Sashe 16
Masarautar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kafin ya zama sarki shi Ambasada ne na kasar Egypt, saida mahaifinsa Sarki Abdulhakim ya rasu ne aka dawo dashi gida aka bashi sarauta, don haka yana da kyakkyawar alaqa da ambasadan Egypt mai ci a lokacin kamar amini yake a gare shi, sannan yana da connections mai yawa da kasar ta Misra domin yayi sama da shekaru goma yana aikin jakada a cikin ta.
Don haka ya yanke shawarar kai shi kasar muslunci bai kai shi kasar turai ba don ya kara hankali, a Egypt din ma hannun Aminin sa Amb. Hassan Labaran ya damka shi bai yarda ya zauna a hostel ba. Amb. Hasan bai taba haihuwa ba shida matarsa Hajiya Laila, suka karbi amanar Sageer da Awaisu a gidan su wadanda aka samarwa gurbi a jami'ar Al. Azhar. Saidai ba fanni daya suke karanta ba.
Daga wannan lokacin ne kuma haihuwar 'ya'ya maza ta budewa Sarki Yusufu daga duka matan nashi biyu, a lokacin ne ya hadu da Hibbani ya aure ta, daga baya ya auri Bilkisu, haihuwar ta biyar suna mutuwa.
Amb. Hassan zazzafan da boko ne mai zafi da sanya ido akan iyalin sa, tashin farko ya gano dabi'ar da Sageer ya zo masa gida da ita ta shan sigari, kuma ba jimawa yayi fata-fata da ita, ya cigaba da dora shi a hanya ta hanyar tsawatarwa da jan sa a jiki, yana nuna masa illar smoking ga lafiyar sa ta dan adam. Wani abu da bai samu daga iyayen sa ba sabida kawaici na masu sarauta ga 'ya'yan su. Gara ma Maimartaba akan Ya Gumsu wadda babu wani kusanci ko kankani tsakanin ta da dan nata, bata san me yake ciki ba, bata taba bincikar halayyar sa ba, ita dai burin ta ya kasance cikin gata ya samu duk abinda yake so, ya girma ya gaje sarauta.
Cikin dan lokaci kankani Amb. Hassan ya canza da yawa daga baragurbin halayen Sageer sai abinda ba'a rasa ba. Shima Awaisu a nasa bangaren yana iya nasa kokarin wurin ganin Sageer ya canza munanan dabi'un sa zuwa na cikakken dalibin da ya san ciwon kansa.
A karshe Awaisu ya fahimci wani abu, zai iya nasarar raba Sageer da komai, amma ba zai iya raba shi da 'yammata ba.
Mahaukatan kudin da sarki ke turo masa don yayi hidimar karatu, da wadanda Amb. Ke basu lokaci-lokaci duk a hidimar 'yammatan sa yake karar dasu. Yana kuma da masaniyar cewa yana branching da 'yammata a hotel ba da sanin Amb. Hassan ba.
Al'amarin ya kara kazanta ne lokacin da aka yiwa Amb. Hassan sauyin kasa, daga Egypt zuwa Amsterdam akan aikin jakadancin sa. Suka tattara suka bar Egypt suka koma can. Inda suka fara karatun doctorate degree dinsu a fannin da kowanne yake a babbar jami'ar Amsterdam. Awaisu na karantar (Social Work) yayinda Sageer ke karantar (Pure and Applied Chemistry).
A duka wadannan shekarun bai kara ganin kowa nasa ba, wadanda aka haifa baya nan bai san su ba. Haka wadda aka aura a bayan sa wato Fulani Bilkisu. Bayan su akwai kwarkwarori da yawa. Sannan elder sisters dinsa biyu duk sunyi aure sun hayayyafa: Ya Maira da Mairam Murjanatu. Bayan su an haifi maza biyar, biyu Ya Gumsu, uku Ya Kirjinoma, sannan Hibbani na da Humaira da Najaatu. Bayan kammala M. Sc din su dukkan su sun samu aiki a kasar Amsterdam, Awaisu aikin asibiti yake yi yayin da Yarima Sageer ke aiki da wani mashahurin kamfanin sarrafa kayan abincin gongoni na kasar.
Tuni sun manta daga gidan sarauta suka fito, sun karbi rayuwar gidan Amb. Hassan wanda bazaka taba sanin ba shi ya haife su ba. Rayuwar kasar Amstedam ta karbe su sosai, sun tara arziki nasu na kansu, ga aiki ga muhalli ga ababen hawa. Amma duk da haka a gidan Amb. Suke zaune.
