← Book details Masarautar Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 19

Sashe 9

Masarautar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 1 min read

EL-KANEMI COLLEGE OF ISLAMIC
THEOLOGY
Makarantar kwalejin kimiyya ce ta addinin muslunci wadda Larabawan Yemen dana Sudan suka bude a Maiduguri da hadin gwiwar manyan masu kudin jihar Borno. Itace makarantar da sarki Yusufu ke kai 'ya'yan sa maza da mata, tun daga kan babbar 'yar sa (Ya Maira) sunan sarautar ta kenan a matsayin ta na babbar 'ya, har zuwa kan auta Humairah.
A tsarin makarantar daga Lahadi zuwa Alhamis sune renakun karatu, Juma'ah da Asabar renakun hutu.
Malamin maths na fita na Qur'an na shiga, na English na fita na Nahawu ko Fiqh zai shiga, na chemistry na fita na Adab ko Tarikh ko Mutala'a zai shiga haka dai tsarin karantarwar su yake. Wato kimiyya cakude da ilmin addini tsantsa.
Sannan ana gama lessons karfe uku ake fara Islamiyya ga mai son haddan Qur'an zalla ake yi har zuwa biyar na yamma.
Malaman makarantar kuma yawanci larabawan Sudan da Yemen ne, sai kuma Yarabawa
Maza da mata basa haduwa sam, dan katanga ce makekiya a tsakanin su sannan kowane bangare da gate din shi.
Chapter 9 · 0% Book details