Sashe 10
Mugunta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hirar su suka cigaba da yi har Ayaman ta daura ma ta girkin dare , su na cikin girkin Ayaman ke neman shawarar Inna a kan maganar auren Anas.
"Ya kike gani inna?"
Inna taja numfashi sannan tace "Ayaman, a rayuwar nan in kana abu dole ka nemi zaɓin Allah domin shi ne mai kowa mai komai, sannan Anas ba shi da wani aibu, yana da sana'ar sa, ba sata yake ba ko cutar wani, ga mahallin da zai aje ki , gaskiya a gani na ki amince da maganar auren nan, ko kin huta da rayuwar da kike fuskanta a yanzu." Inna ta ƙarashe maganar tana kallon Ayaman.
Shiru Ayaman ta yi tana nazarin maganganun inna, tabbas haka zancen yake in ta yi auren zata huta da rayuwar gidansu.
Nan Inna ta cigaba da bata shawarwari har ta kammala girkin suka ci tare sannan Ayaman ta yi ma ta sallama ta tafi.
Tana fita daga gidan aka kira sallar magriba, dan haka kanta a ƙasa ta fita daga gidan sakamakon mazan da ke wucewa domin shiga masallaci.
Wasu maza wanda aƙalla zasu yi sa'anin mahaifinta ne suka zo wucewa ta gaishe su, "yanzu ace malam Isyaku ya bar yarinya ta riƙa ta zama riƙaƙƙiyar kubewa, duk ta zama wata uwa a unguwa wannan ai bai dace ba." Ɗaya daga cikin mutanen ya faɗa, ɗayan kuma yace "Hmm, wa ya sa ni ko akwai abinda suka shirya shiyasa suka ƙi aurar da ita, koma dai mene muna nan muna zuba ido."
Wucewa ta yi ba tare da ta kalli ko inda suke ba duk da ta san da ita suke kuma taji me suke cewa.
Tana mamakin yadda mutane ke ma ta wata fahimtar daban, ita a ganinta aure ay lokaci ne kamar yadda mutuwa take .
Da sallama ta shiga gidan duk da ba kowa, ta tsaya a banɗaki ta yi alwala ta zo ɗaki ta dauko zanin da take sallah da shi.
A tsakar gida ta shimfiɗa ta yi sallar kasancewar akwai wutar lantarki dan sun ci sa'a an gyara musu.
Tana zaune a kan zanin har aka kira sallar Isha'i ta yi sallar ta.
Tana idarwa kam bayan ta gama zikiri ta shige ɗaki ta yi kwanciyar ta dan cikinta a koshe yake bata jin yunwa kuma tunda Ladiyo ta fita ta san sai sanda ta ga damar dawowa.
********************************
* Nafee(p.o.v)*
"Ke wallahi aikin mutumin nan yana ci, yau gashi da kansa yazo yake faɗa min zai yi magana da mamansa a kaina, kinsan mun daɗe muna fama da shi a fara maganar auren sai yau dai Allah ya yi." Nafee ta ƙarasa maganar cike da jin daɗi.
Ta ɗayan ɓangaren Lubna tace " ai ke kike wasa da tsafi, baki ji me bahaushe yace ba tsafi gaskiyar mai shi."
Hira suka cigaba da yi a kan yadda zasu shirya abubuwa dan Nafee ji take kamar an yi ma ta hajji da Umrah.
********************************
*Farouk(p.o.v)*
Yana isa office ya tarar da aiki ya yi mai yawa, dan mataimakin nasa bai yi abinda ya dace ba dan tafiyar da harkokin kamfanin.
Sai da ya gama mitar kuma ya fara aikin, har wurin la'asar yana abu ɗaya, sallah ce kawai ke tayar da shi.
Gidansa ya wuce bayan sallar la'asar.
A falo ya tarar da Ummu Kulsum tana turaren wuta, dan bata bari mai aiki ta yi ma ta.
Gaishe sa ta yi ya amsa ciki-ciki, dinning ya nufa ya bude kular abincin, masa da miyar taushe ya gani.
"Oh shit!!, wai me yake damun ki ne, jahilcin da baki gama ba a kauye shi zaki zo ki dasa min a gida? Mtcwwww."
Wullar da kular ya yi, sai ga waina ta yi ɗaiɗai a ƙasa, miyar ta biyo bayanta.
Fuuu ya wuce ɗakinsa kamar iska, kallon dinning ɗin Ummu Kulsum ta yi tana zama turuss a kan kujera.