Tun barin sa gida sai a shekarar baya ne maimartaba da Ya Gumsu suka kai masa ziyara, bisa tsananin rokon Amb. Hassan don maimartaba yace shi har abada Sageer bazai dawo masa gida ba, ya barwa Amb. Hassan shi duniya da lahira sabida gamsuwa da irin rikon da yake musu shi da Awaisu, shi kansa Waziri bai taba bada shawarar su dawo gida ba.
Sai kuma ga abinda Ya Gumsu ta zo da shi yau, na nema masa alfarmar zuwa gida yayi ko sati daya ne.
Ya sake lumshe idon sa ya bude a hankali. A fili ya furta "nima ina kewar ka Muhammad Sageer, tsoron abinda zai je ya zo nake. Ina tattalin mutuncin ka a idon al'ummarka. Duk da Baban ka ya tabbatar min baka da matsala yanzu".
****
A shawarar da suka yi da Waziri ya karfafe shi akan ya bar Yarima ya zo gida, koda sati dayan ne, tunda dai bazai dawwama a kasar da ba tasa ba, dole watarana zai zo gida, sannan Amb. Hassan ya tabbatar musu komai lafiya a tareda Yarima. Awaisu ne dai da yafi kowa kusanci da shi ya ce da Babansa Waziri da saura. Wazirin kuma bai gayawa sarki hakan ba don ya samu nutsuwar barin dan sa ya shiga cikin 'yan uwan sa ko yaya ne. A gefe ya saka limamin Askira da sauran malaman fada yin addu'a ta musamman akan zuwan Yarima Sageer, Allah ya kintsawa mahafin sa shi a matsayin sa na magajin sa.
Da wannan sarki ya yiwa Yarima umarnin zuwa gida don yayi sati daya. A wannan lokacin Amb. Hassan ya gama tenure dinsa na aikin jakadanci yana shirin dawowa gida gabadaya, don haka tare suka soma shirin tahowa shi da 'ya'yan nasa Sageer da Awaisu, inda Amb. Hassan zai sauka a kasar shi ta haihuwa Kanon Dabo, kafun ya koma Birnin Tarayya da zama.
*****
"Na ga sai wani zumudi kake zaka je gida, kamar wani special abu ne zamu je mu taras banda zafin Maiduguri, ni banda Ya Gumsu ta dage sai naje ai har abada na bar Askira kenan, tunda Alanguburo baya son gani na".
Awaisu yayi murmushi yana ninke kayan Yarima yana jera masa cikin tsadaddiyar trolley din sa. Bai yi niyyar bashi amsa ba sai da ya ji Yarima ya sake yin kwafa, "ni ko satin ma bazan cika ba zan dawo, ka san nextweek akwai birthday din da na hadawa (Rose), kawai sai jin zancen tafiyar nan na yi, da na san da ita da tun satin da ya wuce mun yi mun gama, she will be 26 by next week". (Rose, yarinyar Yarima ce da yake ji da ita, 'yar asalin kasar Korea ta kudu), Awaisu ya tamke fuska kamar bai ji shi ba, ya cigaba da jera masa kaya. Daga baya kuma ya ce "ayya! Ai kawai ka tafi da ita Askira ka hada mata birthday din acan zai fi bada ma'ana" Yarima yayi miskilin murmushin sa, ya ce "me kake ci na baka na zuba? Ka zuba ido zuwa shekaru biyu zan kaita Askiran ne, amma a matsayin matata ba budurwa ta ba".
Awaisu ya dauka ya fada ne kawai don ya ji dadin bakin sa, ya manta da wani hali na Yarima Sageer Yusuf Askira, duk abinda ya furta yana nufin sa ne har zuciyar sa. Amma akan zancen Rose bayahudiya bai taba kawowa Yarima da gaske aurenta yake da niyyar yi ba.
A halayen Yarima in ka dauke son matan sa, sauran duka ababen sha'awa ne, Awaisu ba zai daina kiran sa (his role model) ba. Mutum ne mai muhimmanta sallah da kiyaye lokutanta, mai kirki mai kyauta, abun hannun sa bai taba rufe mai ido ba. Ga jin kan na kasa da shi, ga girmama iyaye, sannan ga kokari wajen neman na kai kamar ba dan sarki ba.
Bayan kamfanin da yake yiwa aiki yana kasuwancin automobile daga Amurka zuwa Amsterdam. Duk da haka maimartaba bai taba fasa turo masa kudi duk karshen wata ba, shi Awaisun shine akan komai na kasuwancin nasa kuma kyautatawar da Yarima yake masa a ciki sai ka rantse su biyu suka mallaki jarin kasuwancin.
