Sashe 18
Kulsum Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
*** *** ***
READING
Turaki ne tafe cikin kankanuwar motar sa kirar Acura akan shimfidadden titin da zai sada shi da gidan aminin sa Abdul'Ahad Aminu Maikano, misalin karfe biyar da rabi na yammacin ranar Talata bayan ya taso aiki daga jami'ar ta Reading. Kamar kullum sanye yake cikin bakaken suit masu kauri, ya tsuke wuyan sa da ruwan tokar tie fatar shi tayi santsi har wani sheki take yi na musamman. Ta earpiece din dake makale a kunnen sa yake magana da Abdul'Ahad din "i am on my way Aboki....nan da mintuna ashirin zan karaso".
Sati biyu kenan da angwancewar Abdul'Ahad da amaryar sa wata hazikar dalibar sa Dr. Sajidah wadda 'yar kasar Eritrea ce. Iyayenta Refugees ne a United Kingdom. Sanda ya iso gidan nasu mai cike da korran shuke-shuke daga sama har kasa, har lokacin sallar maghriba ya gabato.
A kofar gidan ya tadda Abdul'Ahad da Sajeedah din suna jiran isowar sa, ya faka motar ya fito Sajeedah na yi masa barka da zuwa, tare suka rankaya su duka zuwa cikin gidan.
Gidan nasu bai cika girma ba amma cike yake da duk wani nau'in kayan alatun jin dadi da saukaka rayuwar dan adam. Abdul'Ahad ya gayyato shi cin abincin dare ne kamar yadda su kanyi lokaci zuwa lokaci. Kuma su tattauna akan matsalar Turakin wadda ba komai bace banda 'UmmuKulsum' kamar yadda Turakin ke kiran ta in full.
Sallah suka fara yi, kafin su idar Sajeedah ta gama shirya musu tebir, bayan sun idar suka nufi dining din Abdul'Ahad na cewa Sajeedah "in ji dai kin cika tukunya da kyau, kinsan gwauraye ba'a sa musu sanwa kadan". Dariya Sajidah tayi tace "shima Dr. Abubakar ya kusa tashi daga gwauro don nayi masa kamun kanwata, Fadwa, jira nake ta samu hutu in dauko ta su ga juna". Turaki na dan murmushi bai ce komi ba. Abdul'Ahad yace "wane Abubakar din? Yana da matar sa a gida fa, Allah ya kashe ya bata, ya gama mutuwa a kanta, ki dai taya shi biko shine za ki yi gwanin ta, Kulsum yake jira ya dawo da abar sa, kuma insha Allah zamu yi nasara".
Cikin mamaki Sajeedah ta tambayi mijin ta cikin harshen turanci "dama yana da mata?" Turaki wanda ke zuba abinci a plate kansa a kasa, cikin kwantaccen sautin sa yace "Sajeedah, rabu da mijin ki kin ji, i am all alone, living alone, ta riga ta kubuce min, bisa sakaci da kuskure na, bansan ina zan nemo ta ba, duk wata hanya da zan samu labarin inda take bani da ita, keep praying for me kin ji, ita kadai nake so!"
Cikin mamakin abinda take ji yau daga bakin Dr. Turaki Sajeedah tace.
"Kun rabu ne?"
"An raba mu dai, don ba ni na saketa ba". Ya bata amsa.
A gajarce Abdul'Ahad ya bata labarin komai. Sajeedah ta rasa abinda zata ce, a karshe tace "hakkin iyaye dana Kulsum ne ya rikide ya koma maka soyayyah Dr. Abubakar. How i wish zan ga Kulthum da na yi kokari na bata hakuri ta dawo". Murmushi Abdul'Ahad yayi cikin zolaya ya ce "to ka karbi wadda ake ma tayi mana ka rage zafi? In ya so in Kulsum ta bayyana sai ka hada biyu? Sanyin garinnan without a wife is terrible".
Hararar Abdul'Ahad yayi, sannan ba tare da ya tofa ba ya mike yana duba agogon swatch blustery dake daure a damtsen hannun daman sa.
"Zan tafi gida, akwai marking din takardun dalibai da zan yi. Sajeedah, you cooks nicely, thank you once again". Sajeedah tace "ai fa ka kore shi, inama zan ga Kulthum dinnan in gaya mata how lucky she is! For winning this precious heart of Turaki. Ta dawo wa mijin ta mai kaunar ta.
