Sashe 3
Kulsum Part 2 Complete Hausa Novel · about 5 min read
*** *** ***
Satin Kulsumu uku kenan a gidan Hajiya Nasara, ta yi sumul da ita, ta murje ta yi haske, har wani irin glowing na musamman fatarta ke yi. Hankalinta ya kwanta ba ta da damuwa ko kankani. Hajiya Nasara ta fada mata sai nan da watanni uku za a fara daukar dalibai a makarantar da zata je. So ta ke ta yi medicine ba Nursing da ta kwallafa wa rai ba. Amma Kulsumu ta ce ita nan duniya Nursing kadai ta ke so.
Yau ne Dr. Sakeenah diyar Hajiya Nasara da mijinta Engr. Farouq za su sauka Nigeria amma a garin Lagos za su sauka, can inda mijin Sakeenahr ya samu aiki a hukumar haraji ta kasa (FIRS) wato Federal Inland Revenue Service.
Tare suka taho da Nasma, wadda ke karatu a jami’ar Nottingham, za ta yi hutun karshen shekara tare da iyayenta. Daga Lagos suka sako Nasma a jirgin Abuja, Hajiya Nasara ta tura direbansu Yusha'u tare da Kulsumu su taho da Nasma daga filin jirgi.
Alhaji Muhammad Bello ya yi tafiya zuwa Port-hearcourt tun kafin zuwan Kulsumu Abuja. Satin ta daya a gidan ya dawo, shi ba mai yawan kula mutane bane kamar matar sa, amma duk da haka sosai ya yi mata barka da zuwa cikin family dinsa. Hajiya Nasara ta yi masa bayanin komai a kan Kulsumu, amma ta sakaya rashin lafiyar ta. Ta ce ta daukota ne kawai don ta yi karatu, in ta gama zata koma Gaya kamar yadda ta alqawartawa su Goggo.
Kulsumu ta sha ganin hoton Nasma a wayar Hajiya, don haka ba ta sha wahalar gane ta a fili ba. Nasma za ta girme mata da a kalla shekaru hudu don kuwa shekarunta ashirin da biyu ne. Tana shekarar karshe a jami’a inda ta ke karantar accountancy. Ita ma Nasma ta gane Kulsumu don Hajiya Nasara ta sha tura mata hoton ta. Tana ganinta ta sakar mata murmushi tare da rike hannunta, ta ce.
“It is nice meeting you Kulthum. Ganinki ya fi jin ki, you are really beautiful”.
Murmushi Kulsumu ta yi, murmushin jin dadi irin wanda dan adam ke yi in an yabe shi, ta ce, “Barka da zuwa Aunty Nasma”.
Ta karbi jakar hannunta daidai lokacin da Yusha'u ya zo ya dauki trolley dinta suka rankaya zuwa mota.
*** *** ***
Nasma ta fito kanta babu kallabi, gashi gare ta ba na wasa ba na fulanin usli, ta dunkule shi cikin hair bound ta nufi dakin mahaifiyar ta. Ita da Kulsumu ne a dakin, Hajiya na amsa waya a gefen gadonta yayin da Kulsumu ke tsaye jikin closet dinta tana jera mata kayanta da aka kawo daga wanki da guga, ta zauna gefen Hajiya Nasara wadda ta ajiye wayarta ta bata hankalinta.
“Har kin gama cin abincin ne Nasma?”
“Sai anjima zan ci Mum, Kulsum ta dinga kwana dakina mana, ni ban iya kwana ni kadai kin sani. A gidan Aunty Sakeenah ni da su Waleed (‘ya’yan Sakeenah) muke kwana”.
Hajiya ta yi dan jim, kafin ta ce, “Kin fiya rigima Nasma, da girmanki ki ke wani tsoron kwana ke kadai? To ba za ta taya ki kwanan ba, ki koma gidan su Waleed din”.
Nasma ta marairaice, “Don Allah Mum, at least ko na sati daya ne zuwa in saba da dakin, ya yi min girma”.
Kulsumu kirjinta sai duka yake sabida fargabar amincewar Hajiya ta kwana daki daya da Nasma, what of idan ta yi mata fitsari? Nasma ma’abociyar gayu na karshe, duk wannan son da ta ke mata ta sani da zarar ta gane ita mai fitsari a kwance ce zai koma kyama.
Abin farin cikinta sai Hajiya ta kori Nasma, ta ce ba ta amince Kulsumu ta taya ta kwanan ba.