Babban abunda ke burge Awaisu a halayen Yarima Sageer shine submissiveness, ya san shi mai laifi ne a gurin Ubangiji, amma yana yawan ce da Awaisu ya kasa dainawa, kuma yana so ya daina din, mata sun zame masa barin rayuwa da baya iya rayuwa daidai sai tare da su, don haka kullum cikin istigfari yake yana fadin yana rokon Allah yasa kada ya mutu yana aikata laifin da yake aikatawa.
Ko Awaisu ya soma wa'azi, baya arguing da shi, cewa ya ke ya sani babu kyau ya taya shi addu'a. Sai Awaisu ya koma yi masa yakin karkashin kasa, don kuwa yarima tausayi yake bashi, kana sabo ka san kana yi amma ka ce ba zaka iya dainawa ba, duk yarinyar da ya gani tare da shi zai bi ta bayan idon sa ya ci mutuncin ta ya razanata akan tarayya da Sageer, wani zubin har ya ce Sageer nada cuta, ga turawa da shegen tsoro, saidai Sageer ya nemi yarinyar sa sama ko kasa ya rasa, a karshe saidai ya nemo wata, shi kuma Awaisu baya gajiya da lalatawa, kamar yadda shima baya gajiya da sake nemowa.
Wannan itace rayuwar Yarima Sageer da dan uwan sa Awaisu a kasar Amsterdam. Tamkar ciki daya suka fito, sha'awar su akan komai daya ce ra'ayin su daya, sannan zuciyar su tsayayya ce akan junan su, saidai hali kowa nasa daban.
Jirgin su ya sauka a filin jirgin saman Maiduguri da asubahin safiyar Litinin, zaratan matasan suka soma saukowa daga matattakalar jirgin 'AZMAN' cikin shiga ta barebarin usli, wadanda fatar jikin su ta jiku da boko da kasar sanyi, kai da ganin su ka san sun fito ne daga sarauta ta ainahi ko daga irin takun su da kasaitar su.
Suna sauka motar 'Askira Emirate' na jiran su. Tun a Abuja suka rabu da Amb. Hassan da Mama Laila wadanda suka hau jirgin Kano, su kuma suka hawo na Maiduguri.
Dogarawa bila- adadin duk daga motocin masarautar Askira, suka bude musu kofar motar BMW wadda maimartaba kadai ke hawan ta a gidan. Daga nan basu bata lokaci ba suka kama hanyar Askira da motar civilian mai dauke da wasu fadawan cike fal a cikin ta.
Don haka ya yanke shawarar kai shi kasar muslunci bai kai shi kasar turai ba don ya kara hankali, a Egypt din ma hannun Aminin sa Amb. Hassan Labaran ya damka shi bai yarda ya zauna a hostel ba. Amb. Hasan bai taba haihuwa ba shida matarsa Hajiya Laila, suka karbi amanar Sageer da Awaisu a gidan su wadanda aka samarwa gurbi a jami'ar Al. Azhar. Saidai ba fanni daya suke karanta ba.
Daga wannan lokacin ne kuma haihuwar 'ya'ya maza ta budewa Sarki Yusufu daga duka matan nashi biyu, a lokacin ne ya hadu da Hibbani ya aure ta, daga baya ya auri Bilkisu, haihuwar ta biyar suna mutuwa.
Amb. Hassan zazzafan da boko ne mai zafi da sanya ido akan iyalin sa, tashin farko ya gano dabi'ar da Sageer ya zo masa gida da ita ta shan sigari, kuma ba jimawa yayi fata-fata da ita, ya cigaba da dora shi a hanya ta hanyar tsawatarwa da jan sa a jiki, yana nuna masa illar smoking ga lafiyar sa ta dan adam. Wani abu da bai samu daga iyayen sa ba sabida kawaici na masu sarauta ga 'ya'yan su. Gara ma Maimartaba akan Ya Gumsu wadda babu wani kusanci ko kankani tsakanin ta da dan nata, bata san me yake ciki ba, bata taba bincikar halayyar sa ba, ita dai burin ta ya kasance cikin gata ya samu duk abinda yake so, ya girma ya gaje sarauta.
Cikin dan lokaci kankani Amb. Hassan ya canza da yawa daga baragurbin halayen Sageer sai abinda ba'a rasa ba. Shima Awaisu a nasa bangaren yana iya nasa kokarin wurin ganin Sageer ya canza munanan dabi'un sa zuwa na cikakken dalibin da ya san ciwon kansa.