Kuka ta fashe da shi mai ciwo, ita meye laifinta? Dan kawai daga ƙauye aka kawo ta shi ne ta yi jahilci? Ace kusan shekara ɗaya kana rayuwa da mutum amma baka taɓa samun farin ciki ba? Sai yaushe kenan?? Ta tambayi kanta cikin kuka.
A gaskiya ta fara gajiya da halin Farouk, ba zata ga murmushinsa ba sai in dare ne ya yi yana nemanta? "Na jure da yawa wallahi." Ummu Kulsum ta kuma faɗa tana kuka.
Mop da tsintsiya ta dauko ta gyara gurin dan Allah ya sa ta aiki ƴar aikinta wani wuri da tuni a gabanta zai yi wannan abin.
Bayan ta gama gyara gurin ta shige ɗakinta ta kullo ƙofa, tana tunanin raba ta da aka yi da masoyinta aka aura ma ta Farouk da sunan zumunci.
*Asalin su Farouk*
Love you all 💞💋 ❤️
More comment more typing ✍️
Khairat ✍️https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
*😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈*
By
*Khairat 💞💙*
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 27-28
*Asalin su Farouk*
Mahaifin Farouk Alhaji Aliyu Umar Datti ɗan asalin garin Katsina ne a kaita local government.
Ya taso cikin gata inda ya kasance shi kaɗai ne ɗan Fateema da Umar, dan shima sai da aka jima sannan aka haife sa.
Ya yi karatunsa na boko da Arabi a nan kaita inda ya tafi babbar University a lokacin wadda ita ce University of Lagos.
A nan makaranta ya hadu da Amina, har ta kai su da fara soyayya mai karfi, Amina ƴar asalin garin Lagos ce inda aka haife ta take.
Bayan kammala karatunsu ne Farouk ya gabatar da kansa a wurin iyayen ta har ta kai ga ya tura manya domin nemo mai auren Amina.
A lokacin an sha gumurzu kafin iyayen Amina su amince da auren dan sun so Amina ta auri wani ɗan uwanta.
An daura aure da kimanin sati biyu aka dauko Amina daga Lagos zuwa gidan Aliyu dake Katsina bayan nasihohi masu ratsa zuciya da iyayenta suka yi ma ta.
Watan Amina biyu a gidan Aliyu ta fara laulayi inda bayan cikin ya cika wata tara da ƴan kwanaki ta haifo santaleliyar ƴar ta mai kama da ubanta, aka raɗa ma ta suna Halima wanda sunan mahaifiyar Amina ne.
Halima taga gata iya gata a wurin iyayenta da kakkaninta kasancewar ta jikar farko a family ɗin.
Halima na da shekara biyar Amina ta kuma haifar ƴa mace wadda taci suna Raihana.
Bayan haihuwar Raihana ne suka koma garin Kano da zama saboda sauyin wurin aiki da Aliyu ya samu.
Amina sai da ta jima dan sai da Raihana ta kai shekara goma sannan ta haifo ɗa namiji wato Farouk.
Amina da Aliyu suka haɗa kam ƴaƴansu suka raina har suka kawo karfi, Halima ta yi aure da kwanaki kaɗan Allah ya amshi ran Aliyu sai gidansa na gaskiya.
A lokacin sunyi baƙin cikin rashin uban nasu amma suka yi tawakkali suka rumgumi ƙaddararsu.
A haka rayuwa ta cigaba da nisawa har Raihana ta kammala karatunta ta yi auri inda ta auri ɗan mataimakin shugaban kasa su na zaune a Abuja.
Lokaci zuwa lokaci Fateema tana kawo wa jikokinta ziyara, a wannan zuwa ta taho da wata budurwa wadda tace jikar aminiyar ta ce wacce mahaifiyar ta ta rasu tana da tarbiyya da hankali dan haka take son haɗa ta da Farouk.
A lokacin hauka ne kawai Farouk bai yi ba dan ya gama shirinsa zai auri Nafee sai ga Ummu Kulsum ta shigo.
Hajjo (Fateema) ta yi amfani da ƙarfin ikonta har aka ɗaura auren Farouk da Ummu Kulsum.
Tun daga lokacin Farouk yake ƙullace da Ummu Kulsum na ganin ta yadda an daura auren bayan jan kunnen da ya yi ma ta.
Tana zaune an lulluɓe ta da mayafi ta yi shiru tana tunanin wannan sabuwar rayuwar da zata shiga, kawai taji an ja ma ta mayafin aka cillar a ƙasa.
