Sashe 12
Kulsum Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
*** *** ***
ABUJA
Tarba ta musamma Kulsumu ta samu daga Hajiya, har ta fi murna da dawowarta a kan ta Taufeeq. Abinci kala-kala ta sa Serah ta shirya musu a dining. Hajiya ta aika Serah dakinta ta ce ta kirata ta ci abinci in ta huta. A lokacin ta fito wanka tana shafa mai Serah ta iske ta da sakon Hajiya. Doguwar riga kawai ta saka ta yafa veil din rigar ta bi bayan serah.
Ta zauna kenan ta fara zuba fried rice a faranti, Taufeeq ya shigo falon. Kai tsaye dining din ya nufo ya ja kujera mai fuskantarta ya zauna. Shi ma ya yi wanka ya canza kayan jikinsa zuwa T/Shirt DKNY ruwan goro da bakin wando chinose. Da ka ganshi ka ga Alhaji Muhammad Bello, wanda asalinsa bafullatanin Adamawa ne, kuruciya kawai ya fi shi, kwata-kwata ba ya kama da su Nasmah, ya fi su dogon hanci da kwantacciyar suma, su kuma sun fi shi haske.
Tunda ya zauna sai ta samu kanta da kasa cin abincin da ta zuba, sai juya cokali ta ke cikin shinkafa, tana kallonshi yana ta loda vegetables a kan 'yar shinkafar da ya zuba. Ya gama ya fara ci, yana satar kallonta.
"Yanayin yarinyar mai sanya tausayi ne," Taufeeq ya fada a ransa, sam ba ta da rawar kai irin wanda 'yammata tsararrakin ta ke da shi, sannan akwai tarin nutsuwa tattare da ita da wata irin kamala da bai taba gani tare da mace ba. Yana kallo ta dauke farantin abincin ta ta nufi dakin ta. Wannan na nufin; ba za ta iya cin abinci a gaban shi ba. Wanda ya nuna ita din mai kamun kai ce.
Ya ji yana son yi wa mahaifiyarsa tambayoyi a kanta, yana son sanin komai na rayuwar ta.
Shi da Hajiya ne a uwar dakin Hajiyar a daren ranar suna hirar abubuwan da suka baro a UK, Hajiya ta ce, “Don me za ka ajiye aikinka Taufeeq? Idan ka zo nan ka zauna me za ka yi mana? Ga Daddy shi ma tunda ya yi ritaya ba wani abu yake yi ba da pension dinsa kawai yake amfani”.
Taufeeq ya ce, “Mum I cannot endure the loneliness (ba zan iya jure kadaicin ba). Baban wani abokina ya sa an yi min transfer zuwa NIGERIAN NAVY, ina jiran su kira ni”.
Hajiya Nasara ta ce, “Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi”.
Taufeeq ya ce, “Amin Mum… ita wannan yarinyar da na dauko daga gidan Sakeenah wace ce dinki? Ko ita ce yarinyar da Nasmah ta ba ni waya in kawo mata?”
Hajiya Nasara ta ce, “Kulsum ba, ita ce. Jika ta ke ga kanwar mahaifiyata ta Gaya, ai ka san Goggo Aishatu da nake ba ku labari? An yi mata aure ne da Dan Sarkin Gaya, auren bai je ko’ina ba, shi ne na dauko ta don ta ci gaba da karatu nan a gabana. Gobe da safe za ka kaita ta sayo form din school of Nursing, Gwagwalada”.
Taufeeq ya ce, “Kamar ya ya auren bai je ko’ina ba? Mijin ya sake ta ne?”
Hajiya ta girgiza kai, “Bai sake ta ba, iyayensa ne suka raba auren. Ya tafi karatu Turai ya ki dawowa”.
Taufeeq bai kara magana akai ba, wani zancen daban ya koma yi. Amma cikin zuciyarsa sai ya ji yana tausaya wa Kulsumun, karamar yarinya da ita an maida ita bazawara. Matsalar 'ya'yan sarautar nan kenan.
