Sashe 10
Kulsum Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
“Daga baya ke nan!”.
Daga wannan ba ta kara tofawa ba.
*** *** ***
Washegari Goggo ta kira Hajiya Nasara ta ce, “Nasara jiya sai ga mu da babban bako, mijin Kulsumu daga Turai ya zo biko”.
Hajiya Nasara ta ce, “Ina fatan dai Goggo kin bi shawarata ba ki gaya masa inda ta ke ba?”
Goggo ta ce, “Ai na fahimci abin da ki ke nufi Nasara, cewa muka yi ma ba ta kasar, daga ni har Baffa kuma ko sunan kasar da ku ke ba mu sani ba.
Amma gaskiya Turaki ya ba ni tausayi, sai da na ji kamar in ba shi lambar wayarta, amma na ce bari in fara shawara da ke tukun kada in bata lamari. Amma mai zai hana mu maida mishi matarshi ta yi karatun a dakinta Nasara? Aure fa yana gaba da komai, kuma na san ba za su hana Kulsumu karatu ba”.
A tsanake Hajiya Nasara ta ce, “Goggo, kada ki yi saurin karaya. Mijin Kulsumu yana bukatar a ba shi lokaci ya tantance tsakanin fari da baki a cikin aurensa da Kulsumu. Ma’ana, baki da tabbacin zai maida ta ne don ya faranta wa iyayensa ko don yana sonta. Sannan ita ma Kulsumu akwai bukatar ta kara hankali, wayewa da nutsuwa kafin ta zaba wa kanta hukuncin komawa gidan mijinta ko yin sabon aure.
Goggo ki daure ki ci gaba da ba ni hadin kai tukunna, ki cire tausayin Turaki a ranki. Shi bai tausaya wa jikarki ba ya tafi ya barta shekara da shekaru a dakinsa ba sako babu kulawa? Ni ban yarda yanzu sonta yake ba, na fi yarda da cewa so yake ya gyara tsakaninsa da iyayensa.
Ki kyale Kulsumu na dan lokaci ta kara sanin kanta, ta samu lafiyar jikin ta, ta yi karatunta sannan ta auri mijin da ke son ta ta ke son shi. Ra’ayi da tunanin su ya zo daya. Koda kuwa Turakin ne amma a can gaba. Sannan Turakin nan fa ba shi ne autan maza ba, ba'a ce bayan shi Kulsumu bazata auru ba wai don lalurar ta, kuma duk abin da ki ke hange a tare da shi akwai shi a sauran maza.
Ki fahimce ni Yaya Aishatu, ba nufi na in hana Kulsumu aure ba, amma don Allah ki kara mata lokaci. Na yi miki alkawarin ranar data zama cikakkiyar Nurse zan dawo miki da ita ta zabi mijin aure. Alhamdu lillahi ta samu lafiyarta wadda ya guje ta a kanta bai kamata don ya zo ya marairaice muku tashi daya ku yi saurin amsa masa ba, gara ya san Kulsumu mace ce mai daraja ya kuma san cewa akwai bambanci tsakanin mai lalurar da ya guda da wannan ta yanzu”.
Goggo ta rausayar da kai, ta ce, “Duk na fahimce ki, na kuma yarda da shawarar ki. Sai dai ba mu da hujjar cewa Turaki ya guji Kulsumu ne sabida lalurarta. Sun auri Kulsumu a kan sanin cewa tana da lalurar. Aure ne dai in Allah ya kawo karshensa dan Adam bai da dabara, amma na yarda da hujjojin da ya bayar kwata-kwata ba su da alaka da lalurar ta”.
Hajiya Nasara ta ce, “Shi ke nan. Allah shi ne masanin gaibu, amma maganar komen nan ki manta da ita Goggo, cikin watan nan Kulsumu za ta fara karatunta, ina rokonku don Allah ku manta da Turaki. Can gaba in suna da rabon komawar sa koma idan tana son shi yana sonta cikin nutsuwa da cikakken hankalin su, Allah ya yi wa Kulsumu zabi mafi alkhairi”.
Goggo ta ce, “Amin Nasara, insha Allahu yadda ki ka ce, haka za a yi”.
*** *** ***
Umma ta shiga turakar Maimartaba a daren ranar a matsayinta na mai girki a ranar. Bayan ya gama cin abinci ta ke labarta masa yadda Batulu ta ba ta labarin zuwansu gidan Malam Jibo ita da Turaki, Maimartaba ya gama sauraronta tsaf! Sannan ya yi murmushi ya ce.
“Kin ga hikimar da na yi ta zare hannunmu daga cikin maganar ta fito zahiri ko? Sun dauke ‘yar su zuwa inda za ta samu kwanciyar hankali ta yi karatun da suke so ta yi, ta auri miji mai sonta tsakani da Allah. Yau da mun saka baki da mun shiga hakkinsu, kunyarmu tasa su dawo da ita ya zo ya sake ba mu kunya, ya sake tafiya ya barta, don ya ce min ashe aiki ya samu a can din amma bayan shekaru uku zai dawo gida gabadaya.