Dr. Abubakar duk ranar da Kulsum ta dawo mana zan zama babbar abokiyar ta, ko don in gaya mata irin son da muka wanzu muna yi mata, a lokacin da ta kubuce mana".
Murmushin dai kawai yayi, sai dai bai ce komai ba, tausayin kansa yake ji don gani yake kamar ya rasa Kulsum har abada, wani abu da ya tabbatar zuciyar sa komai juriyar ta bazata karba ba. Gaban sa har wani irin faduwa yake yi idan ya tuna Kulsum zata iya auren wani a halin yanzu. Idan kuma hakan ya tabbata shi da aure sai ranar da Ubangiji ya nufa. Zai kare rayuwar sa a haka. Sannan zai fasa komawa gida.
Duk wani tanadin rayuwar sa ta gaba, ya tsara shi ne tare da Kulsum. Duk abinda yake tarawa don ta ji dadi ne ita da 'ya'yan da zasu haifa. Yayi wa Kulsumu tanadin rayuwa mai gardi, da soyayya irin wadda ko a hikaya babu duk don ya wanke laifukan sa na baya. Ya sa kai ya fita ya nufi motar sa Dr. Abdul'Ahad ya biyo bayan sa.
A jikin motar sa suka tsaya yayin da Sajeedah ta koma gida.
"Any development?" AbdulAhad ya tambaya.
"Aboki ina cikin damuwa mai tsanani, i'm just pretending to look okay. Bana iya barci, ko na yi barci mafarkin ta nake yi tare da wani na, na kira Batulu ko sun samu wani labari ta ce har yanzu babu, har makotan su data sa su gaya mata da zarar sun ga tazo wajen Kakannin nata sun ce har yanzu bata zo ba. Na tabbata su Goggo sun boye UmmuKulsum ne kuma ba don kowa suka boye ta ba sai don ni. Idan ta auri wani ba ni ba na tabbata karshen farin ciki na ya zo Aboki. Su Maimartaba sun ki sanya baki har yanzu. Ina cikin yanayin da nake bukatar aure, in kuma ba ita na samu ta dawo min ba bazan iya auren kowacce mace ba, ka bani shawara, domin kwarai na ji dadin shawararka ta baya, na kuma amfana da ita".
Abdul Ahad ya nisa yace "a yanzu dai bamu da zarafin zuwa gida har sai mun hada abinda ke gabanmu (zama cikakkun consultants), na maka alkawarin ni zan taya ka nemo Kulsum kuma kakannin ta da kan su zasu gaya mana inda take, na san abinda zan ce musu su karbi nadamar mu, ai da ciwo abinda ka yin, it's not easy ka dawo yanzu ka ce kana son ta su yarda da wuri, zasu yi ta tsammanin ka dawo ne don ka samu ka farantawa iyayen ka ba don kana son 'yar su ba, in aka yi la'akari da yadda komai ya wakana".
Sun dade suna tattaunawa Abdul 'Ahad na kwantar masa da hankali, har yana fadin "Turaki believe me..... Kulsum bazata iya auren kowa ba bayan kai, u are her first love, her first husband, duk wanda zata aura da fargaba zata shiga gidan sa tunda ta san ita ba budurwa bace, ko zata yi aure a gaskiya ba yanzu ba, abinda zata fi maida hankali a kai yanzu shine neman ilmi don ta gina rayuwar ta".
*** *** ***
Dr. Sakeenah ta daga waya ta yi kiran lambar Taufeeq, “Yaya Taufeeq guess what?”
Dan tsaki ya yi, “Ke fa haka ki ke, sai mutum yana tsaka da aiki ki ishe shi da shirme, komi ba za ki fada kanki tsaye ba sai kin yi ta kumbiya-kumbiya”.
Sakeenah ta ce, “Tunda ba za ka saurare ni ba ka yi wa kanka, na fasa gaya maka albishir din”.
Ta kashe wayarta.
Ya kira ta ki dagawa, ya sake kira ta kashe wayar gabadaya. Don haka da ya tashi aiki ya dauke kan motarsa ya yi Victoria Island gidan Sakeenah, duk da ya san ba wani abu ba ne mai muhimanci za ta gaya masa.