Washegari da safe Kulsumu na yi wa Hajiya Nasara gyaran daki, ta ce da ita ta shirya Taufeeq zai kai ta sayen form. Haka nan dai ita ba ta son hada hanya da Taufeeq dinnan, kallon idanunsa na sa wa ta ji wani iri a ranta. Za ta so a ce ba shi zai kai ta ba, Hajiyar ce da kanta ko direba ko Serah ta raka ta, amma ba za ta iya yi wa Hajiya musu ba. Dole ta shirya cikin daya daga kayan da Sakeenah ta bata ta nemi hijab cikin kayan da ta zo da su daga Gaya ta dora a kai. Ta je ta ce da Hajiya ta shirya, ita kuma ta kira Taufeeq a waya, ya ce ta same shi a cikin mota yana waje.
Suna tafe cikin motar Daddy (Honda 2015 model) babu mai cewa komai tun bayan da ta gaishe shi ya amsa. Sai da suka iso makarantar ya yi tambaya aka nuna musu inda za su je. A mota ya ce ta jira shi, ya je ya sayo ya dawo ya dora mata a cinya. A hanyarsu ta dawowa ya tsaya ya sayi abu a supermarket, sannan suka karaso gida.
Ta bude kofar motar za ta fita, ya kira sunanta. Da dumbin mamaki ta juyo don ba ta san ya san sunan ta ba. Wani dan karamin farin kwali ya miko mata.
Cikin taushin murya ya ce,
“A message from Nasmah (sako daga Nasmah)”.
Hannu biyu ta sa ta amsa, ta yi masa godiya ta shige cikin gida. Ya bi bayanta da kallo. Wani irin kallo da ya tabbata bai taba yiwa kowacce diya mace ba.
A falo ta tadda Hajiya, ta ce, “Har an dawo?”
“Mun dawo Hajiya, kin ga sakon da Nasmah ta aiko min”.
Ta zauna gefen Hajiyar tana kokarin bude kwalin wayar. Murna fal kumatunta, Hajiya ta ce, “An gode wa Nasmah”.
Ta fiddo wayar mai kyau da ita. Ta ce, “Hajiya ki aika wa Baban ‘Yalleman, ni sai in ci gaba da amfani da ta wajen Aunty Sakeenah”.
Hajiya Nasra ta ce, “Ba za a yi haka ba, tunda ta saya da sunanki ki hada duka ki yi amfani da su, insha Allah zan bai wa Yusha'u wata ya kai masa har Gaya, sai Goggo ta ba shi”.
Kulsum ta ji dadi sosai, wai ita ce mallakin wayar hannu har guda biyu rus! Na nunawa sa'a.
Taufeeq Hajiya ta sa ya taimaka mata ta cike form din ta online. Babu jimawa admission ya fito, an dauke ta a FCT Nursing School. Duka wani shige da fice da Taufeeq suka yi shi, har ta fara shiga aji.
Malam Yusha'u direban Hajiya ya ci gaba da kaita yana dauko ta, sabida shi ma Taufeeq din aikinsa ya fito ya yi joining Nigerian Navy, ya tattara ya tafi Lagos inda suka ajiye shi.
Sai dai kuma ya tafi ne da Kulsum manne cikin ransa. Wani al’amari da bai taba faruwa da shi ba a kan diya mace. Tun daga ranar da Hajiya ta hada su zuwa sayen form ya kasa mallakar kansa a kan Kulsum. Sosai ta zauna cikin zuciyarsa, da ya ji labarinta kuma da yadda mijin ta ya tafi ya barta sai feelings dinsa a kanta ya karu. Da ma kuma tausayi yana taimakawa wajen kimsa so. Ya bar wa ransa komai don ya san yadda Hajiyarsa ta sa wa ranta son Kulsum ta yi karatu ba za ta taba aminta ba.
Amma ko da ya kama aikinsa a Lagos sai nutsuwa ta gagare shi. A duk abin da yake yi Kulsum na gilma masa, tunaninta ya hana shi sakat, yana mamakin wane ne ya auri Kulsum ya kuma sake ta cikin hankalinsa? Wannan shi ake kira sauta ga wawa.
Hajiya ba ta fito fili ta gaya wa Taufeeq lalurar da Kulsum ta yi fama a baya ba, kuma ba ta kafa hujja da ita a kan dalilin rabuwar aurenta ba, tunda su Goggo kansu ba su da tabbas a kan hakan. Ta barshi a yadda su ma suka barshi, wato ya tafi karatu ya ki dawowa, iyayensa suka raba auren.