Rakiya raba kanki da sha’anin Turaki, in ya damu ya je ya nemo ta a inda iyayenta suka boye ta. Ya karbi aurenta a hannunsu da kansa, in sun amince mu sai mu bi su da addu’a, amma kada ki sake sa baki a sha’anin Turaki, wanda muka yi a baya ya bula mana kasa a ido, Allah ya ba mu lada”.
Umma ta ce, “Ai na cire hannun nawa ranka ya dade, na dai kasa cire yarinyar a raina ne. Ni na san na yi asarar surukar kwarai mai son Turaki da zuciya daya. Zan bi su da addu’a Allah ya yi musu zabin alkhairi dukkanninsu. Allah ya sa watarana Kulsumu za ta dawo min”.
Murmushi Maimartaba Sarkin Gaya ya yi, ya ce, “Mata kuna son kanku da yawa, sannan kuna saurin manta girman laifin ‘ya’yan ku. Ni kuma na fi yi mata addu’ar Allah ya ba ta miji mai sonta ba Turaki ba, har yanzu ban gasgata wannan sabuwar soyayyar tasa ta dare daya ba, ya ce tunda ya tafi ya soma sonta, me ya hana ya dawo ya gyara laifinsa a lokacin da ya dace?”
Umma ta ce, “Haka Allah ya rubuta masa ranka ya dade, ko mun yi niyyar yin abu sai Allah ya nufa, ko ni ka shammace ni ban taba zaton za ka raba auren nan ba komai dadewar da Turaki zai yi. Sabida jikina na ba ni komai daren dadewa Turaki zai so Kulsumu, domin na mika lamarin su ga Ubangiji, kuma na tabbatar da ya karbi budurcin ta ranar da zai tafi. Kuma Alhamdulillah inada yaqinin wannan ne ya zama silar canzawar zuciyar sa a kanta”.
Maimartaba ya tsura mata ido, bai ce komai ba, amma can a karkashin zuciyarsa ya fara nadamar tsatstsauran hukuncin nasa, da ta yi masa wannan bayanin tun farko da ya yi wani hukuncin da bai kai raba su tsauri ba. Bai san cewa Turaki ya bi umarninsa ba ya tabbatar da auren sa kafin ya tafi. Ya soma zargin kansa da yin zalunci ga karamar yarinyar da ya mayar bazawara a kananan shekarunta. Amma da ya tuna ya yi ne bisa kyakkyawar niyya ta adalci ga talakawansa sai ya rage zargin kan nasa.
***
Watanni biyu Turaki ya kwashe cikin iyayensa da ‘yan uwansa. Duk wata ‘yar uwarsa da ke gidan aure sai da ya kai mata ziyara. Wajen aikinsa na ta nemansa, don haka ya kara neman izinin iyayensa kan ya koma U.K, ya kammala consultant ya baro aiki da su ya dawo gida bakidaya. A kan wannan alkawarin suka amince masa ya koma. Batulu har kuka ta yi sosai da zai tafi.
Bai tafi ba sai da ya je ya yi wa Goggo sallama ita da Baffa, yana kara yi musu tunin lambar waya idan su Kulsumu sun zo, ya yi alkawarin ko a wacce kasa suke zai bi Kulsumu. Baffa dai sai da ya ji kamar ya ba shi lambar, amma ya tuna rokon da Nasara ta yi ta yi masa a waya kan kada ya bayar din. Ya sani ita mai nufin alkhairi ga Kulsumu ne. Ta yi hakan ne da kyakkyawar manufa ba don ta hana ta zaman aure ba.
Ranar da ya tafi ne kuma aka sauke musu buhunhuna da katon-katon na kayan abinci. Sai da aka cika dakin da Baffa ke ajiye shirginsa. Sako ne daga Turaki, da kudi masu yawa cikin ambulan.
Baffa ya ce da ‘yan aiken su mayar masa da kudin ba zai karba ba, inda suke gaya amsa ai Turaki ya riga ya bar garin Gaya zuwa inda ya fito. Haka ya wuni da jimamin abin. Goggo ta ce za ta je ta yi wa Hajiya Rakiya godiya, Baffa ya yi hakuri kawai ya karba don bai kamata su mayar wa Hajiya Rakiya ba.
Ko da ta je yi wa Umma godiyar cewa ta yi, “Haba Hajiya Shatu, Turaki ai dan ku ne, don ya yi muku alheri ba sai na sani ba. Don Allah kada irin haka ta sake faruwa ki ce za ki yi min godiya, tsakaninku ne da Dan ku, ni babu ruwana”.