READING
Turaki ne tafe cikin kankanuwar motar sa kirar Acura akan shimfidadden titin da zai sada shi da gidan aminin sa Abdul'Ahad Aminu Maikano, misalin karfe biyar da rabi na yammacin ranar Talata bayan ya taso aiki daga jami'ar ta Reading. Kamar kullum sanye yake cikin bakaken suit masu kauri, ya tsuke wuyan sa da ruwan tokar tie fatar shi tayi santsi har wani sheki take yi na musamman. Ta earpiece din dake makale a kunnen sa yake magana da Abdul'Ahad din "i am on my way Aboki....nan da mintuna ashirin zan karaso".
Sati biyu kenan da angwancewar Abdul'Ahad da amaryar sa wata hazikar dalibar sa Dr. Sajidah wadda 'yar kasar Eritrea ce. Iyayenta Refugees ne a United Kingdom. Sanda ya iso gidan nasu mai cike da korran shuke-shuke daga sama har kasa, har lokacin sallar maghriba ya gabato.
A kofar gidan ya tadda Abdul'Ahad da Sajeedah din suna jiran isowar sa, ya faka motar ya fito Sajeedah na yi masa barka da zuwa, tare suka rankaya su duka zuwa cikin gidan.
Gidan nasu bai cika girma ba amma cike yake da duk wani nau'in kayan alatun jin dadi da saukaka rayuwar dan adam. Abdul'Ahad ya gayyato shi cin abincin dare ne kamar yadda su kanyi lokaci zuwa lokaci. Kuma su tattauna akan matsalar Turakin wadda ba komai bace banda 'UmmuKulsum' kamar yadda Turakin ke kiran ta in full.
Sallah suka fara yi, kafin su idar Sajeedah ta gama shirya musu tebir, bayan sun idar suka nufi dining din Abdul'Ahad na cewa Sajeedah "in ji dai kin cika tukunya da kyau, kinsan gwauraye ba'a sa musu sanwa kadan". Dariya Sajidah tayi tace "shima Dr. Abubakar ya kusa tashi daga gwauro don nayi masa kamun kanwata, Fadwa, jira nake ta samu hutu in dauko ta su ga juna". Turaki na dan murmushi bai ce komi ba. Abdul'Ahad yace "wane Abubakar din? Yana da matar sa a gida fa, Allah ya kashe ya bata, ya gama mutuwa a kanta, ki dai taya shi biko shine za ki yi gwanin ta, Kulsum yake jira ya dawo da abar sa, kuma insha Allah zamu yi nasara".
Cikin mamaki Sajeedah ta tambayi mijin ta cikin harshen turanci "dama yana da mata?" Turaki wanda ke zuba abinci a plate kansa a kasa, cikin kwantaccen sautin sa yace "Sajeedah, rabu da mijin ki kin ji, i am all alone, living alone, ta riga ta kubuce min, bisa sakaci da kuskure na, bansan ina zan nemo ta ba, duk wata hanya da zan samu labarin inda take bani da ita, keep praying for me kin ji, ita kadai nake so!"
Cikin mamakin abinda take ji yau daga bakin Dr. Turaki Sajeedah tace.
"Kun rabu ne?"
"An raba mu dai, don ba ni na saketa ba". Ya bata amsa.
A gajarce Abdul'Ahad ya bata labarin komai. Sajeedah ta rasa abinda zata ce, a karshe tace "hakkin iyaye dana Kulsum ne ya rikide ya koma maka soyayyah Dr. Abubakar. How i wish zan ga Kulthum da na yi kokari na bata hakuri ta dawo". Murmushi Abdul'Ahad yayi cikin zolaya ya ce "to ka karbi wadda ake ma tayi mana ka rage zafi? In ya so in Kulsum ta bayyana sai ka hada biyu? Sanyin garinnan without a wife is terrible".
Hararar Abdul'Ahad yayi, sannan ba tare da ya tofa ba ya mike yana duba agogon swatch blustery dake daure a damtsen hannun daman sa.
"Zan tafi gida, akwai marking din takardun dalibai da zan yi. Sajeedah, you cooks nicely, thank you once again". Sajeedah tace "ai fa ka kore shi, inama zan ga Kulthum dinnan in gaya mata how lucky she is! For winning this precious heart of Turaki. Ta dawo wa mijin ta mai kaunar ta.