Ta yi shirin kwanciya ke nan za ta karanta azkar din dare ta kwanta, sai ga Nasma ta shigo buguzum-buguzum niki-niki rungume da duvet dinta, ta ce, “Kulsum mu kwana tare, ban iya kwana ni kadai Allah, duk yadda na yi kokari”.
Ba tare da ta jira cewarta ba ta haye gadon ta dukunkune cikin duvet dinta. A wannan ranar yadda Kulsumu ta ga rana haka ta ga dare a zaune don tsoron kada ta kwanta barci ya dauke ta ta yi fitsari Nasma ta sani. Cikin matsanancin tashin hankali.
Sai da Hajiya ta zo tashinta sallar asubahi ta ga Nasma na sharar barci akan gado, ita kuma Kulsumu na jingine jikin gadon tana gyangyadi tana farkawa. Tausayi ya yi mugun kamata, ta sakar wa Nasma duka a cinya, ba shiri ta zabura ta mike zaune.
Hajiya ta ce, ta koma dakinta yanzun nan ba ta ganin Kulsumu a kasa ta kwana? Ta zo ta takura mata saboda tsoron ta na banza da wofi, me zai cinye ta in ta kwana ita kadai din? Kada ta kara zuwa ta takura mata.
Hajiya Nasara zaune bisa stool a washegarin ranar, waya ta ke da ‘yarta Sakeenah da ke Lagos, ta gaya mata komai game da Kulsumu da halin da ta ke ciki na lalurar fitsarin kwance tun haihuwar ta. Sakeenah ta ce a sako mata Kulsumu a jirgi ta zo Lagos za ta duba ta na ‘yan kwanaki, amma za ta yi akalla wata biyu a hannunta. Hajiya Nasara ta ce, ba za ta iya barinta ta zo har Lagos ita kadai ba sabida ba wani wayewar kai ne da ita sosai ba, sai dai ta hado su da Nasma, amma ta lura Kulsumu ba ta son Nasma ta san lalurarta. Ita ma kuma ba ta son ta sani din, kowa yana da sirri a rayuwarsa.
Sakeenah ta fahimta, ta ce da mahaifiyarta kada ta damu, ta sako ta a jirgi kawai, ita da kanta za ta je ta dauke ta. Insha Allah ba za ta bata ba. Da haka suka yi sallama.
Satin Kulsumu uku kenan a gidan Hajiya Nasara, ta yi sumul da ita, ta murje ta yi haske, har wani irin glowing na musamman fatarta ke yi. Hankalinta ya kwanta ba ta da damuwa ko kankani. Hajiya Nasara ta fada mata sai nan da watanni uku za a fara daukar dalibai a makarantar da zata je. So ta ke ta yi medicine ba Nursing da ta kwallafa wa rai ba. Amma Kulsumu ta ce ita nan duniya Nursing kadai ta ke so.
Yau ne Dr. Sakeenah diyar Hajiya Nasara da mijinta Engr. Farouq za su sauka Nigeria amma a garin Lagos za su sauka, can inda mijin Sakeenahr ya samu aiki a hukumar haraji ta kasa (FIRS) wato Federal Inland Revenue Service.
Tare suka taho da Nasma, wadda ke karatu a jami’ar Nottingham, za ta yi hutun karshen shekara tare da iyayenta. Daga Lagos suka sako Nasma a jirgin Abuja, Hajiya Nasara ta tura direbansu Yusha'u tare da Kulsumu su taho da Nasma daga filin jirgi.
Alhaji Muhammad Bello ya yi tafiya zuwa Port-hearcourt tun kafin zuwan Kulsumu Abuja. Satin ta daya a gidan ya dawo, shi ba mai yawan kula mutane bane kamar matar sa, amma duk da haka sosai ya yi mata barka da zuwa cikin family dinsa. Hajiya Nasara ta yi masa bayanin komai a kan Kulsumu, amma ta sakaya rashin lafiyar ta. Ta ce ta daukota ne kawai don ta yi karatu, in ta gama zata koma Gaya kamar yadda ta alqawartawa su Goggo.
Kulsumu ta sha ganin hoton Nasma a wayar Hajiya, don haka ba ta sha wahalar gane ta a fili ba. Nasma za ta girme mata da a kalla shekaru hudu don kuwa shekarunta ashirin da biyu ne. Tana shekarar karshe a jami’a inda ta ke karantar accountancy. Ita ma Nasma ta gane Kulsumu don Hajiya Nasara ta sha tura mata hoton ta. Tana ganinta ta sakar mata murmushi tare da rike hannunta, ta ce.
