Sashe 5
Masarautar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sarki Yusufu ya kama hannun Sa'ade ya sanya cikin nata. Expression na fuskarta kadai ya gaya masa duk abinda Baba Saleh ya fada gaskiya ne.
"Jeki ga mahaifiyar ki Sa'adatu, ki ji dumin jikin ta, kamar yadda kowanne da yake jin dumin jikin uwar sa".
Sa'ade ta kasa yin hakan, ganin yadda matar ta cire hannu daga fuskar ta ta bubbude mata ido, kamr tana gargadin ta da yin hakan. Ta dubi Baba Saleh da kakkausar murya tace.
"Kai dan aiken Hashimu! Ka koma ka gaya masa yadda Bilkisu bata taba son sa ba, haka bata son abinda ya fito daga jikin sa, bana bukatar 'yar sa ya cigaba da rikon abar sa shi kadai".
Sa'ade ta fashe da kuka, Baba Saleh kuma ya sunkuyar da kai. Sarki Yusufu ya daga ido cikin firgici ya dube ta, anya Bilkisun sa ce wannan? Wadda ko barorin ta bata dagawa murya tsakanin ta da kowa kyautayi ne da mutuntawa? Balle dan da ta haifa? Dan da kullum take adduar Allah ya bar mata ko guda daya?
"Ko da Hashimun ya mutu bazaki rike 'yar da kika haifa ba?"
Muryar sarki akwai fushi da fusata mai tsanani a cikin ta a lokacin da ya jefe ta da wannan kalami, mikewa tayi tana shirin barin falon ko kadan zuciyar ta bata russuna ba, "idan ya mutu yana da dan uwa a garin Damaturu, a kai ta can ya rike masa". Har ta kai bakin kofa sarki ya kira ta da kakkausar murya...
"FULANI BILKISU!"
Ta dakata, amma ba tare da ta juyo ba.
"Zo ki kama hannun 'yar ki ki tafi da ita sassan ki, ki bata duk kulawar da uwa zata baiwa danta, tana karkashin amana ta, zamana zata yi a gidannan daga nan har karshen rayuwar ta, a bisa kulawa da kiyayewa ta".
Yana fadin hakan ya mike tsaye, ya dubi Sa'ade da ke kuka wurjanjan, "daina kuka Sa'adatu, mahaifiyar ki ce bazata cutar da ke ba, dauki kayan ki ki bi bayan ta". Sa'ade ta share hawayen ta da bayan hannun ta, ita in aka ce wannan galleliyar matar mahaifiyar ta ce ma wani iri take ji, tsigar jikin ta har tashi take, tsoron ta take ji sosai, gata da manyan ido da wani irin kwarjini, ita gara ta bi Baba Sale su koma Tsanyawa, abinda ta fada cikin kuka kenan, amma Baba Saleh ya girgiza mata kai ya ce.
"Bi ta Sa'ade, kiyi mata biyayya a bisa dukkan umarnin ta, aljannar ki na tare da ita".
Ta dauki tsummokaranta tana waiwayen Baba Saleh, shikuma yana yi mata murmushi, tuni Fulani Bilkisu ta fice, kuyangin ta sun mara mata baya, sai da ta hada da gudu-gudu ta cimmasu, Sarki Yusufu yace da Baba Saleh za'azo a kai shi masauki ya huta har zuwa iya kwanakin da ya ke so, sannan zai sa a maida shi har Tsanyawa a motar gida, zai bada sallama a bashi, Allah ya kai shi gida lafiya, yana yi masa fatan hutu mai dadi cikin masarautar sa.
Baba Saleh ya zube yayi ta godiya, a take dogarawa suka kai shi masaukin bakin sarki, aka wadata shi da abinciccika da ababen sha na alfarma, sittiru da duk abinda zai bukata. Amma duk wannan bai dame shi ba, tunanin sa na ga halin da Sa'ade zata kasance a hannun mahaifiyar ta.
Wadda ta nuna a fili bata bukatar ta cikin rayuwar ta.
Bai san laifin da Malam Hashimu yayi mata ba, amma ya lura kiyayyarsa ce ta shafi 'yar sa.
Abu daya yake da yakini yake kuma dan kwantar masa da hankali idan ya tuna ita ta haifeta da gaske, duk kin ta da ita bazata cutar da ita ba, sai dai ta kasa nuna mata soyayya.