Dr. Abubakar duk ranar da Kulsum ta dawo mana zan zama babbar abokiyar ta, ko don in gaya mata irin son da muka wanzu muna yi mata, a lokacin da ta kubuce mana".
Murmushin dai kawai yayi, sai dai bai ce komai ba, tausayin kansa yake ji don gani yake kamar ya rasa Kulsum har abada, wani abu da ya tabbatar zuciyar sa komai juriyar ta bazata karba ba. Gaban sa har wani irin faduwa yake yi idan ya tuna Kulsum zata iya auren wani a halin yanzu. Idan kuma hakan ya tabbata shi da aure sai ranar da Ubangiji ya nufa. Zai kare rayuwar sa a haka. Sannan zai fasa komawa gida.
Duk wani tanadin rayuwar sa ta gaba, ya tsara shi ne tare da Kulsum. Duk abinda yake tarawa don ta ji dadi ne ita da 'ya'yan da zasu haifa. Yayi wa Kulsumu tanadin rayuwa mai gardi, da soyayya irin wadda ko a hikaya babu duk don ya wanke laifukan sa na baya. Ya sa kai ya fita ya nufi motar sa Dr. Abdul'Ahad ya biyo bayan sa.
A jikin motar sa suka tsaya yayin da Sajeedah ta koma gida.
"Any development?" AbdulAhad ya tambaya.
"Aboki ina cikin damuwa mai tsanani, i'm just pretending to look okay. Bana iya barci, ko na yi barci mafarkin ta nake yi tare da wani na, na kira Batulu ko sun samu wani labari ta ce har yanzu babu, har makotan su data sa su gaya mata da zarar sun ga tazo wajen Kakannin nata sun ce har yanzu bata zo ba. Na tabbata su Goggo sun boye UmmuKulsum ne kuma ba don kowa suka boye ta ba sai don ni. Idan ta auri wani ba ni ba na tabbata karshen farin ciki na ya zo Aboki. Su Maimartaba sun ki sanya baki har yanzu. Ina cikin yanayin da nake bukatar aure, in kuma ba ita na samu ta dawo min ba bazan iya auren kowacce mace ba, ka bani shawara, domin kwarai na ji dadin shawararka ta baya, na kuma amfana da ita".
Abdul Ahad ya nisa yace "a yanzu dai bamu da zarafin zuwa gida har sai mun hada abinda ke gabanmu (zama cikakkun consultants), na maka alkawarin ni zan taya ka nemo Kulsum kuma kakannin ta da kan su zasu gaya mana inda take, na san abinda zan ce musu su karbi nadamar mu, ai da ciwo abinda ka yin, it's not easy ka dawo yanzu ka ce kana son ta su yarda da wuri, zasu yi ta tsammanin ka dawo ne don ka samu ka farantawa iyayen ka ba don kana son 'yar su ba, in aka yi la'akari da yadda komai ya wakana".
Sun dade suna tattaunawa Abdul 'Ahad na kwantar masa da hankali, har yana fadin "Turaki believe me..... Kulsum bazata iya auren kowa ba bayan kai, u are her first love, her first husband, duk wanda zata aura da fargaba zata shiga gidan sa tunda ta san ita ba budurwa bace, ko zata yi aure a gaskiya ba yanzu ba, abinda zata fi maida hankali a kai yanzu shine neman ilmi don ta gina rayuwar ta".
*** *** ***
Dr. Sakeenah ta daga waya ta yi kiran lambar Taufeeq, “Yaya Taufeeq guess what?”
Dan tsaki ya yi, “Ke fa haka ki ke, sai mutum yana tsaka da aiki ki ishe shi da shirme, komi ba za ki fada kanki tsaye ba sai kin yi ta kumbiya-kumbiya”.
Sakeenah ta ce, “Tunda ba za ka saurare ni ba ka yi wa kanka, na fasa gaya maka albishir din”.
Ta kashe wayarta.
Ya kira ta ki dagawa, ya sake kira ta kashe wayar gabadaya. Don haka da ya tashi aiki ya dauke kan motarsa ya yi Victoria Island gidan Sakeenah, duk da ya san ba wani abu ba ne mai muhimanci za ta gaya masa.