A yatsine yake kallon ta kamar ya ga wani abin ƙi, ya buɗe baki da kyar yace "Finally kin yadda an daura auren, har an kawo ki gidan nan, ya yi kyau..." Ya faɗa yana cilla ma ta kaza wadda bisa umurnin Ammi ya siya.
Ɗago kai ta yi ta ga yana ficewa daga ɗakin, "Ikon Allah." Ta faɗa a ranta.
Tashi ta yi tana kallon ɗakin, gaskiya iya tsaruwa ya tsaru amma dimm gabanta ya faɗi sanin ba wani zaman daɗi zata yi a gidan ba.
Haka ta yi ta hakuri da zama da Farouk, wata ranar ya dawo a bige ya neme ta ta ƙarfi, wata rana ya kawo matan banza har sai da abin ya dame ta ta gaya wa Ammi sannan ta tsawatar mai, shi ne ta ɗan samu sauƙin matan da yake kawo wa.
A haka har ta haifi Mu'ayyad, a haka kuma Farouk bai daina abin da yake ba sai dai ma ƙaruwa da yake.
Wannan kenan...
*Cigaban labari*
A karo na ba adadi Ummu Kulsum ta kuma fashe wa da wani kukan tuno rayuwar ta da ta yi a garin su, ga masoyinta da aka raba ta da shi ganin shi ba kowa bane .
Da ta gaji da kukan ta tashi ta ɗauro alwala a banɗaki ta yi nafila tana kai ƙaran Farouk wurin Allah.
********************************
*Ladiyo*
Tana nan har bayan sallar Isha'i a gidan Delu, sai wurin ƙarfe tara na dare sannan suka yi shirin zuwa wurin boka Barqaan.
A hankali suke hawa kan tsaunin gudun kar wata ta fado wani abu ya same ta.
Kamar yadda al'adar da kuma tsarin Barqaan yake, ba'a shigar mai kogo da kaya dole ka cire su , ka ajiye har sai ka fito.
Babu tsoro ko kunya su Ladiyo suka aikata abinda aka umarce su kafin suka shiga cikin kogon.
Boka Barqaan yana nan cikin kogon zaune cikin kazanta da ɗoyi wanda su Ladiyo basa ji sakamakon rufewa da idanunsu ya yi wurin neman taimako.
"Ya kike gani inna?"
Inna taja numfashi sannan tace "Ayaman, a rayuwar nan in kana abu dole ka nemi zaɓin Allah domin shi ne mai kowa mai komai, sannan Anas ba shi da wani aibu, yana da sana'ar sa, ba sata yake ba ko cutar wani, ga mahallin da zai aje ki , gaskiya a gani na ki amince da maganar auren nan, ko kin huta da rayuwar da kike fuskanta a yanzu." Inna ta ƙarashe maganar tana kallon Ayaman.
Shiru Ayaman ta yi tana nazarin maganganun inna, tabbas haka zancen yake in ta yi auren zata huta da rayuwar gidansu.
Nan Inna ta cigaba da bata shawarwari har ta kammala girkin suka ci tare sannan Ayaman ta yi ma ta sallama ta tafi.
Tana fita daga gidan aka kira sallar magriba, dan haka kanta a ƙasa ta fita daga gidan sakamakon mazan da ke wucewa domin shiga masallaci.
Wasu maza wanda aƙalla zasu yi sa'anin mahaifinta ne suka zo wucewa ta gaishe su, "yanzu ace malam Isyaku ya bar yarinya ta riƙa ta zama riƙaƙƙiyar kubewa, duk ta zama wata uwa a unguwa wannan ai bai dace ba." Ɗaya daga cikin mutanen ya faɗa, ɗayan kuma yace "Hmm, wa ya sa ni ko akwai abinda suka shirya shiyasa suka ƙi aurar da ita, koma dai mene muna nan muna zuba ido."
Wucewa ta yi ba tare da ta kalli ko inda suke ba duk da ta san da ita suke kuma taji me suke cewa.
Tana mamakin yadda mutane ke ma ta wata fahimtar daban, ita a ganinta aure ay lokaci ne kamar yadda mutuwa take .
Da sallama ta shiga gidan duk da ba kowa, ta tsaya a banɗaki ta yi alwala ta zo ɗaki ta dauko zanin da take sallah da shi.
A tsakar gida ta shimfiɗa ta yi sallar kasancewar akwai wutar lantarki dan sun ci sa'a an gyara musu.