“It is nice meeting you Kulthum. Ganinki ya fi jin ki, you are really beautiful”.
Murmushi Kulsumu ta yi, murmushin jin dadi irin wanda dan adam ke yi in an yabe shi, ta ce, “Barka da zuwa Aunty Nasma”.
Ta karbi jakar hannunta daidai lokacin da Yusha'u ya zo ya dauki trolley dinta suka rankaya zuwa mota.
*** *** ***
Nasma ta fito kanta babu kallabi, gashi gare ta ba na wasa ba na fulanin usli, ta dunkule shi cikin hair bound ta nufi dakin mahaifiyar ta. Ita da Kulsumu ne a dakin, Hajiya na amsa waya a gefen gadonta yayin da Kulsumu ke tsaye jikin closet dinta tana jera mata kayanta da aka kawo daga wanki da guga, ta zauna gefen Hajiya Nasara wadda ta ajiye wayarta ta bata hankalinta.
“Har kin gama cin abincin ne Nasma?”
“Sai anjima zan ci Mum, Kulsum ta dinga kwana dakina mana, ni ban iya kwana ni kadai kin sani. A gidan Aunty Sakeenah ni da su Waleed (‘ya’yan Sakeenah) muke kwana”.
Hajiya ta yi dan jim, kafin ta ce, “Kin fiya rigima Nasma, da girmanki ki ke wani tsoron kwana ke kadai? To ba za ta taya ki kwanan ba, ki koma gidan su Waleed din”.
Nasma ta marairaice, “Don Allah Mum, at least ko na sati daya ne zuwa in saba da dakin, ya yi min girma”.
Kulsumu kirjinta sai duka yake sabida fargabar amincewar Hajiya ta kwana daki daya da Nasma, what of idan ta yi mata fitsari? Nasma ma’abociyar gayu na karshe, duk wannan son da ta ke mata ta sani da zarar ta gane ita mai fitsari a kwance ce zai koma kyama.
Abin farin cikinta sai Hajiya ta kori Nasma, ta ce ba ta amince Kulsumu ta taya ta kwanan ba.
Ta yi shirin kwanciya ke nan za ta karanta azkar din dare ta kwanta, sai ga Nasma ta shigo buguzum-buguzum niki-niki rungume da duvet dinta, ta ce, “Kulsum mu kwana tare, ban iya kwana ni kadai Allah, duk yadda na yi kokari”.
Ba tare da ta jira cewarta ba ta haye gadon ta dukunkune cikin duvet dinta. A wannan ranar yadda Kulsumu ta ga rana haka ta ga dare a zaune don tsoron kada ta kwanta barci ya dauke ta ta yi fitsari Nasma ta sani. Cikin matsanancin tashin hankali.
Sai da Hajiya ta zo tashinta sallar asubahi ta ga Nasma na sharar barci akan gado, ita kuma Kulsumu na jingine jikin gadon tana gyangyadi tana farkawa. Tausayi ya yi mugun kamata, ta sakar wa Nasma duka a cinya, ba shiri ta zabura ta mike zaune.
Hajiya ta ce, ta koma dakinta yanzun nan ba ta ganin Kulsumu a kasa ta kwana? Ta zo ta takura mata saboda tsoron ta na banza da wofi, me zai cinye ta in ta kwana ita kadai din? Kada ta kara zuwa ta takura mata.
Hajiya Nasara zaune bisa stool a washegarin ranar, waya ta ke da ‘yarta Sakeenah da ke Lagos, ta gaya mata komai game da Kulsumu da halin da ta ke ciki na lalurar fitsarin kwance tun haihuwar ta. Sakeenah ta ce a sako mata Kulsumu a jirgi ta zo Lagos za ta duba ta na ‘yan kwanaki, amma za ta yi akalla wata biyu a hannunta. Hajiya Nasara ta ce, ba za ta iya barinta ta zo har Lagos ita kadai ba sabida ba wani wayewar kai ne da ita sosai ba, sai dai ta hado su da Nasma, amma ta lura Kulsumu ba ta son Nasma ta san lalurarta. Ita ma kuma ba ta son ta sani din, kowa yana da sirri a rayuwarsa.
Sakeenah ta fahimta, ta ce da mahaifiyarta kada ta damu, ta sako ta a jirgi kawai, ita da kanta za ta je ta dauke ta. Insha Allah ba za ta bata ba. Da haka suka yi sallama.