Daga wannan ba ta kara tofawa ba.
*** *** ***
Washegari Goggo ta kira Hajiya Nasara ta ce, “Nasara jiya sai ga mu da babban bako, mijin Kulsumu daga Turai ya zo biko”.
Hajiya Nasara ta ce, “Ina fatan dai Goggo kin bi shawarata ba ki gaya masa inda ta ke ba?”
Goggo ta ce, “Ai na fahimci abin da ki ke nufi Nasara, cewa muka yi ma ba ta kasar, daga ni har Baffa kuma ko sunan kasar da ku ke ba mu sani ba.
Amma gaskiya Turaki ya ba ni tausayi, sai da na ji kamar in ba shi lambar wayarta, amma na ce bari in fara shawara da ke tukun kada in bata lamari. Amma mai zai hana mu maida mishi matarshi ta yi karatun a dakinta Nasara? Aure fa yana gaba da komai, kuma na san ba za su hana Kulsumu karatu ba”.
A tsanake Hajiya Nasara ta ce, “Goggo, kada ki yi saurin karaya. Mijin Kulsumu yana bukatar a ba shi lokaci ya tantance tsakanin fari da baki a cikin aurensa da Kulsumu. Ma’ana, baki da tabbacin zai maida ta ne don ya faranta wa iyayensa ko don yana sonta. Sannan ita ma Kulsumu akwai bukatar ta kara hankali, wayewa da nutsuwa kafin ta zaba wa kanta hukuncin komawa gidan mijinta ko yin sabon aure.
Goggo ki daure ki ci gaba da ba ni hadin kai tukunna, ki cire tausayin Turaki a ranki. Shi bai tausaya wa jikarki ba ya tafi ya barta shekara da shekaru a dakinsa ba sako babu kulawa? Ni ban yarda yanzu sonta yake ba, na fi yarda da cewa so yake ya gyara tsakaninsa da iyayensa.
Ki kyale Kulsumu na dan lokaci ta kara sanin kanta, ta samu lafiyar jikin ta, ta yi karatunta sannan ta auri mijin da ke son ta ta ke son shi. Ra’ayi da tunanin su ya zo daya. Koda kuwa Turakin ne amma a can gaba. Sannan Turakin nan fa ba shi ne autan maza ba, ba'a ce bayan shi Kulsumu bazata auru ba wai don lalurar ta, kuma duk abin da ki ke hange a tare da shi akwai shi a sauran maza.
Ki fahimce ni Yaya Aishatu, ba nufi na in hana Kulsumu aure ba, amma don Allah ki kara mata lokaci. Na yi miki alkawarin ranar data zama cikakkiyar Nurse zan dawo miki da ita ta zabi mijin aure. Alhamdu lillahi ta samu lafiyarta wadda ya guje ta a kanta bai kamata don ya zo ya marairaice muku tashi daya ku yi saurin amsa masa ba, gara ya san Kulsumu mace ce mai daraja ya kuma san cewa akwai bambanci tsakanin mai lalurar da ya guda da wannan ta yanzu”.
Goggo ta rausayar da kai, ta ce, “Duk na fahimce ki, na kuma yarda da shawarar ki. Sai dai ba mu da hujjar cewa Turaki ya guji Kulsumu ne sabida lalurarta. Sun auri Kulsumu a kan sanin cewa tana da lalurar. Aure ne dai in Allah ya kawo karshensa dan Adam bai da dabara, amma na yarda da hujjojin da ya bayar kwata-kwata ba su da alaka da lalurar ta”.
Hajiya Nasara ta ce, “Shi ke nan. Allah shi ne masanin gaibu, amma maganar komen nan ki manta da ita Goggo, cikin watan nan Kulsumu za ta fara karatunta, ina rokonku don Allah ku manta da Turaki. Can gaba in suna da rabon komawar sa koma idan tana son shi yana sonta cikin nutsuwa da cikakken hankalin su, Allah ya yi wa Kulsumu zabi mafi alkhairi”.
Goggo ta ce, “Amin Nasara, insha Allahu yadda ki ka ce, haka za a yi”.
*** *** ***
Umma ta shiga turakar Maimartaba a daren ranar a matsayinta na mai girki a ranar. Bayan ya gama cin abinci ta ke labarta masa yadda Batulu ta ba ta labarin zuwansu gidan Malam Jibo ita da Turaki, Maimartaba ya gama sauraronta tsaf! Sannan ya yi murmushi ya ce.
“Kin ga hikimar da na yi ta zare hannunmu daga cikin maganar ta fito zahiri ko? Sun dauke ‘yar su zuwa inda za ta samu kwanciyar hankali ta yi karatun da suke so ta yi, ta auri miji mai sonta tsakani da Allah. Yau da mun saka baki da mun shiga hakkinsu, kunyarmu tasa su dawo da ita ya zo ya sake ba mu kunya, ya sake tafiya ya barta, don ya ce min ashe aiki ya samu a can din amma bayan shekaru uku zai dawo gida gabadaya.