Tana zaune a kan zanin har aka kira sallar Isha'i ta yi sallar ta.
Tana idarwa kam bayan ta gama zikiri ta shige ɗaki ta yi kwanciyar ta dan cikinta a koshe yake bata jin yunwa kuma tunda Ladiyo ta fita ta san sai sanda ta ga damar dawowa.
********************************
* Nafee(p.o.v)*
"Ke wallahi aikin mutumin nan yana ci, yau gashi da kansa yazo yake faɗa min zai yi magana da mamansa a kaina, kinsan mun daɗe muna fama da shi a fara maganar auren sai yau dai Allah ya yi." Nafee ta ƙarasa maganar cike da jin daɗi.
Ta ɗayan ɓangaren Lubna tace " ai ke kike wasa da tsafi, baki ji me bahaushe yace ba tsafi gaskiyar mai shi."
Hira suka cigaba da yi a kan yadda zasu shirya abubuwa dan Nafee ji take kamar an yi ma ta hajji da Umrah.
********************************
*Farouk(p.o.v)*
Yana isa office ya tarar da aiki ya yi mai yawa, dan mataimakin nasa bai yi abinda ya dace ba dan tafiyar da harkokin kamfanin.
Sai da ya gama mitar kuma ya fara aikin, har wurin la'asar yana abu ɗaya, sallah ce kawai ke tayar da shi.
Gidansa ya wuce bayan sallar la'asar.
A falo ya tarar da Ummu Kulsum tana turaren wuta, dan bata bari mai aiki ta yi ma ta.
Gaishe sa ta yi ya amsa ciki-ciki, dinning ya nufa ya bude kular abincin, masa da miyar taushe ya gani.
"Oh shit!!, wai me yake damun ki ne, jahilcin da baki gama ba a kauye shi zaki zo ki dasa min a gida? Mtcwwww."
Wullar da kular ya yi, sai ga waina ta yi ɗaiɗai a ƙasa, miyar ta biyo bayanta.
Fuuu ya wuce ɗakinsa kamar iska, kallon dinning ɗin Ummu Kulsum ta yi tana zama turuss a kan kujera.
Kuka ta fashe da shi mai ciwo, ita meye laifinta? Dan kawai daga ƙauye aka kawo ta shi ne ta yi jahilci? Ace kusan shekara ɗaya kana rayuwa da mutum amma baka taɓa samun farin ciki ba? Sai yaushe kenan?? Ta tambayi kanta cikin kuka.
A gaskiya ta fara gajiya da halin Farouk, ba zata ga murmushinsa ba sai in dare ne ya yi yana nemanta? "Na jure da yawa wallahi." Ummu Kulsum ta kuma faɗa tana kuka.
Mop da tsintsiya ta dauko ta gyara gurin dan Allah ya sa ta aiki ƴar aikinta wani wuri da tuni a gabanta zai yi wannan abin.
Bayan ta gama gyara gurin ta shige ɗakinta ta kullo ƙofa, tana tunanin raba ta da aka yi da masoyinta aka aura ma ta Farouk da sunan zumunci.
*Asalin su Farouk*
Love you all 💞💋 ❤️
More comment more typing ✍️
Khairat ✍️https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
*😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈*
By
*Khairat 💞💙*
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 27-28
*Asalin su Farouk*
Mahaifin Farouk Alhaji Aliyu Umar Datti ɗan asalin garin Katsina ne a kaita local government.
Ya taso cikin gata inda ya kasance shi kaɗai ne ɗan Fateema da Umar, dan shima sai da aka jima sannan aka haife sa.
Ya yi karatunsa na boko da Arabi a nan kaita inda ya tafi babbar University a lokacin wadda ita ce University of Lagos.
A nan makaranta ya hadu da Amina, har ta kai su da fara soyayya mai karfi, Amina ƴar asalin garin Lagos ce inda aka haife ta take.
Bayan kammala karatunsu ne Farouk ya gabatar da kansa a wurin iyayen ta har ta kai ga ya tura manya domin nemo mai auren Amina.
A lokacin an sha gumurzu kafin iyayen Amina su amince da auren dan sun so Amina ta auri wani ɗan uwanta.
An daura aure da kimanin sati biyu aka dauko Amina daga Lagos zuwa gidan Aliyu dake Katsina bayan nasihohi masu ratsa zuciya da iyayenta suka yi ma ta.
