← Book details Kulsum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 22

Sashe 22

Kulsum Part 2 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Mu karasa a littafi na uku. Kuma na karshe insha Allahu. Kulsum 3 zai biyo bayan sa bada jimawa ba. Nayi muku alkawarin cigaban bazai jima ba. Gundarin labarin Kulsum yana cikin littafi na uku.
Taku har abada:- SUMAYYAH ABDULKADIR TAKORI.
JANUARY, 2021.

Ga masu bukatar tsofaffin littafaina zaku iya mallakar su a softcopy ko hardcopy (based on order idan hardcopy ne), a tuntube ni a whtsp ta wannan lamba 07030137870.

DANDANO DAGA KULSUM 3
"Malam lafiya?"
Tayi tambayar tana dojewa kallon idanunsa. "Na zo fita, ka sa securities din ku sun tare ni, na ci bashin ku ban biya ne?"
Bata yi aune ba ta ji hannun ta cikin na Turaki, kafin ta tantance meke faruwa ya jata tana tirjewa ya bude motarshi ya sanya ta, tare da rufe kofar da key din hannunsa. Ya zagaya ya shiga mazaunin sa ya tashi motar. Masu gadin suka wangale masa kofar ya fice suna daga masa hannu cikin girmamawa.

Tafiya kawai yake bisa shimfidaddun titunan garin Lagos ba tareda Kulsumu ta san inda aka nufa ba. "Malam sace ni zaka yi? Malam ina ruwan ka da ni ne? Malam ni matar aure ce ko baka ganni tare da mijina ba!" Idan sitiyarin motar ya bata amsa, to mai tukin motar ma ya bata. Inda take wannan bai kalla ba, tukin sa kawai yake cikin nishadi, sai sharara gudu yake amma murmushin dake kan tattausar fatar bakin sa ya kasa bacewa.
Kulsumu ta soma bugun gilashin motar da duka hannayen ta, fatan ta gilashin ya fashe koda zai yanke ta ne, tayi ihun da mutane zasu ji su kawo mata dauki. Amma ta lura gilashin motar ko sound baya badawa kuma ko zata shekara tana bugun sa bazai fashe ba.
Kawai sai ta fashe da kuka tana kiran Goggonta da Baffanta. Abinda yayi matukar baiwa Turaki dariya, ya dubeta ta gefen idanunsa,
"saura Batulu da Ummah".
Idanun cike da kuka amma hararar shi take yi. Har suka shiga unguwar Ikoyi Kulsumu bata bar kuka ba, don ta gane in ma sata ce Turaki ya gama sace ta. Sun wuce gidaje kamar guda biyar kafin su shiga wani kyakkyawan 'lodge' mai hawa daya. Mai gadi ya zo ya bude, Turaki ya zura hancin motar sa cikin gidan.
Yayi parking a rumfar adana motoci wadda ke dauke da wasu motocin guda biyu, ya kashe motar tare da sakin nannauyar ajiyar zuciya. Ya dubi Kulsumu wadda ta ki dagowa daga cinyoyinta, balle ta san inda ya kawo ta. Sautin kukanta kadai kake ji a motar, kamar wadda aka fadawa sakon mutuwar iyayen ta.
Kirjinsa ne kawai yake dagawa yana sauka da sauri da sauri. Ya yarda wani lokacin 'excitement' zai iya haifar da bugun zuciya. To hakan ce ta faru ga Turaki. Wanda ke ganin komai dake faruwa dashi yau kamar a mafarki..... wai shine da Kulsumu a gabansa!
Idan mafarki yake yana rokon Allah kada ya farkar dashi daga wannan mafarkin, har sai ya ga karshen sa. Har sai ya gan shi tare da Kulsumu matsayin ma'aurata a karo na biyu. Ashe duk mahaukacin neman nan da yake wa Kulsumu tana cikin kasar Nigeria, a Najeriyar ma a garin da yake rayuwa!. Allah shine shaida kan babu abinda ya wahalar dashi a duniya irin neman da yayi wa Kulsumu, shekaru dai-dai har guda hudu. Shi Allah da yake Gafurun-Rahimu ne, yau gashi ya tankado keyar Kulsumu ya kawo mishi ita har cikin ofishinsa. Shin shi wane irin wawa ne da zai yi saken da zata sake kufce masa?
"If u are done the cry (idan kin gama kukan) ki wuce mu karasa ciki".
A matukar fusace ta dago ta dubeshi....

"Nima bansan meye hadin nawa dake ba.... I just want to confirm ko Kulsumu na ce wannan. I just want to confirm....idan matata dana rasa nake nema ce. I just want to confirm....idan reaction din ta sabida ganina a inda bata yi tsammani ba yana da alaqa da ta gane ni ne itama, ko kuwa wani abu ne daban ya firgitata take neman mafaka.....".

Kulsum 3. Kada ku bari a baku labari. Akwai Dambarwa ba 'yar kadan ba.
-Takori
Chapter 22 · 0% Book details