Yana tausayin Sa'ade sabida bata taba dandana kaunar UWA ba, bata taba jin dumin uwa ba, ga wahalar data sha hannun Laure, sannan yanzu ga ta ga uwar amma bata kaunar ta.
Zuciyar sa tayi maza ta ce masa "ba ita ce bata so ba uban ta ne bata so, da sannu in sun zauna tare Allah zai musanya zuciyar ta zuwa alkhairi akan 'yar ta"..
Da kyar ya samu ya runtsa a wannan dare sabida tunanin Sa'ade, hutun da aka ce ya zauna yayi ya ga bazai iya ba, washegari ya gayawa mai kula da shi ya gayawa maimartaba yau zai koma garin su. Sarki yasa aka yi masa goma ta arziki, aka cika masa bayan mota hilux, sannan ya damka mishi kyautar kudi da sittiru masu yawa.
Suka kama hanyar zuwa Tsanyawa a mota hilux zuciyar Baba Saleh cike da alhini na tausayin Sa'ade.
****
Sa'ade na bin kuyangin Fulani a baya, fada nan fada can har suka dangana da wani babban gini, kamar gida guda bangare guda haka, aka bude kofar Fulani ta sanya kafar ta kamar wata Dawisu sabida yadda take taku su kuma suna biye da ita, kyawu da kayatuwar ginin yasa Sa'ade sakin baki da hanci tana kallo, har tana tuntube saura kadan ta fadi.
Manyan faluka suka rika wucewa har suka tadda wanda daga shi kuyangin suke da shamaki, sai guda daya daga cikin su ce ta bi bayan Fulani, bata jima ba ta fito tace da Sa'ade wadda ta tsaya a inda ta ga kowa ya tsaya itama, ta biyo ta ta kai ta dakin da zata zauna.
Inda Fulanin ta shiga nan ta ga sun shiga, wani (english parlour) ne komai fari sol har labulaye da kujeru, kilishin falon ne kawai launin makuba shima da adon fari da baki a jiki, kofofi ne wajen guda hudu a falon bata san a wanne Fulani ke ciki ba, kuyangar ta bude daki daya suka shiga. Sa'ade ji tayi numfashin ta ya tsaya a wuyanta sabida kyawun dakin da tsaruwar sa, komai dake cikin dakin kalar blue and light pink ne, ga wani shimfidadden gado na sarauta (royal bed) da ya ji shimfidu na alfarma.
Kuyangar ta shiga bandaki ta hada mata ruwan wanka, tazo ta kama hannnun ta ta kaita har gaban kwamin wankan, ta nuna mata yadda ake amfani da komai don ba sai da bayani ba kallo daya za'ayi wa Sa'ade a fahimci bata taba alaqa da irin wannan muhallin ba a rayuwar ta. Ta kasa boye firgici da razanar data ke ciki.
Kuyangar tace zata cuda mata baya. Sa'ade ta zaro ido tace "bana so". Ta fita ta barta bayan ta tattare tsummokaran data tube ta hada da kullin kayan ta ta fita dasu ta zubar kamar yadda Fulani ta bata umarni.
Kafin Sa'ade ta fito ta ajiye mata dogayen riguna daidai tsayin ta guda biyu a gefen gado, sannan ta shigo mata da abinci lafiyayye kala kala akan tray. Ta zauna har ta fito daga wankan daure da tawul din data nuna mata sannan ta gaya mata nan ne dakin ta, ba koyaushe zata ga Fulani ba, in tana son ganin ta zata nemeta da kanta, ba'a yarda taje ko'ina bayan dakin nan ba, duk abinda take so ita kuyangar zata dinga shigowa tana yi mata, ta gaya mata cewa itace amintacciyar Fulani, kuma ita kadai ke shigowa wannan sashen, sunan ta "Fanna".
Sa'ade ta gyada mata kai alamar ta gane, sannan ta ce da ita "ga hijab nan da darduma kiyi sallah".
Bayan fitar Fanna Sa'ade zama tayi a bakin gadon a dofane tana ta kallon dakin, sai ta ji duk alatun dake cikin sa bai burgeta ba, ta ji duniya tayi mata kunci, kewar Baban ta mai son ta, ta zo ta lullube ta. Soyayyarsa ta fi mata duka wannan alatun da babu soyayya a cikin sa sai kiyayya zallah.
