wata sabuwar gajiyar da Mu'ayyad yake son ɗaura mata, ringing ɗin wayarta ne ya tayar ta ita taje ta ciro ta a chaji, number Farouk ce wadda ta yi saving da Abban Mu'ayyad.
Ɗaga wa ta yo kafin tace komai taji muryar Nafee, ki dafo min tea ki kawo min yanzu.
Kamar zata kurma ihu haka ta dafa tea ta juye a flask ta dauki hijabi da Mu'ayyad ta nufi sashen Nafee.
Su na zaune a falo su na kallon wani American film ta shiga ta samesu, Nafee ta yi luff a jikin Farouk wanda ya lulluɓe ta a bargo da alama ko kaya babu a jikinsu.
Ajiye tea ɗin ta yi ta miƙe da niyyar fita, "Ɗumamamin meat pie a microwave ki kawo min nan." Taji muryar Nafee cike da izza.
Kitchen ta nufa ta aikata abinda aka sa ta kafin ta bar sashen.
Tana fita ta shaqi wata iska mai daɗi, dan indai tana sashen Nafee bata iya numfashi da kyau dan ba ƙaramin tsoronta take ji ba.
Tana shiga sashenta ta lallaɓa Mu'ayyad ya yi bacci finally ita ma dai ta samu lokacin kanta.
Sai mun haɗu a next page more comment more typing ✍️
Khairat ce ✍️ 🤍
Love you all 💞 🥰😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈
By
Khairat ✍️🤍
https://chat.whatsapp.com/Js1xb4FBd2v0o5mxXpssVr. (Posting room)
My WhatsApp group comment section 👇 👇 👇 👇
https://chat.whatsapp.com/FYbZw86FTfQDpyIkILlMuN
Wannan page ɗin ma sadaukar da shi zuwa ma karanta littafin MUGUNTA da masu comment, ina godiya I love you lodi lodi🙈❤️🩹💋♥️♥️♥️♥️♥️♥️♥️.
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.
_With strong passion, we change pain into strength,and dreams into stories. We are Jajirtattu Writers born to share powerful words.🤌💪_
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 49-50
*END OF BOOK ONE*
Haka ana kiran asuba ta farka kamar birkitacciya, alwala ta ɗauro ta tayar da sallah.
Tana jin Mu'ayyad na maganganunsa tayi mai shiru.
Ko ƙarasa azkhar baya yi ba ta fara gyangyaɗi, ay kuwa ta koma gado taja blanket tayi baccinta.
********************************
*_Ladiyo_*