A karshe Awaisu ya fahimci wani abu, zai iya nasarar raba Sageer da komai, amma ba zai iya raba shi da 'yammata ba.
Mahaukatan kudin da sarki ke turo masa don yayi hidimar karatu, da wadanda Amb. Ke basu lokaci-lokaci duk a hidimar 'yammatan sa yake karar dasu. Yana kuma da masaniyar cewa yana branching da 'yammata a hotel ba da sanin Amb. Hassan ba.
Al'amarin ya kara kazanta ne lokacin da aka yiwa Amb. Hassan sauyin kasa, daga Egypt zuwa Amsterdam akan aikin jakadancin sa. Suka tattara suka bar Egypt suka koma can. Inda suka fara karatun doctorate degree dinsu a fannin da kowanne yake a babbar jami'ar Amsterdam. Awaisu na karantar (Social Work) yayinda Sageer ke karantar (Pure and Applied Chemistry).
A duka wadannan shekarun bai kara ganin kowa nasa ba, wadanda aka haifa baya nan bai san su ba. Haka wadda aka aura a bayan sa wato Fulani Bilkisu. Bayan su akwai kwarkwarori da yawa. Sannan elder sisters dinsa biyu duk sunyi aure sun hayayyafa: Ya Maira da Mairam Murjanatu. Bayan su an haifi maza biyar, biyu Ya Gumsu, uku Ya Kirjinoma, sannan Hibbani na da Humaira da Najaatu. Bayan kammala M. Sc din su dukkan su sun samu aiki a kasar Amsterdam, Awaisu aikin asibiti yake yi yayin da Yarima Sageer ke aiki da wani mashahurin kamfanin sarrafa kayan abincin gongoni na kasar.
Tuni sun manta daga gidan sarauta suka fito, sun karbi rayuwar gidan Amb. Hassan wanda bazaka taba sanin ba shi ya haife su ba. Rayuwar kasar Amstedam ta karbe su sosai, sun tara arziki nasu na kansu, ga aiki ga muhalli ga ababen hawa. Amma duk da haka a gidan Amb. Suke zaune.
Tun barin sa gida sai a shekarar baya ne maimartaba da Ya Gumsu suka kai masa ziyara, bisa tsananin rokon Amb. Hassan don maimartaba yace shi har abada Sageer bazai dawo masa gida ba, ya barwa Amb. Hassan shi duniya da lahira sabida gamsuwa da irin rikon da yake musu shi da Awaisu, shi kansa Waziri bai taba bada shawarar su dawo gida ba.
Sai kuma ga abinda Ya Gumsu ta zo da shi yau, na nema masa alfarmar zuwa gida yayi ko sati daya ne.
Ya sake lumshe idon sa ya bude a hankali. A fili ya furta "nima ina kewar ka Muhammad Sageer, tsoron abinda zai je ya zo nake. Ina tattalin mutuncin ka a idon al'ummarka. Duk da Baban ka ya tabbatar min baka da matsala yanzu".
****
A shawarar da suka yi da Waziri ya karfafe shi akan ya bar Yarima ya zo gida, koda sati dayan ne, tunda dai bazai dawwama a kasar da ba tasa ba, dole watarana zai zo gida, sannan Amb. Hassan ya tabbatar musu komai lafiya a tareda Yarima. Awaisu ne dai da yafi kowa kusanci da shi ya ce da Babansa Waziri da saura. Wazirin kuma bai gayawa sarki hakan ba don ya samu nutsuwar barin dan sa ya shiga cikin 'yan uwan sa ko yaya ne. A gefe ya saka limamin Askira da sauran malaman fada yin addu'a ta musamman akan zuwan Yarima Sageer, Allah ya kintsawa mahafin sa shi a matsayin sa na magajin sa.
Da wannan sarki ya yiwa Yarima umarnin zuwa gida don yayi sati daya. A wannan lokacin Amb. Hassan ya gama tenure dinsa na aikin jakadanci yana shirin dawowa gida gabadaya, don haka tare suka soma shirin tahowa shi da 'ya'yan nasa Sageer da Awaisu, inda Amb. Hassan zai sauka a kasar shi ta haihuwa Kanon Dabo, kafun ya koma Birnin Tarayya da zama.
*****
"Na ga sai wani zumudi kake zaka je gida, kamar wani special abu ne zamu je mu taras banda zafin Maiduguri, ni banda Ya Gumsu ta dage sai naje ai har abada na bar Askira kenan, tunda Alanguburo baya son gani na".