Amma duk da wannan damuwar dake cin ranta, ba abinda zuciyar ta ke hango mata sai fuskar Fulani Bilkisu ma'abociyar zati da kamala, da wani irin feelings mai fizgar zuciya tamkar maganadisu (maternal love). Wata irin soyayya da bata taba ji akan kowa a duniya ba bayan Babanta, wannan soyayyar har ta zarta wadda take ji akan Baban ta. Shine abinda ta ke ji akan Fulani Bilkisu!
Ta lumshe ido tana hasaso yadda ta zazzaro mata ido kada ta zo kusa da ita, a kuruciyar Sa'ade ba don komai bane sai don ita 'yar kauye ce. Tana kyankyamin ta ne kawai. Tasa a ranta daga yau kullum zata dinga wanka, don Fulani ta daina tsantsamin ta.
Ta mike ta sanya hijab ta tada birkitacciyar sallarta, wadda ko kadan ba daidai take yin ta ba, sannan babu wani karatun sallah na azo a gani, karewa ma "BA-SIM-MI'ARA" take karantawa a cikin sallahr.
Data idar da azahar da la'asar sai ta ja farantin abincin da Fanna ta ajiye mata, ta ci iya cinta kunnenta kamar ya gutsure don dadin naman tolo-tolo, data gama ta je ta wanke hannu ta dawo ta kwanta a gadon da tun dazu take son ta ji yaya yake? Wane irin laushi gareshi haka da tun dazu ya ke fizgar idanun ta? Wani barawon barci yazo yayi awon gaba da ita, sau biyu Fanna tana shigowa, ta fidda farantin ta kunna mata iyakwandishan wanda ni'imar ta ya kara armasa mata barcin.
****
Sai safah da marwa take a dakin barcinta, ta kasa barci, ta rasa abinda ke mata dadi. It's very unusual maimartaba ya shigo sassan matan sa. Amma yau sai kawai ta ganshi ya shigo har dakin barcin nata, ba zaton ta ba tsammani.
"Zuwa nayi ki gaya min abinda matsayi na bai kai na sani ba, wanda ya faru cikin rayuwar ki ta baya".
Ya fada yana mai zama a gefen hamshakin gadon ta.
"Jeki ga mahaifiyar ki Sa'adatu, ki ji dumin jikin ta, kamar yadda kowanne da yake jin dumin jikin uwar sa".
Sa'ade ta kasa yin hakan, ganin yadda matar ta cire hannu daga fuskar ta ta bubbude mata ido, kamr tana gargadin ta da yin hakan. Ta dubi Baba Saleh da kakkausar murya tace.
"Kai dan aiken Hashimu! Ka koma ka gaya masa yadda Bilkisu bata taba son sa ba, haka bata son abinda ya fito daga jikin sa, bana bukatar 'yar sa ya cigaba da rikon abar sa shi kadai".
Sa'ade ta fashe da kuka, Baba Saleh kuma ya sunkuyar da kai. Sarki Yusufu ya daga ido cikin firgici ya dube ta, anya Bilkisun sa ce wannan? Wadda ko barorin ta bata dagawa murya tsakanin ta da kowa kyautayi ne da mutuntawa? Balle dan da ta haifa? Dan da kullum take adduar Allah ya bar mata ko guda daya?
"Ko da Hashimun ya mutu bazaki rike 'yar da kika haifa ba?"
Muryar sarki akwai fushi da fusata mai tsanani a cikin ta a lokacin da ya jefe ta da wannan kalami, mikewa tayi tana shirin barin falon ko kadan zuciyar ta bata russuna ba, "idan ya mutu yana da dan uwa a garin Damaturu, a kai ta can ya rike masa". Har ta kai bakin kofa sarki ya kira ta da kakkausar murya...
"FULANI BILKISU!"
Ta dakata, amma ba tare da ta juyo ba.
"Zo ki kama hannun 'yar ki ki tafi da ita sassan ki, ki bata duk kulawar da uwa zata baiwa danta, tana karkashin amana ta, zamana zata yi a gidannan daga nan har karshen rayuwar ta, a bisa kulawa da kiyayewa ta".