Watan Amina biyu a gidan Aliyu ta fara laulayi inda bayan cikin ya cika wata tara da ƴan kwanaki ta haifo santaleliyar ƴar ta mai kama da ubanta, aka raɗa ma ta suna Halima wanda sunan mahaifiyar Amina ne.
Halima taga gata iya gata a wurin iyayenta da kakkaninta kasancewar ta jikar farko a family ɗin.
Halima na da shekara biyar Amina ta kuma haifar ƴa mace wadda taci suna Raihana.
Bayan haihuwar Raihana ne suka koma garin Kano da zama saboda sauyin wurin aiki da Aliyu ya samu.
Amina sai da ta jima dan sai da Raihana ta kai shekara goma sannan ta haifo ɗa namiji wato Farouk.
Amina da Aliyu suka haɗa kam ƴaƴansu suka raina har suka kawo karfi, Halima ta yi aure da kwanaki kaɗan Allah ya amshi ran Aliyu sai gidansa na gaskiya.
A lokacin sunyi baƙin cikin rashin uban nasu amma suka yi tawakkali suka rumgumi ƙaddararsu.
A haka rayuwa ta cigaba da nisawa har Raihana ta kammala karatunta ta yi auri inda ta auri ɗan mataimakin shugaban kasa su na zaune a Abuja.
Lokaci zuwa lokaci Fateema tana kawo wa jikokinta ziyara, a wannan zuwa ta taho da wata budurwa wadda tace jikar aminiyar ta ce wacce mahaifiyar ta ta rasu tana da tarbiyya da hankali dan haka take son haɗa ta da Farouk.
A lokacin hauka ne kawai Farouk bai yi ba dan ya gama shirinsa zai auri Nafee sai ga Ummu Kulsum ta shigo.
Hajjo (Fateema) ta yi amfani da ƙarfin ikonta har aka ɗaura auren Farouk da Ummu Kulsum.
Tun daga lokacin Farouk yake ƙullace da Ummu Kulsum na ganin ta yadda an daura auren bayan jan kunnen da ya yi ma ta.
Tana zaune an lulluɓe ta da mayafi ta yi shiru tana tunanin wannan sabuwar rayuwar da zata shiga, kawai taji an ja ma ta mayafin aka cillar a ƙasa.
A yatsine yake kallon ta kamar ya ga wani abin ƙi, ya buɗe baki da kyar yace "Finally kin yadda an daura auren, har an kawo ki gidan nan, ya yi kyau..." Ya faɗa yana cilla ma ta kaza wadda bisa umurnin Ammi ya siya.
Ɗago kai ta yi ta ga yana ficewa daga ɗakin, "Ikon Allah." Ta faɗa a ranta.
Tashi ta yi tana kallon ɗakin, gaskiya iya tsaruwa ya tsaru amma dimm gabanta ya faɗi sanin ba wani zaman daɗi zata yi a gidan ba.
Haka ta yi ta hakuri da zama da Farouk, wata ranar ya dawo a bige ya neme ta ta ƙarfi, wata rana ya kawo matan banza har sai da abin ya dame ta ta gaya wa Ammi sannan ta tsawatar mai, shi ne ta ɗan samu sauƙin matan da yake kawo wa.
A haka har ta haifi Mu'ayyad, a haka kuma Farouk bai daina abin da yake ba sai dai ma ƙaruwa da yake.
Wannan kenan...
*Cigaban labari*
A karo na ba adadi Ummu Kulsum ta kuma fashe wa da wani kukan tuno rayuwar ta da ta yi a garin su, ga masoyinta da aka raba ta da shi ganin shi ba kowa bane .
Da ta gaji da kukan ta tashi ta ɗauro alwala a banɗaki ta yi nafila tana kai ƙaran Farouk wurin Allah.
********************************
*Ladiyo*
Tana nan har bayan sallar Isha'i a gidan Delu, sai wurin ƙarfe tara na dare sannan suka yi shirin zuwa wurin boka Barqaan.
A hankali suke hawa kan tsaunin gudun kar wata ta fado wani abu ya same ta.
Kamar yadda al'adar da kuma tsarin Barqaan yake, ba'a shigar mai kogo da kaya dole ka cire su , ka ajiye har sai ka fito.
Babu tsoro ko kunya su Ladiyo suka aikata abinda aka umarce su kafin suka shiga cikin kogon.
Boka Barqaan yana nan cikin kogon zaune cikin kazanta da ɗoyi wanda su Ladiyo basa ji sakamakon rufewa da idanunsu ya yi wurin neman taimako.