ABUJA
Tarba ta musamma Kulsumu ta samu daga Hajiya, har ta fi murna da dawowarta a kan ta Taufeeq. Abinci kala-kala ta sa Serah ta shirya musu a dining. Hajiya ta aika Serah dakinta ta ce ta kirata ta ci abinci in ta huta. A lokacin ta fito wanka tana shafa mai Serah ta iske ta da sakon Hajiya. Doguwar riga kawai ta saka ta yafa veil din rigar ta bi bayan serah.
Ta zauna kenan ta fara zuba fried rice a faranti, Taufeeq ya shigo falon. Kai tsaye dining din ya nufo ya ja kujera mai fuskantarta ya zauna. Shi ma ya yi wanka ya canza kayan jikinsa zuwa T/Shirt DKNY ruwan goro da bakin wando chinose. Da ka ganshi ka ga Alhaji Muhammad Bello, wanda asalinsa bafullatanin Adamawa ne, kuruciya kawai ya fi shi, kwata-kwata ba ya kama da su Nasmah, ya fi su dogon hanci da kwantacciyar suma, su kuma sun fi shi haske.
Tunda ya zauna sai ta samu kanta da kasa cin abincin da ta zuba, sai juya cokali ta ke cikin shinkafa, tana kallonshi yana ta loda vegetables a kan 'yar shinkafar da ya zuba. Ya gama ya fara ci, yana satar kallonta.
"Yanayin yarinyar mai sanya tausayi ne," Taufeeq ya fada a ransa, sam ba ta da rawar kai irin wanda 'yammata tsararrakin ta ke da shi, sannan akwai tarin nutsuwa tattare da ita da wata irin kamala da bai taba gani tare da mace ba. Yana kallo ta dauke farantin abincin ta ta nufi dakin ta. Wannan na nufin; ba za ta iya cin abinci a gaban shi ba. Wanda ya nuna ita din mai kamun kai ce.
Ya ji yana son yi wa mahaifiyarsa tambayoyi a kanta, yana son sanin komai na rayuwar ta.
Shi da Hajiya ne a uwar dakin Hajiyar a daren ranar suna hirar abubuwan da suka baro a UK, Hajiya ta ce, “Don me za ka ajiye aikinka Taufeeq? Idan ka zo nan ka zauna me za ka yi mana? Ga Daddy shi ma tunda ya yi ritaya ba wani abu yake yi ba da pension dinsa kawai yake amfani”.
Taufeeq ya ce, “Mum I cannot endure the loneliness (ba zan iya jure kadaicin ba). Baban wani abokina ya sa an yi min transfer zuwa NIGERIAN NAVY, ina jiran su kira ni”.
Hajiya Nasara ta ce, “Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi”.
Taufeeq ya ce, “Amin Mum… ita wannan yarinyar da na dauko daga gidan Sakeenah wace ce dinki? Ko ita ce yarinyar da Nasmah ta ba ni waya in kawo mata?”
Hajiya Nasara ta ce, “Kulsum ba, ita ce. Jika ta ke ga kanwar mahaifiyata ta Gaya, ai ka san Goggo Aishatu da nake ba ku labari? An yi mata aure ne da Dan Sarkin Gaya, auren bai je ko’ina ba, shi ne na dauko ta don ta ci gaba da karatu nan a gabana. Gobe da safe za ka kaita ta sayo form din school of Nursing, Gwagwalada”.
Taufeeq ya ce, “Kamar ya ya auren bai je ko’ina ba? Mijin ya sake ta ne?”
Hajiya ta girgiza kai, “Bai sake ta ba, iyayensa ne suka raba auren. Ya tafi karatu Turai ya ki dawowa”.
Taufeeq bai kara magana akai ba, wani zancen daban ya koma yi. Amma cikin zuciyarsa sai ya ji yana tausaya wa Kulsumun, karamar yarinya da ita an maida ita bazawara. Matsalar 'ya'yan sarautar nan kenan.