Yana fadin hakan ya mike tsaye, ya dubi Sa'ade da ke kuka wurjanjan, "daina kuka Sa'adatu, mahaifiyar ki ce bazata cutar da ke ba, dauki kayan ki ki bi bayan ta". Sa'ade ta share hawayen ta da bayan hannun ta, ita in aka ce wannan galleliyar matar mahaifiyar ta ce ma wani iri take ji, tsigar jikin ta har tashi take, tsoron ta take ji sosai, gata da manyan ido da wani irin kwarjini, ita gara ta bi Baba Sale su koma Tsanyawa, abinda ta fada cikin kuka kenan, amma Baba Saleh ya girgiza mata kai ya ce.
"Bi ta Sa'ade, kiyi mata biyayya a bisa dukkan umarnin ta, aljannar ki na tare da ita".
Ta dauki tsummokaranta tana waiwayen Baba Saleh, shikuma yana yi mata murmushi, tuni Fulani Bilkisu ta fice, kuyangin ta sun mara mata baya, sai da ta hada da gudu-gudu ta cimmasu, Sarki Yusufu yace da Baba Saleh za'azo a kai shi masauki ya huta har zuwa iya kwanakin da ya ke so, sannan zai sa a maida shi har Tsanyawa a motar gida, zai bada sallama a bashi, Allah ya kai shi gida lafiya, yana yi masa fatan hutu mai dadi cikin masarautar sa.
Baba Saleh ya zube yayi ta godiya, a take dogarawa suka kai shi masaukin bakin sarki, aka wadata shi da abinciccika da ababen sha na alfarma, sittiru da duk abinda zai bukata. Amma duk wannan bai dame shi ba, tunanin sa na ga halin da Sa'ade zata kasance a hannun mahaifiyar ta.
Wadda ta nuna a fili bata bukatar ta cikin rayuwar ta.
Bai san laifin da Malam Hashimu yayi mata ba, amma ya lura kiyayyarsa ce ta shafi 'yar sa.
Abu daya yake da yakini yake kuma dan kwantar masa da hankali idan ya tuna ita ta haifeta da gaske, duk kin ta da ita bazata cutar da ita ba, sai dai ta kasa nuna mata soyayya.
Yana tausayin Sa'ade sabida bata taba dandana kaunar UWA ba, bata taba jin dumin uwa ba, ga wahalar data sha hannun Laure, sannan yanzu ga ta ga uwar amma bata kaunar ta.
Zuciyar sa tayi maza ta ce masa "ba ita ce bata so ba uban ta ne bata so, da sannu in sun zauna tare Allah zai musanya zuciyar ta zuwa alkhairi akan 'yar ta"..
Da kyar ya samu ya runtsa a wannan dare sabida tunanin Sa'ade, hutun da aka ce ya zauna yayi ya ga bazai iya ba, washegari ya gayawa mai kula da shi ya gayawa maimartaba yau zai koma garin su. Sarki yasa aka yi masa goma ta arziki, aka cika masa bayan mota hilux, sannan ya damka mishi kyautar kudi da sittiru masu yawa.
Suka kama hanyar zuwa Tsanyawa a mota hilux zuciyar Baba Saleh cike da alhini na tausayin Sa'ade.
****
Sa'ade na bin kuyangin Fulani a baya, fada nan fada can har suka dangana da wani babban gini, kamar gida guda bangare guda haka, aka bude kofar Fulani ta sanya kafar ta kamar wata Dawisu sabida yadda take taku su kuma suna biye da ita, kyawu da kayatuwar ginin yasa Sa'ade sakin baki da hanci tana kallo, har tana tuntube saura kadan ta fadi.
Manyan faluka suka rika wucewa har suka tadda wanda daga shi kuyangin suke da shamaki, sai guda daya daga cikin su ce ta bi bayan Fulani, bata jima ba ta fito tace da Sa'ade wadda ta tsaya a inda ta ga kowa ya tsaya itama, ta biyo ta ta kai ta dakin da zata zauna.
Inda Fulanin ta shiga nan ta ga sun shiga, wani (english parlour) ne komai fari sol har labulaye da kujeru, kilishin falon ne kawai launin makuba shima da adon fari da baki a jiki, kofofi ne wajen guda hudu a falon bata san a wanne Fulani ke ciki ba, kuyangar ta bude daki daya suka shiga. Sa'ade ji tayi numfashin ta ya tsaya a wuyanta sabida kyawun dakin da tsaruwar sa, komai dake cikin dakin kalar blue and light pink ne, ga wani shimfidadden gado na sarauta (royal bed) da ya ji shimfidu na alfarma.