Rakiya raba kanki da sha’anin Turaki, in ya damu ya je ya nemo ta a inda iyayenta suka boye ta. Ya karbi aurenta a hannunsu da kansa, in sun amince mu sai mu bi su da addu’a, amma kada ki sake sa baki a sha’anin Turaki, wanda muka yi a baya ya bula mana kasa a ido, Allah ya ba mu lada”.
Umma ta ce, “Ai na cire hannun nawa ranka ya dade, na dai kasa cire yarinyar a raina ne. Ni na san na yi asarar surukar kwarai mai son Turaki da zuciya daya. Zan bi su da addu’a Allah ya yi musu zabin alkhairi dukkanninsu. Allah ya sa watarana Kulsumu za ta dawo min”.
Murmushi Maimartaba Sarkin Gaya ya yi, ya ce, “Mata kuna son kanku da yawa, sannan kuna saurin manta girman laifin ‘ya’yan ku. Ni kuma na fi yi mata addu’ar Allah ya ba ta miji mai sonta ba Turaki ba, har yanzu ban gasgata wannan sabuwar soyayyar tasa ta dare daya ba, ya ce tunda ya tafi ya soma sonta, me ya hana ya dawo ya gyara laifinsa a lokacin da ya dace?”
Umma ta ce, “Haka Allah ya rubuta masa ranka ya dade, ko mun yi niyyar yin abu sai Allah ya nufa, ko ni ka shammace ni ban taba zaton za ka raba auren nan ba komai dadewar da Turaki zai yi. Sabida jikina na ba ni komai daren dadewa Turaki zai so Kulsumu, domin na mika lamarin su ga Ubangiji, kuma na tabbatar da ya karbi budurcin ta ranar da zai tafi. Kuma Alhamdulillah inada yaqinin wannan ne ya zama silar canzawar zuciyar sa a kanta”.
Maimartaba ya tsura mata ido, bai ce komai ba, amma can a karkashin zuciyarsa ya fara nadamar tsatstsauran hukuncin nasa, da ta yi masa wannan bayanin tun farko da ya yi wani hukuncin da bai kai raba su tsauri ba. Bai san cewa Turaki ya bi umarninsa ba ya tabbatar da auren sa kafin ya tafi. Ya soma zargin kansa da yin zalunci ga karamar yarinyar da ya mayar bazawara a kananan shekarunta. Amma da ya tuna ya yi ne bisa kyakkyawar niyya ta adalci ga talakawansa sai ya rage zargin kan nasa.
***
Watanni biyu Turaki ya kwashe cikin iyayensa da ‘yan uwansa. Duk wata ‘yar uwarsa da ke gidan aure sai da ya kai mata ziyara. Wajen aikinsa na ta nemansa, don haka ya kara neman izinin iyayensa kan ya koma U.K, ya kammala consultant ya baro aiki da su ya dawo gida bakidaya. A kan wannan alkawarin suka amince masa ya koma. Batulu har kuka ta yi sosai da zai tafi.
Bai tafi ba sai da ya je ya yi wa Goggo sallama ita da Baffa, yana kara yi musu tunin lambar waya idan su Kulsumu sun zo, ya yi alkawarin ko a wacce kasa suke zai bi Kulsumu. Baffa dai sai da ya ji kamar ya ba shi lambar, amma ya tuna rokon da Nasara ta yi ta yi masa a waya kan kada ya bayar din. Ya sani ita mai nufin alkhairi ga Kulsumu ne. Ta yi hakan ne da kyakkyawar manufa ba don ta hana ta zaman aure ba.
Ranar da ya tafi ne kuma aka sauke musu buhunhuna da katon-katon na kayan abinci. Sai da aka cika dakin da Baffa ke ajiye shirginsa. Sako ne daga Turaki, da kudi masu yawa cikin ambulan.
Baffa ya ce da ‘yan aiken su mayar masa da kudin ba zai karba ba, inda suke gaya amsa ai Turaki ya riga ya bar garin Gaya zuwa inda ya fito. Haka ya wuni da jimamin abin. Goggo ta ce za ta je ta yi wa Hajiya Rakiya godiya, Baffa ya yi hakuri kawai ya karba don bai kamata su mayar wa Hajiya Rakiya ba.
Ko da ta je yi wa Umma godiyar cewa ta yi, “Haba Hajiya Shatu, Turaki ai dan ku ne, don ya yi muku alheri ba sai na sani ba. Don Allah kada irin haka ta sake faruwa ki ce za ki yi min godiya, tsakaninku ne da Dan ku, ni babu ruwana”.