Awaisu yayi murmushi yana ninke kayan Yarima yana jera masa cikin tsadaddiyar trolley din sa. Bai yi niyyar bashi amsa ba sai da ya ji Yarima ya sake yin kwafa, "ni ko satin ma bazan cika ba zan dawo, ka san nextweek akwai birthday din da na hadawa (Rose), kawai sai jin zancen tafiyar nan na yi, da na san da ita da tun satin da ya wuce mun yi mun gama, she will be 26 by next week". (Rose, yarinyar Yarima ce da yake ji da ita, 'yar asalin kasar Korea ta kudu), Awaisu ya tamke fuska kamar bai ji shi ba, ya cigaba da jera masa kaya. Daga baya kuma ya ce "ayya! Ai kawai ka tafi da ita Askira ka hada mata birthday din acan zai fi bada ma'ana" Yarima yayi miskilin murmushin sa, ya ce "me kake ci na baka na zuba? Ka zuba ido zuwa shekaru biyu zan kaita Askiran ne, amma a matsayin matata ba budurwa ta ba".
Awaisu ya dauka ya fada ne kawai don ya ji dadin bakin sa, ya manta da wani hali na Yarima Sageer Yusuf Askira, duk abinda ya furta yana nufin sa ne har zuciyar sa. Amma akan zancen Rose bayahudiya bai taba kawowa Yarima da gaske aurenta yake da niyyar yi ba.
A halayen Yarima in ka dauke son matan sa, sauran duka ababen sha'awa ne, Awaisu ba zai daina kiran sa (his role model) ba. Mutum ne mai muhimmanta sallah da kiyaye lokutanta, mai kirki mai kyauta, abun hannun sa bai taba rufe mai ido ba. Ga jin kan na kasa da shi, ga girmama iyaye, sannan ga kokari wajen neman na kai kamar ba dan sarki ba.
Bayan kamfanin da yake yiwa aiki yana kasuwancin automobile daga Amurka zuwa Amsterdam. Duk da haka maimartaba bai taba fasa turo masa kudi duk karshen wata ba, shi Awaisun shine akan komai na kasuwancin nasa kuma kyautatawar da Yarima yake masa a ciki sai ka rantse su biyu suka mallaki jarin kasuwancin.
Babban abunda ke burge Awaisu a halayen Yarima Sageer shine submissiveness, ya san shi mai laifi ne a gurin Ubangiji, amma yana yawan ce da Awaisu ya kasa dainawa, kuma yana so ya daina din, mata sun zame masa barin rayuwa da baya iya rayuwa daidai sai tare da su, don haka kullum cikin istigfari yake yana fadin yana rokon Allah yasa kada ya mutu yana aikata laifin da yake aikatawa.
Ko Awaisu ya soma wa'azi, baya arguing da shi, cewa ya ke ya sani babu kyau ya taya shi addu'a. Sai Awaisu ya koma yi masa yakin karkashin kasa, don kuwa yarima tausayi yake bashi, kana sabo ka san kana yi amma ka ce ba zaka iya dainawa ba, duk yarinyar da ya gani tare da shi zai bi ta bayan idon sa ya ci mutuncin ta ya razanata akan tarayya da Sageer, wani zubin har ya ce Sageer nada cuta, ga turawa da shegen tsoro, saidai Sageer ya nemi yarinyar sa sama ko kasa ya rasa, a karshe saidai ya nemo wata, shi kuma Awaisu baya gajiya da lalatawa, kamar yadda shima baya gajiya da sake nemowa.
Wannan itace rayuwar Yarima Sageer da dan uwan sa Awaisu a kasar Amsterdam. Tamkar ciki daya suka fito, sha'awar su akan komai daya ce ra'ayin su daya, sannan zuciyar su tsayayya ce akan junan su, saidai hali kowa nasa daban.
Jirgin su ya sauka a filin jirgin saman Maiduguri da asubahin safiyar Litinin, zaratan matasan suka soma saukowa daga matattakalar jirgin 'AZMAN' cikin shiga ta barebarin usli, wadanda fatar jikin su ta jiku da boko da kasar sanyi, kai da ganin su ka san sun fito ne daga sarauta ta ainahi ko daga irin takun su da kasaitar su.
Suna sauka motar 'Askira Emirate' na jiran su. Tun a Abuja suka rabu da Amb. Hassan da Mama Laila wadanda suka hau jirgin Kano, su kuma suka hawo na Maiduguri.
Dogarawa bila- adadin duk daga motocin masarautar Askira, suka bude musu kofar motar BMW wadda maimartaba kadai ke hawan ta a gidan. Daga nan basu bata lokaci ba suka kama hanyar Askira da motar civilian mai dauke da wasu fadawan cike fal a cikin ta.