Kuyangar ta shiga bandaki ta hada mata ruwan wanka, tazo ta kama hannnun ta ta kaita har gaban kwamin wankan, ta nuna mata yadda ake amfani da komai don ba sai da bayani ba kallo daya za'ayi wa Sa'ade a fahimci bata taba alaqa da irin wannan muhallin ba a rayuwar ta. Ta kasa boye firgici da razanar data ke ciki.
Kuyangar tace zata cuda mata baya. Sa'ade ta zaro ido tace "bana so". Ta fita ta barta bayan ta tattare tsummokaran data tube ta hada da kullin kayan ta ta fita dasu ta zubar kamar yadda Fulani ta bata umarni.
Kafin Sa'ade ta fito ta ajiye mata dogayen riguna daidai tsayin ta guda biyu a gefen gado, sannan ta shigo mata da abinci lafiyayye kala kala akan tray. Ta zauna har ta fito daga wankan daure da tawul din data nuna mata sannan ta gaya mata nan ne dakin ta, ba koyaushe zata ga Fulani ba, in tana son ganin ta zata nemeta da kanta, ba'a yarda taje ko'ina bayan dakin nan ba, duk abinda take so ita kuyangar zata dinga shigowa tana yi mata, ta gaya mata cewa itace amintacciyar Fulani, kuma ita kadai ke shigowa wannan sashen, sunan ta "Fanna".
Sa'ade ta gyada mata kai alamar ta gane, sannan ta ce da ita "ga hijab nan da darduma kiyi sallah".
Bayan fitar Fanna Sa'ade zama tayi a bakin gadon a dofane tana ta kallon dakin, sai ta ji duk alatun dake cikin sa bai burgeta ba, ta ji duniya tayi mata kunci, kewar Baban ta mai son ta, ta zo ta lullube ta. Soyayyarsa ta fi mata duka wannan alatun da babu soyayya a cikin sa sai kiyayya zallah.
Amma duk da wannan damuwar dake cin ranta, ba abinda zuciyar ta ke hango mata sai fuskar Fulani Bilkisu ma'abociyar zati da kamala, da wani irin feelings mai fizgar zuciya tamkar maganadisu (maternal love). Wata irin soyayya da bata taba ji akan kowa a duniya ba bayan Babanta, wannan soyayyar har ta zarta wadda take ji akan Baban ta. Shine abinda ta ke ji akan Fulani Bilkisu!
Ta lumshe ido tana hasaso yadda ta zazzaro mata ido kada ta zo kusa da ita, a kuruciyar Sa'ade ba don komai bane sai don ita 'yar kauye ce. Tana kyankyamin ta ne kawai. Tasa a ranta daga yau kullum zata dinga wanka, don Fulani ta daina tsantsamin ta.
Ta mike ta sanya hijab ta tada birkitacciyar sallarta, wadda ko kadan ba daidai take yin ta ba, sannan babu wani karatun sallah na azo a gani, karewa ma "BA-SIM-MI'ARA" take karantawa a cikin sallahr.
Data idar da azahar da la'asar sai ta ja farantin abincin da Fanna ta ajiye mata, ta ci iya cinta kunnenta kamar ya gutsure don dadin naman tolo-tolo, data gama ta je ta wanke hannu ta dawo ta kwanta a gadon da tun dazu take son ta ji yaya yake? Wane irin laushi gareshi haka da tun dazu ya ke fizgar idanun ta? Wani barawon barci yazo yayi awon gaba da ita, sau biyu Fanna tana shigowa, ta fidda farantin ta kunna mata iyakwandishan wanda ni'imar ta ya kara armasa mata barcin.
****
Sai safah da marwa take a dakin barcinta, ta kasa barci, ta rasa abinda ke mata dadi. It's very unusual maimartaba ya shigo sassan matan sa. Amma yau sai kawai ta ganshi ya shigo har dakin barcin nata, ba zaton ta ba tsammani.
"Zuwa nayi ki gaya min abinda matsayi na bai kai na sani ba, wanda ya faru cikin rayuwar ki ta baya".
Ya fada yana mai zama a gefen hamshakin gadon ta.