Washegari da safe Kulsumu na yi wa Hajiya Nasara gyaran daki, ta ce da ita ta shirya Taufeeq zai kai ta sayen form. Haka nan dai ita ba ta son hada hanya da Taufeeq dinnan, kallon idanunsa na sa wa ta ji wani iri a ranta. Za ta so a ce ba shi zai kai ta ba, Hajiyar ce da kanta ko direba ko Serah ta raka ta, amma ba za ta iya yi wa Hajiya musu ba. Dole ta shirya cikin daya daga kayan da Sakeenah ta bata ta nemi hijab cikin kayan da ta zo da su daga Gaya ta dora a kai. Ta je ta ce da Hajiya ta shirya, ita kuma ta kira Taufeeq a waya, ya ce ta same shi a cikin mota yana waje.
Suna tafe cikin motar Daddy (Honda 2015 model) babu mai cewa komai tun bayan da ta gaishe shi ya amsa. Sai da suka iso makarantar ya yi tambaya aka nuna musu inda za su je. A mota ya ce ta jira shi, ya je ya sayo ya dawo ya dora mata a cinya. A hanyarsu ta dawowa ya tsaya ya sayi abu a supermarket, sannan suka karaso gida.
Ta bude kofar motar za ta fita, ya kira sunanta. Da dumbin mamaki ta juyo don ba ta san ya san sunan ta ba. Wani dan karamin farin kwali ya miko mata.
Cikin taushin murya ya ce,
“A message from Nasmah (sako daga Nasmah)”.
Hannu biyu ta sa ta amsa, ta yi masa godiya ta shige cikin gida. Ya bi bayanta da kallo. Wani irin kallo da ya tabbata bai taba yiwa kowacce diya mace ba.
A falo ta tadda Hajiya, ta ce, “Har an dawo?”
“Mun dawo Hajiya, kin ga sakon da Nasmah ta aiko min”.
Ta zauna gefen Hajiyar tana kokarin bude kwalin wayar. Murna fal kumatunta, Hajiya ta ce, “An gode wa Nasmah”.
Ta fiddo wayar mai kyau da ita. Ta ce, “Hajiya ki aika wa Baban ‘Yalleman, ni sai in ci gaba da amfani da ta wajen Aunty Sakeenah”.
Hajiya Nasra ta ce, “Ba za a yi haka ba, tunda ta saya da sunanki ki hada duka ki yi amfani da su, insha Allah zan bai wa Yusha'u wata ya kai masa har Gaya, sai Goggo ta ba shi”.
Kulsum ta ji dadi sosai, wai ita ce mallakin wayar hannu har guda biyu rus! Na nunawa sa'a.
Taufeeq Hajiya ta sa ya taimaka mata ta cike form din ta online. Babu jimawa admission ya fito, an dauke ta a FCT Nursing School. Duka wani shige da fice da Taufeeq suka yi shi, har ta fara shiga aji.
Malam Yusha'u direban Hajiya ya ci gaba da kaita yana dauko ta, sabida shi ma Taufeeq din aikinsa ya fito ya yi joining Nigerian Navy, ya tattara ya tafi Lagos inda suka ajiye shi.
Sai dai kuma ya tafi ne da Kulsum manne cikin ransa. Wani al’amari da bai taba faruwa da shi ba a kan diya mace. Tun daga ranar da Hajiya ta hada su zuwa sayen form ya kasa mallakar kansa a kan Kulsum. Sosai ta zauna cikin zuciyarsa, da ya ji labarinta kuma da yadda mijin ta ya tafi ya barta sai feelings dinsa a kanta ya karu. Da ma kuma tausayi yana taimakawa wajen kimsa so. Ya bar wa ransa komai don ya san yadda Hajiyarsa ta sa wa ranta son Kulsum ta yi karatu ba za ta taba aminta ba.
Amma ko da ya kama aikinsa a Lagos sai nutsuwa ta gagare shi. A duk abin da yake yi Kulsum na gilma masa, tunaninta ya hana shi sakat, yana mamakin wane ne ya auri Kulsum ya kuma sake ta cikin hankalinsa? Wannan shi ake kira sauta ga wawa.
Hajiya ba ta fito fili ta gaya wa Taufeeq lalurar da Kulsum ta yi fama a baya ba, kuma ba ta kafa hujja da ita a kan dalilin rabuwar aurenta ba, tunda su Goggo kansu ba su da tabbas a kan hakan. Ta barshi a yadda su ma suka barshi, wato ya tafi karatu ya ki dawowa, iyayensa suka raba auren.